Showing 30001 words to 33000 words out of 352722 words

Chapter 11 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30706

da bakin kofar zauren,
Cikin sanyi yace.
"Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kin rama kena".
Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace.
"Ga wuri kizo ki zauna mana".
A hankali tace,
"A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana".

"Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?".
Salmanu ya faɗa a hankali.
Da sauri tace.
"Eh".
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
"Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?".

A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi.
Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace.
"Gaya min me kike tsoro?".
Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai".
Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace.
"Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba".
Da sauri tace.
"Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi".
Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace.
"Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon".
Cikin yanayin nitsuwarta tace.
"A a kaci kawai Ya Salmanu".
Da sauri yace.
"No kada kimin musu".
Shiru tayi jin yaci gaba da cewa.
"Muddin dai ina raye in sha Allah.
wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki".
Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu.

A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna ɗan hirarsu
Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai.

Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa.
"Ummey".

"Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru,
Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace.
"Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?".
Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace.
"Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?".
Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa.
"To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi".
Kai ta juya tare da cewa.
"Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko".
Murmushi Ummey tayi kana tace.
"Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki".
da haka suka konta bacci.

Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai,
Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta.

Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu.

Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma.
To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu.

Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba.
Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki shiyasa tun yana ƙaraminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi. Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani ɗin.

A can ƙasa mai tsarki kuwa,
Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana uku da zuwa suka tafi, Madina,
Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki Jalaluddin, shi kuma yaje har Ɓadamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi ɗaurin auren.

To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka.

Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal.
Kullum yakan kira Juwairiyya.

Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce.

Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh Abdulkareem domin yana tare da manyan baƙi.

Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti.

Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan jin daɗin rayuwar duniya,

Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah suna gefenta, cikin shiga ta al'farma,

Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim ɗin sukeyiwa tausa.
Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da danƙawa-ɗanƙwal dajaja sai sauran abincinsu na larabawa.

Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna ɗan taɓa hira.

Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya ɗan juya ya kalli wayar ba tare daya juya kanshiba,
Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar,
da sauri ya ɗauko wayar ya miƙa mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran.
Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace.
"Barka da dare Hajia Mama".
A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare da cewa.
"Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane".
Idonshi ya ɗan ɗago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace.
"Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal".
Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata muzurai".
Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace.
"Hajia Mama kiyi musu faɗa kice su barifa sun girma".
Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa.
"Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma".
Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa.
"Ina Sitti na?". A taƙaice yace.
"Gata nan kusa dani".
Cikin yanayin jin daɗi tace.
"Bata waya". To yace kana ya miƙa Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa.
"(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ƙara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace, kana suka gaisa cikin tsananin jin daɗi.
Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake kishinƙiɗe ya lumshe ido a hankali tace.
"Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka ɗaki ɗaki, da bai gankaba yaƙi fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu.
Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo mishi,
Haka Jazrah da Jannart,
Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace.
"Lamiɗo ya gaya min ɗazu da mukayi waya".
Shiru sukayi baki ɗayansu, a hankali Haroon ya miƙe kwance tare da faɗawa nazari mai zurfi.
Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar musu hankali kafin, sukayi sallama da juna.



Yau jumma'a ne gajeren lokacine basa kai yamma a wurin kiwo, kafin azahar suke dawowa, shiyasa yau Shatu tace da ita za'aje kiwo.
Dariya kawai sukayi mata dan sun san ba iya jurewa zatayiba amman tunda ta kafa ta tsare cewa dole zataje, sai aka barta.

Kasan cewar basu kai yamman bane yasa kuma suna tafiya da wuri.
Bayan duk an kunce dabobbin gaba ɗaya, hakama sauran makiyayan baki ɗaya, sahu- sahu shanayen keta wucewa.

Sun tafi tun shida da rabi na safe,

Kafin zuwa tara na safe sunyi nisa cikin wurin kiwonsu, inda nan kuma Aysha ta samu su Hindema sunzo kiwo, wanda su kullum dama suna zuwa.

Wani irin hadarine mai ƙarfi ya taso daga ƙasa, ganin hakane yasa, Gaini kwallawa Shatu kira wacce take can cikin ƴan uwanta mata makiyaya, jin shiru bata amsa bane ya nufi wurin da suke zaune,
Cikin kula yace.
"Aysha tashi keda Hinde dasu Mero duk ku tafi gida, kunga hadarine mai ƙarfi ke tasowa daga ƙasa da alamun za'ayi ruwa mai ƙarfi".
Cikin ƙarfin hali da son wasa cikin ruwan da taketa hari murya a sanyaye tace.
"Ba komai ya Gaini zamu jiraku ai lokacin tashi kuma ya kusa ko?".
Su Giɗi dasu Aro da sauran makiyayan ne sukace.
"Ya Gaini barsu mana ba kiwo zasuyi ba ai makiyayin shanu da tumaki baya gudun ruwa duk yawa shi".
Cikin jin daɗi sukace, eh mana,
Shi kuwa Ya Gaini murmushi kawai yayi tare da cewa.
"Shike nan yau zakusha dukan ruwa".
Murmushi sukayi sukace "Babu matsala". daga nan mazan duk suka koma wurin kula da dabobbin nasu da suka duƙufa cin koren ciyawa.

Su kuwa Shatu da Hinde a hankali sukaci gaba da tafiya, sosai tsarin wurin da yanayin shigar suturar dake jikinta yayi tsananin dacewa da ita.
Doguwar rigace irin tamu ta fulani, yadin farine, sai daga samanshi akayi mishi kolliya da zaron huɗu, mai color red white, blue, yellow, and green, wanda aka ƙawata saman rigar da kolliyar zanen ɗawisu, inda daga kafaɗunta har zuwa saman ƙirjinta, duk an shimfiɗa zaren, bisa wuyan rigar mai V.
sai kuma hannun rigar shima duk an zagayeshi da kolliyar,
Kana sai tsakiyar rigar dai-dai kan ƙugunta shima an ƙawatashi da wannan kolliyar ulu irin namu na fulanin daji,
Kana sai ƙasar rigar can itama an ƙawata da wannan zaren.

Sai dogon gashin kanta da yake zube a kafaɗunta, yayinda daga saman goshinta kuma tasa, bandana amman irin namu na fulani mai kalolin ƴaƴan tsakiya, ta zagaye kanta dashi, sai kolliyar da tayi a fuskarta irin ta asalin fulani, a goshinta zanen kan shanu tayi, shaidar cikekkiyar bafulatanace, sai kuma ƙasan lip ɗinta na ƙasa zuwa kan ɗan gemunta shi kuma taja zane da kuma yin ɗigo-ɗigo a gefenshi.
Sai wata kekkewar jakar sakan ulun mai kalolin kolliyar jikin rigarta data rataya a hannun damanta, wanda cikin jakar kuma ruwan shantane a ciki sai sassanyan kinɗirmo da goran zuma, sai ɗan sandar mu ta gado, takalman sawunta irin sau cikin nanne daku mutanen cikin birane kuke masa laƙabi da tashi kabi shanu.
Tayi masifar kyau a cikin wannan shigar tamu ta gado, kyau iya kyau farar fatarta ta baiyana tamkar balarabiya gashin girarta ya konta lib lib.

A hankali suke ɗan tattaki a cikin dogayen saunukan, da koriyar ciyawa da tayiwa ƙasanshi ƙawanya. suna ɗan tafe
Suna ɗan tsinkar ya'yan kanya da gwandar daji da suke cike da wurin Chaɓɓulle wato tsada.

Hadari kuwa sai gamgami yakeyi gabas da yamma kudu da arewa, ko ina yayi dib babu motsin komai sai nasu dana dabobbin su,
Iska ta tsaya cak koda ganye ɗaya baya kaɗawa duhu ya kareɗe illahirin yankin.

A hankali Hinde ta kalli sararin samaniya cikin tsoron ganin gaba ɗaya duniyar tayi baƙiƙƙirin ko ina yayi dib, hakanne yasata ɗan zaro ido tare da cewa.
"Kai Shatu, kalli sama, fa hadarin nan yayi duhu da yawa gsky mu tafi gida".
Da sauri ta ɗago kanta kana tasa hannunta na hagu ta ɗan kare saman goshinta kaɗan, ware idanunta tayi ta kalli sararin samaniya, wani irin azabebben firgita da tsorone ya rufeta wanda yasa ta juya da azaban ƙarfi ta ruggume Hinde dai-dai lokacin, sukaga wani irin tartsatsin azabebben igiyar...!






Dan Allah da Manzonsa in dai kin san zaki sayi littafinane ɗan ki fiddashi na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar su. Kada ki saya bana so, ki riƙe kudinki.

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘

*GARKUWA*

PAGE 9

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘


*FREE PAGE*

*TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta wannan number 09097853276 DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA littafin GARKUWA, ba tare da haƙƙin kowa a kankiba. Akwai Special Group shi kuma na 1k rak, ki turoshi ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai ta WhatsApp 09097853276*


~Ga masu buƙatar kayan gyara na amare, akwai set-set masu kyau, a ƙananan robobi masu sauƙin kuɗi, akwai kuma na manyan robobi masu zafi, akwiasu dai-dai da tsarin al'jihun mai ƙarfi da mai rauni, ina araha ina hana bashi. Koda kuɗinka saida rabonka, kayan Kamfani daban dana shago.~

*Al'ummar Hausawa mazauna Saudiya wannan shafin nakune kyauta gareku, domin jiya da yau saida mai zaton babu wasu masu karanta littafi sama daku. Nasha mamaki da sanyin safiya naita cin karo da numbers ɗin ƙasa mai tsarki suna ta antayo min manyan kuɗi na ƙasa mai tsarki tun ina ƙidaya numbers ɗin +966 har dai abun yaci tura sabida yawansu, ashe daga zauren Umar Maisanyi sukayi ta antayowa gareni. Godiya mai tarin Yawa Umar maisanyi mai Tsakar gida You tube limamin tsakar gida*



Walƙiya mai tsananin haske da tartsatsi wanda saida ya haska gaba ɗaya, dajin ya zamana, har kana iya ganin inuwar dogayen bishiyoyin wurin da sukayi musu ƙawanys.
Wani irin tsoro da firgici da karkarwan ne ya bijirowa Aysha.
Cikin dauriya da sabo da ganin ire-iren irin waɗannan ababen a wurin kiwo, Hinde ta kamo hannun Shatu tare da cewa.
"Kai Aysha babu komai fa walƙiyace kawai fa kai".
Sai kuma tayi dariya tare da cewa,
"Uhum a hakan kike tunanin jurar taraddadin da muke gani cikin tsaunuka in muna kiwo".
Janye jikinta tayi daga jikin Hinde, hannun tasa ta tattare gashin kanta dake baje a kafaɗunta, tubkeshi tayi cikin, fidda numafashin tsoro take karisa addu'o'in datake tayi a bakinta, a hankali taja da baya ta jingina da jikin ƙatuwar bishiyar Gamji dake gefensu, jingina kanta tayi jikin bishiyar gamjin tana jin yadda zuciyarta ke harbawa, pat-pat da azaban ƙarfi domin tasan Hinde bata san me idonta ke shirin hango mataba,
ita kuwa Hinde, a gabanta take tsaye ya zamana sun fuskantar juna.
Su Ya Gaini kuwa sun duƙufa kiwonsu kamar dai yadda suka saba, ruwa ko iska ko zafin rana da ƙishi baya kora makiyaye daga kiwo a daji ya dawo gida.
So duk kowa yana yankin da yake bawa dabobbin tsaro, sam basuma hango su Aysha sosai.

Ita kuwa Shatu idonta dake lumshe ta fara ƙoƙarin buɗewa sabida wani irin tashi da taji tsikar jikinta nayi.
Hinde kuwa ido ta zuba mata tana ganin yadda ƙirjinta yake sama da ƙasa alamun tsananin firgita.
A hankali ta ware manyan kyawawan idanunta.
Wani ƙaton curi, dake can bayan Hinde ta zubawa ido sabida wani abu da take gani kamar hayaƙi yana fitowa ta ƙananan ƙofofin curin. Ita kuwa Hinde bata san meke wakana ba sabida, ita baya ta bawa curin, asalima yanzu kanta ta ɗaga sama tana shan ruwan dake cikin goranta.

Ita kuwa Shatu so take ta janye idanunta daga kan wannan CURIN amman sai taji ta kasa, bugun da zuciyarta keyine ya tsananta, lokaci ɗaya jikinta ya fara tsuma da karkarwa zufa mai azabar zafi ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta.
Yayin da zuciyarta. Ke harba jini one litter. A Cikin ko wanne one second. Bakinta ta buɗe da nufun furta addu'o'in dake jere a zuciyarta amman sai taji ta kasa, zuru-zuru tayi da idanunta lokacin da taga wani dogon abu yana fitowa daga cikin babban ramin dake tsakiyar CURIN nan, a hankali ta ɗaga kwayar idanunta sama tana bin abin da kallo, wani irin dogon numfashi taja, ganin abun nan yana miƙewa yana yin sama, abun dogo kamar igiya sai dai kuma yanada zane kala-kala red, yellow, green, blue.
Kuma abun biyune ɗaya a sama ɗaya a ƙasa, cikin ranta take iya ammabaton sunan Allah ganin zahiri fitowar bakan Gizo daga cikin curi Allah ya nuna mata, ras zanen bakan Gizon nan yayi kama da kalolin kolliyar jikin rigarta,
Kanta ta ɗaga sama, tana bin Bakan Gizon da kwayar idanunta, tana gani har ya haura sama can ya konta a gicciye gabas da yamma kudu da arewa, kana kuma mai hasken ras yana sama mai ɗan dishi-dishin yana ƙasa. Wanda a falsafar al'ummar Duniya ake cewa suma mata da mijine, muddin kaga mai hasken in ka zuba ido zakaga mai dishi-dishin wanda


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login