Showing 183001 words to 186000 words out of 352722 words
da shigowa ɗakinshi yafi kwana goma.
Umaymah kuwa cikin murmushi mai sauti tace.
"Ina ɗiyata, tanata kuka ko?".
A hankali yace.
"Gata".
Wani irin farin cikine ya rufe zuciyar Umaymah tasan burinsu bazai tabbataba muddin babu shaƙuwa da kusanci tsakanin Sheykh da matarsa.
Cikin jin daɗi tace.
"Bata wayar".
Uhum yace kana ya miƙo mata wayar.
A hankali ta iso gabanshi kusa dashi gab-gab ta tsaya.
wayar ya miƙa mata yana kallon yadda take matsoshi.
Amsar wayar tayi ta kara a kunne tare da yin sallama.
Kana idonta kuma yana kan zanen macijiyar dake konce har kan cikinsa zuwa saman haƙar-ƙarinshi.
Da Ido yabi wurin da take kallon.
Fuskarshi ya haɗe tare da ɗaga ƙafarshi zai ja da baya.
Sai kuma ya tsaya cike da mamaki ya kalli hannunta da tasaka ta kamo bakin robar gajeren wondon dake ƙugunshi.
Hannunshi yasa ya bugi hannunta,
Amman sai ta ƙara matsoshi.
Cikin sanyi ta....!
Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta number nan da nake whatsapp da ita, 09097853276 ba hoton katin zaki turoba, ba kuma TRANSFER ɗin katin zakiyi minba, ba kuma BTU ba, numbers ɗin katin zaki rubuto ki turomin. In kuwa special Group kikeso kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo min screenshort na shaidar biyanki ta wannan number tawa ta whatsapp 09097853276.
Kada kiyi min TRANSFER ko BTU na kati wlh in kinyi ba ruwana.
By
*GARKUWAR FULANI*
Cikin tsuke fuskarsa da muryar dake nuna zafin abinda ke zuciyarshi yace.
"Ummi in ya fito kiyi mishi jagora zuwa wurin sarkin ƙofa ki nunashi kada a sake barin yazo ko kusa da katangar masarautar Joɗa ne, a korashi ya bar jihar Ɓadamaya."
Da sauri Ummi tace. "Toh".
Kana tayi gaba tare da cewa.
"Mu tafi".
Da sauri Barun yabi bayanta.
A can falon Sheykh kuwa komawa yayi ya zauna gaban Bappa cikin sanyi yace.
"Bappa kayi haƙuri, ka gafarceni, bisa korarshi da nayi.
Wannan sunada manufar data kawoshi, ni zan ji da ciwon hannunta, in sha Allah zata samu lfy. Ka kwantar da hankalinka."
Ido Aysha ta zuba mishi cike da mamakin ta ina ta yaya ya gane meke tafe da Barun har ya gane sunada wata manufa, ta yaya ya gano kuramen bakin da Barun ya karanta mata, ta yaya yayi musu wasali har ya basu cikekkiyar jimla ya karancesu da fassararsu, meya sani a kanta.
Hakama Bappan kallon Mamaki yakeyi mishi amman sai ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Ba komai Muhammad Allah ya bamu sa'a ya kuma bata lfy".
Amin Amin yace shida Umaymah.
Al'amin ne ya ɗan gyara zama tare da cewa.
"To Allah yasa a dace. Amman ko za'a gwada asibiti ne?."
Kai ya jujjuya tare da cewa.
"Kada ka damu, in sha Allah ba damuwa".
Kai ya ɗan gyaɗa cikin gamsuwa.
A hankali Umaymah ta miƙe ta fita.
Shi kuwa Sheykh Aysha ya kalla tare da cewa.
"Tashi ki barsu suci abinci mana".
Da sauri Bappa da Al'amin sukayi mgna kusan a tare sukace.
"Alhamdulillah mun ƙoshi".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Al'ameen da kyau kana a hankali yace.
"Ba'a zuwa masarautar Joɗa a fita ba'aci komaiba".
Murmushi mai cike da gamsuwa Bappa yayi kana yace.
"Eh Alhamdulillah munci a wurin Lamiɗo ai".
Kanshi ya gyaɗa cikin gamsuwa da hakan yace.
"Toh Bappa".
Cikin sanyi ita kuma Aysha tace.
"Ya Al'amin bani zanci".
Murmushi Al'amin yayi kana ya jawo Foodflaks ɗin,
a plate ya zuba mata Couscous da biyar hanta.
gyara zamanshi yayi ya fuskanceta da kyau itama gyara zamanta tayi.
Bappa kuwa Murmushi yayi yana kallonsu.
Shi kuwa Sheykh ido ya zuba musu zaiga dai iya gudun ruwansu duk da zuciyarshi ta gama gano mishi nasabarsu.
Shi kuwa Al'ameen. A hankali yasa spoon ya ɗan ɗibo, kana ya nufi bakinta da spoon ɗin tare da cewa.
"Ha, buɗe bakin".
To tace kana ta buɗe bakin ya saka mata.
lumshe idonta tayi tare da tauna abincin dan ya mata daɗi.
Sake dibowa yayi ya bata, still ta buɗe baki yasa mata.
Cire kanshi yayi a kansu, ya maida dubanshi kan Bappa dake mishi mgna.
Umaymah da Ummi ne suka shigo a tare ita Ummi cewa.
Sheykh tayi an fidda Barun.
Ita kuwa Umaymah ƙwaryar fura da nono ta kawo musu.
Murmushi sukayi ganin yadda Aysha ta zage tana cin abinci.
Shi kuwa Al'amin ya dage yana bata.
"Ya Al'amin zan sha ruwa".
Tace mishi tana taunar sokar naman da yasa mata a baki.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Umaymah tare da cewa.
"Allah rene a sammin ruwa in bata".
To Umaymah tace ta miƙo mishi ruwa.
Tana kallon kamanninshi da Aysha ba sai an gaya maka cewar ɗan uwanta jininta bane.
Bata ruwan yayi har baki.
Tasha sosai.
Kana ya kalleta tare da cewa.
"In ƙara miki abincin ne?".
Kai ta gyaɗa mishi.
murmushi yayi tare da cewa.
"Bubbuga rumbun Abboi".
Murmushi tayi itama tana mai share hawayen da suka silalo mata.
Ƙara mata yayi tare da ci gaba da bata.
Sosai kuwa taci tayi haniƙan.
Sheykh kuwa da wutsiyar idonshi yake kallon dukkan motsinsu.
Bayan tayi gyatsa ne, Ummi ta matsar da kwanukan.
Babu yadda Sheykh da Umaymah basuyiba, amman Al'amin da Bappa sunƙi suci abinci.
Kiran sallan azahar ne,
Yasa duk suka miƙe.
Cikin sanyi Al'amin ya kalli ogogon hannunshi da yaketa sheƙi yace.
"Bappa muyi salla mu tafi kada lokacin ya ƙure mana".
Cikin kula Umaymah tace.
"Ba kwana zamuyi ba".
Murmushi Bappa yayi tare da cewa.
"A'a zamu koma tunda jiki da sauƙin gata taci ta ƙoshi tana hira."
A hankali Ummi tace.
"Eh ai dama haka takeyi, anjima kuma in ciwon ya tashi zakace kamar zata shiɗe, sai an mata tofi take ɗan samun sauƙin".
Murmushi Al'amin yayi tare da kallon Sheykh cikin nitsuwa da gogewar cikar wayewar dake nuni ba makiyayin daji bane yace.
"Sheykh ka samu sabuwar wayar hannu, kenan tunda sai kayi tofi akejin sauki.
Dan Allah duk inda kake ta kasance a nan a ƙara kulan mana da Boɗɗin Abbai".
Murmushi ya ɗanyi tare da cewa.
"In Sha Allah".
Cikin karrama Sheykh ya nuna musu wata ƙofar dake gefen ɗakinshi yace.
"Ga wuri kuyi al'wala mu tafi masallacin".
kai Al'amin ya gyaɗa kana yace.
"Bappa je kayi al'wala kazo mu tafi.
Cikin nitsuwa Bappa yace da al'wala ta".
Shima Al'amin gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa.
"Nima inada al'wala".
Cikin gamsuwa Sheykh yace.
"To bisimilla muje nima da al'wala".
To sukace kana duk suka nufi babban falon.
Suna isa tsakiyar falon. Al'amin ya ɗan tsaya tare da cewa.
"Parvina zo".
Da sauri ta ƙaraso gabanshi.
Shiru sukayi jin Al'amin ya juya harshe zuwa wani Yaren ba larabciba ba Turanciba ba hausaba ba fillanciba.
Mgna yakeyi riƙe da hannunta.
Ita kuwa Aysha kai taketa gyaɗa mishi ido cike da kwalla.
Hannunshi yasa ya share mata hawayen kana yasa hannunshi ya shafa kanta tare da juyawa ya fita.
Ita kuwa Aysha cikin sanyi tace.
"Bappa dan Allah a kawo min Junainah".
Kanshi ya gyaɗa kana shima ya fita.
Binsu a baya Sheykh yayi.
Ita kuwa hannunta mai lfyar tasa ta share siraran hawayen da suka zubo mata.
Kana ta juya ta nufi ɗakinta.
Ummi da Umaymah kuwa kallon juna sukayi suma suka wuce ɗakin su.
Bayan an idar da sallan ne, Sheykh da kanshi ya ɗauki su Bappa ya kaisu tasha kamar yadda sukace.
Bayan ya kaisune. Yayi musu fatan isa lfy ne, yaja motarsa kamar ya tafi.
Ya koma can baya ya ajiye motar kana ya kira Ado drevernshi da yake cikin but ya fito.
Sannan yace.
"Bisu".
Da sauri Ado yabi bayansu.
Shi kuma yayi gida.
A hankali Ado yake binsu.
Ga mamakinshi sai yaga sun tari taxi sun shiga.
Shima taxi ya tsaida ya shiga,
tare da cewa.
"Bisu duk inda suka nufa."
To yace, kana yabi bayansu kai tsaye international airport Ɓadamaya suka shiga.
Suna shiga.
Kuwa suka fito. Suka biya mai taxi ɗin da kuɗin ma da bana ƙasar Nigeria bane kuɗin ƙasar Cameroon ne.
Cikin sanyi Al'amin yace.
"Yi haƙuri bamu da canji ne, kaje wurin yan canji za'a canza maka su zuwa Naira".
Cikin jin daɗi mai taxi ɗin ya tafi.
Shima Ado ya sallami nasa mai taxi ɗin.
Kana yabi bayansu tafiya kaɗan sukayi yaga wasu mutane a ƙalla su shida, sunbi bayansu duk suna cikin shigar sut.
Al'amin dake gefen Bappa ne ya miƙo wa ɗaya na kusa dashi hannu.
Wayar iPhone ƙirar wannan shekarar ya miƙa mishi.
Sai kuma system ɗinshi.
Daga nan kan tsaye sukaje suka shiga jirgi.
Dole Ado ya rakasu da ido.
Su kuma jirgi ya ɗaga dasu.
Tun kafin Ado ya koma gida ya kira Sheykh ya labarta mishi.
Murmushi Yayi jin abinda Ado yace mishi. Kai ya jinjina tare da danna wasu ababe a wayarsa.
" ?+? ".
Murmushi yayi kana ya jefa woyar a al'jihunsa.
Bai shiga gidaba sai bayan sallan isha'i.
Yana shiga kuwa ya samu su Ummi a falo.
Aysha da hannunta ya ɗan fara zogin.
ta bishi da ido.
ganin kamar bazata tashi bane yasa.
"Umaymah cewa tashi kije ya miki tofin."
To tace kana ta miƙe, ta nufi Side ɗin nashi.
Babu kowa a falon sai dai ta hango shigarsa ɗakin.
A hankali tabi bayanshi tura ƙofar Bedroom tayi tare da sallama.
Kana ta kutsa kai cikin ɗakin.
A hankali ta isa tsakiyar ɗakin babu kowa.
cikin sanyi tace.
"Ina jiranka dan Allah kamin tofin".
Shiru taji ba mgna ba kuma motsin komai a ɗakin.
Cikin sanyi ta ɗan fara hurawa hannunta iskan bakinta.
Tana kallon ƙofar Bathroom ɗin.
A hankali kuma ta miƙe tana cewa.
"Shyyyuuu hahjjyyyyyyyt".
Sai kuma ta matso bakin ƙofar Bathroom ɗin da niyar ta bubbuga ƙofar.
Tana sa hannu bisa ƙofar ta buɗu.
Da sauri ta ɗan ja da baya.
A hankali tace.
"Yi haƙuri bansan a buɗe yakeba".
Still ba mgn kuma ba motsin ruwa.
Hakane yasa ta ɗan leƙa.
Ganin ba kowane a ciki ta kutsa kai ciki tare da cewa.
"To ina kake ina ka shiga".
Shiru wayam ba kowa, komai na bathroom ɗin yana nan fes-fes a kimtse.
Da sauri ta fito bedroom ɗin.
Waige-waige tayi ba kowa.
Haka yasa ta fito falon da sauri tana cewa.
"Umaymah ban ganshi bafa, kuma na hangoshi yana shiga ɗakin.
Na shiga kuma ban ganshiba."
Ummi ce ta amshi zance da cewa.
"Ko ya shiga wonka ne".
Da sauri tace.
"A a baya cikin bathroom".
Umaymah ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ki duba Dinning area ko yana can".
Da sauri ta juya tana cewa.
"Ɗakin fa ya shiga, kuma ban ganshi ba."
Ummi ce tace.
"To kije dai ki ƙara dubawa".
Dube-duben tayi a falon kana ta koma cikin bedroom ɗin wayam fa
A hankali ta ƙarewa wodurob ɗin shi kallo, buɗesu tayi duka, tana cike da mamakin to ina ya shiga, dan tabbas taga shigarsa ya kuma za'ayi baya ciki to ina ya shiga?.
A haka duk ta bubbuɗe durowowin babushi babu alamarshi.
Falon ta sake fitowa tana mai jin zohin hannun yana tsananta.
Ɗaura hannun tayi a kanta tana jin idonta na kawo ruwa.
Umaymah ce ta shigo.
Ƙofar shiga cikin Garden ɗin su ta duba.
A rufe take babu alamun an taɓata ma.
Ƙofar ɗaya ɗakin ta nufa zata buɗe.
"Aysha tace.
"Allah ko Umaymah bai shiga nanba ɗauki shi ya shiga.
Kuma na duba baya ciki tako ina kuma banga fitanshi ba."
"Ikon Allah to ina ya shiga?".
Umaymah ta faɗa tana.
Shiga ɗakin. Jim kaɗan ta fito.
A gefe ta tsaya tana mamaki tabbas dai sunga ya wuce.
Da sauri suka miƙe ganin ya buɗe ƙofar ɗakinshi ya leƙo yana cewa.
"Umaymah lfy kuwa? Naji kunata salati".
Da sauri tace.
"Kai muke nema bamu ganka ba, ina ka shiga Aysha tace baka cikin ɗakin."
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta tare da cewa.
"Uhumm to dama ya za'ayi ta ganni tanata kuka ta gigita kanta ba dole ta makanceba".
Cikin gamsuwa da hakan dan Umaymah ta yarda wata ƙil ciwone ya gigita Aysha shiyasa Bata ganshi ba.
Ita kuwa Aysha cikin zafin tace.
"Wlh Umaymah ba ciwo bane na duba ko ina ban ganshi ba".
Kai Umaymah ta gyaɗa kana tace.
"To kije ya miƙi tofin".
Miƙewa tayi ta nufi cikin ɗakin.
Ita kuma Umaymah ta koma falon.
Raɓawa gefe tayi ta shigo.
Shi kuwa maida ƙofar yayi tare da cewa.
"Zo nan".
Matsowa tayi ya fara yi mata tofin
tana jingine da ƙofar yanayi yana hura mata iska.
A hankali ta fara lumshe ido,
ganin zatayi bacci ne yace.
"To jeki".
Har zata fita sa kuma ya ɗan sha gabanta ido ya zuba mata kana a hankali yace.
"Ke komai kika gani sai kinyi mgn ne?".
Kai ya jujjuya alamun a a.
Gashin girarta ya zubawa ido tare da cewa.
"Bubbuga Rumbun Abboi".
Baki ta ɗan tura tare da cewa.
"Ni dai ba bubbuga Rumbun bace".
Matsota ya farayi ganin hakane ta ɗan ja da baya ta jingina da ƙofar, kusa da ita ya kuma matsowa kana a hankali yace.
"To ke meyece in ba bubbuga Rumbun ba, ko kunya babu kin zauna gaban wanda ba mijinkiba, yana baki abinci har baki".
Gashin tattausan gemshi ta ɗan kalla tare da cewa.
"To nida Yayana ɗan uwana, tunda mai bani Allah ya kawoshi ai sai ya bani kada yunwa ta kasheni".
Murmushi mai sanyi yayi sabida tambaya ɗaya ya mata cikin amsa tambaya ɗayan kuma ta amsa mishi tarin tambayoyinshi. iskar bakinshi ya ɗan hura mata tare da cewa.
"Kince in baki ban baki bane?".
Da sauri tace.
"Toh sai nace ne?".
Ƙara matsowa kusa da ita yayi tare da ɗada mata girarshi ɗaya a hankali yace.
"Na'am sai kin ce mana shima ai ce masa kikayi ya bakin".
Mutsu-mutsu ta farayi jin ƙirjjinshi na danne nata a hankali tace.
"Toh ai shi ɗan uwanane".
Ba zato yaji mgnar ta subce mishi.
"Toh ai Ni kuma mijinki ne".
Sai kuma yayi sauri ya matsa, tare da juya mata baya.
Ita kuwa sumar ƙeyarshi ta zuba ido kana a hankali ta juya.
Cikin lumshe ido ta fita.
Shi kuwa Sheykh wata iriyar sassayar ajiyar zuciya ya sauƙe mai nauyi.
Kana ys cire kayan jikinshi.
Sannan ya shiga wonka.
Bayan ya fitone yayi shirin baccinsa.
Kana ya kwanta.
Ita kuwa Aysha tana shiga ɗakinta ta kwanta sai bacci.
Umaymah kuwa na ɗakin Ummi suna tattauna wata mahimmiyae mgna,
sai ƙarfe sha biyu ta shigo.
Tayi mamakin ganin Aysha konce tana baccin.
A hankali tace, uhum tana tashi zan kai maka ita tunda ka iya kora masu maganin ka kora sarkin bakan masarautar Joɗa kana ka kora wanda iyayenta suka zo dashi.
Daga nan taje tayi al'wala tazo ta kwanta.
A can wani yankin kuma.
Sarkin baka ne da Ɗalhatu mai sa tayis ne,
zaune su, suna musu bayanin duk abinda ya faru.
Dariya tayi mai cike da jin daɗi tace.
"Uhumm ai zanyi maganin ƴan iska watan cin uwarsune ya kama.
Wannan shegen yaro Jabeer Allah ya sani bana ko son ganin fuskarshi.
Duk sanda na ganshi sai inji zuciyata ta tsinke hankalina ya tashi.
Ɗaya dake gefenta ne, yace.
"Aini da inada dama da a daran nan zan kashe shegu gaba ɗayansu."
Kai ta juya tare da cewa.
"Uhum baka san rashin kunya da tijara da magangun da wannan matar tashi mai kama da aljana tayi minba ne.
Shiyasa dole in taka mata birki zanci uwarta zata gane bata da wayo."
Daya na gefenta ne yace.
"Uhummm ni wlh da zan samu wutan zan bunkawa shegu duk su babbake".
Nan dai sukaci gaba da yiwa Ahlin Sheykh tanadin mugunta.
A can cikin dajin kuwa zaune yake gaban bokanshi shi.
Cikin hatsala yace.
"Kace min abubuwa suna gabda nasara amman akwai tsaiko menene tsaikon gaya min shi in kaudashi".
Dariya bokan yayi tare da zazzare idanu kana yace.
"To ka dai san babban abunda ya hanamu nasara kan yaron nan, shine addu'o'in da yakeyi da yawan zama da al'wala da karatun al'ƙur'ani.
To yanzu kuma na gano wannan matar tashi da aka aura mishi idonta a buɗe suke.
"Akwai makaran gado, wanda sukeda ƙarfin iko, ko jiya wata cikinsu tazo tajamin kunnen kada in kuskura in cutar da ita.
Sannan kuma akwai saurayi ta da ya raineta ya shirya mata jiki, kana tana iya gane sihiri a wuri duk ƙanƙantarshi.
To in dai ba rabashi mukayi da itaba ko a kasheta ba tsira zamuyi ba.
Kuma tana iya tona asirin kowa".
Cikin tashin hankali yace.
"Uhumm zata kuwa bar Masarautar Joɗa nan kusa.
In kuwa ta nuna taurin kai tabbas zata bar duniyar nanda bada jimawa ba, bazan bar duk wani abun da zai shiga tsakanina da sarautar masarautar Joɗa ba".
Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu.
Barun kuwa ana korashi ya nufi ƙasar Cameroon, Ba'ana bai iya jiranshi ba, tahowa yayi suka haɗu ya gaya mishi duk yadda sukayi da Sheykh.
Nan suka sake komawa cikin Rugar tasu can inda ya samu sabon uban gida.
Yanaji kamar ya mutu dan baƙin ciki.
Nan yaci gaba da shirya yaƙan Sheykh.
A nan kuwa ɗakin Aysha.
Ƙarfe ɗaya da rabi Aysha ta farka da salati a bakinta.
Cikin sauri ta buɗe idonta.
Tare da miƙewa a hankali ta nufi falon.
Domin taji zogin na dawowa.
Tazo falon kenan ta hango mutun da irin shigar ranan cikin tsoro tace.
"Waye ne kai me kakeyi mana a nan?".
Juyowa yayi ya kalleta cikin isa ya fara takowa zuwa gabanta.
Da sauri ta fara jan baya-baya tana cewa.
"Me hakan? Me kake nema damu?".
Cikin Tsuke fuskarsa yace.
"Me na samu dai. Ai Jahan tun kafin ya nemi abu yake samun abun a hannunshi".
Da ƙarfi ta buɗe bakinta zata zurma ihu.
Taku biyu yayi ana uku ya isota.
Tafin hannunshi yasa ya rufe mata baki tare da cewa.
"Kada ki razana wancan mataccen mijin naki".
Wani irin zazzaro ido tayi tare da jujjuyasu cikin alamun firgici da tsoro da kiɗima.
Kanshi ya jujjuya mata tare da cewa.
"Kada kisa zuciyarki ta buga a banza dan nace wancan mataccen mijin naki.
Ban kasheshi ba, amman dai ke a wurinki dashi da mace yar uwarki ba sauyi".
Hannunta mai lfyar ta fara kiciniyar ɗagawa zata ture hannunshi da ya ɗaura kan bakinta, ya rufe, ya haɗa kanta kuma da jikin gini.
Juyota yayi da ƙarfi ya manna bayanta da ƙirjinshi still hannunshi na kan bakinta.
Ɗaya hannun kuma, bisa ƙirjinta ya ɗaura.
Taku ya farayi yana janta ya nufi hanyar fita woje.
Wani irin bugu zuciyarta keyi tamkar zai faso ƙirjinta ya faɗo woje.
Zuface ta tsananin firgita da tsoro ta karyo mata tako ina na jikinta.
Tuni tsoro yasa numfashin ta ya fara subce mata.
Kiciniyar kwace kanta takeyi ta samu damar yin ihun amman ta kasa.
Sabida ba ƙaramin riƙo yayi mataba.
Hannunshi dake kan ƙirjinta ya cusa cikin rigar ta saman wuyan rigar tata.
Wani irin azabebben cizo ta dartsawa tafin hannunshi,
amman duk da haka bai janye hannun nashi ba.
Sai ma lumshe idonshi yayi tare da jan dogon numfashi mai fitar da ɗimaucewar da yake ciki.
Wani irin shafa yayiwa breast ɗinta, wanda yasashi rawan jiki bnnarsa tayi wani irin azabebben zabura da miƙewa gal.
wani kiciniya ta fara da iya karfinta dai-dai lokacin kuma suka iso bakin ƙofar fitan
Hannunshi dake cikin rigarta ya zaro bayan ya burza nimple ɗin ta.
Murza key ɗin ƙofar yayi ya kana ya jawo ƙofar ya buɗe.
Wani irin karkarwa jikinta ya fara,
Garin son kwace kanta da neman taimakon kanta, ta buge hannunta mai ciwon jikin ƙofar.
Dai-dai lokacin kuma ya janye hannuunshi kan bakinta.
Wani irin razanenne kuma gigitaccen ihu tasa mai sauti.
Shi kuwa Jahan da gudu ya fice kamar walƙiya.
Ita kuwa cikin karkarwa da tsoro da gigita ta juya ta nufi cikin falon tare da zurma wani ihun mai cike da kiɗima