Showing 15001 words to 18000 words out of 189325 words

Chapter 6 - DUKAN RUWA COMPLETE NOVEL

23 Feb 2026

206

ba na yi, sun ce ai kuwa anan da Bichi ba zan rasa mijin aure cikin ?an uwa ba, Anti Maijidda har cewa ta yi ga babban Wanta Yusuf nan, wai ya kammala? gininsa za ta turo shi ya zo mu yi hira mu fahimci juna. Kin taSa jin wannan irin abu don Allah Humaira? Duka-duka nawa nake da za su ce za su aurar da ni yanzu? Zangon karshe nake a Ss1 zan wuce Ss2, idan ma auren suke buri su ga na yi, ai sa bari dai shekaru biyun da suka ragemin a sakandire na kammala su. Haka kawai don wasu mafarke-mafarken da ba su da tabbas ku rushemin ginin rayuwata? Sun bi sun kafawa Mami karan tsana, ban san hawa ba ban san sauka ba, amma nima su na hantarata akan na mayar da ita tamkar uwar da ta haife ni, gani suke na fifita dangin Babana sama da su. Toh don Allah faWamin, mutanen nan sai na je wurinsu duk shekara a can nake hutun dogon zango da ake ba mu na makaranta har ya ?are, amma su ko sau Waya ba su taSa zuwa garin nan da zummar ganina a gidan nan ba acewarsu su da Mami har abada don ba su yarda da zuciya Waya ta ke ri?e da ni ba. Akan Mami na sha duka a wajensu idan na je domin duk wanda ya aibata? ta zan buWe baki nace sam ba haka take ba, to fa anan sai na WanWana kudata. Yanzu wannan matsalar auren da ta taso ki faWamin Humaira, ta ina zan kashe ta ba tare da na samu matsala da su ba, nikam wallahi gaba Waya kaina ya ?ulle."

Humaira ta sauke ajiyar zuciya.

"Wai Allah!" Shi ne abin da ta furta don ita komai ma ya tsaya mata cak, ta rasa me za ta cewa Ummita. Mamaki take yi na yadda suke yiwa Mami kallon baibai alhalin matarnan iyakar kokari tana yi a kansu, irin kokarin da ko mahaifansu na usuli sai haka. Can kuma ta dubi Ummita.

"Toh kodai ki yiwa Abba bayanin komai? Na tabbata zai fahimceki kuma ba zai rasa matakin Wauka ba yadda zumuncinku ba zai taSu ba."

Shiru ta Wan yi, sai kuma ta ce.

"Ko? Nima na yi wannan tunanin, wallahi maganganunsu ke hargitsa ni tun wancan satin su ke huran wuta, tun fa ina dannewa har suka soma sanya ni kuka. Amma hakan zan yi kawai, zan faWawa Abba komai, ke nasan ma kai tsaye zai nemi Kakana wanda ya haifi Mama ya yi mishi magana. Shi kaWai zai iya tsawatar musu, daman tsoro ne ya sa na kasa faWa mishi, amma na tabbatar zai magancemin."

Humaira ta jinjina kai.

"Sai dai don Allah kar ki faWawa Abba zargin da suke yiwa Mami."

Ummita ta kama baki.

"Rufamin asiri Humaira, dama me zai kai ni?"

Murmushi Humaira ta yi. Suka Wan taSa hira sannan ta kyale ta don ta yi karatu.

? Aikuwa a daren Ummita ta samu Abban ta zayyane mishi komai, ransa ya Saci. ?arshe dai ya ce ta tashi ta wuce zai san matakin da zai Wauka. A ranar kashe wayarta ta yi ta kuma yi al?awarin ba za ta kunna ba har sai komai ya wuce don ta tabbata zagi ne dai za ta sha a wurin su.

***
BAYAN WATA BIYU...

Gadan-gadan Humaira ta fara zuwa koyon girki, abin da ya burge su Abba da Mami bai wuce irin haza?arta ba na saurin Waukar abu. Ita kanta Anti Laila sosai take yabawa da Humairar. A farko-farko ne dai idan aka koyar da su ta zo gida ta yi sai ya kasance bai yi dadi ba ko gishiri ya yi yawa ko dai wani abin, har su Tasleem na ci don su yi mata dariya da kuma kushe. Har su na cewa Abba ya yi asarar kuWinsa. Amma yanzu kam duk da su na kaucewa ba su son nunawa a fili yana musu dadi, to fa a ?asan zuciyarsu su na son su WanWana idan ta yi. Amma fa ana ci ana yamutse fuska ana nuna ba laifi ya Wan yi dadi. Ita dai ba ta tanka musu tunda har Abba da Mami da Ummita su na yabon girkinta.

A farko direba ke kai ta, daga baya kuwa Mami ta nemi Wan sahun da zai dinga kai ta kuma ya Wauko ta. Watarana kuwa da aka yiwa Wan sahun rasuwa da kanta ta Mami ta sanya yaron gidan me musu wanki ya raka ta titi ya sanya ta a adaidaita, a dawowa da kanta ta dawo. Tun kuma daga nan ta soma zuwa da kanta ta dawo, a karshe kuma ya kasance koda Wan sahun bai zo ba ita ke zuwa ta dawo. Ganin ta gane hanya ya sa Mami kawai ta sallami Wan sahun ake ba ta kuWin mota.
Komai idan ta koya tana samun Wan littafin da Ummita ta bata ta rubuce tsaf da hausar ajami. Rubutunta mai Wan karen kyau da burgewa har ya kasance Ummita ta yi ta santin handwritting din.

A bangaren Islamiyya kuwa, kusan tare suke tafiya da Ummita a aji duk kuwa da cewar a can karatunta ya zarta na su, akwai abubuwa da dama da ta sani na daga litattafan addini wanda na ajin ?an gaba ne. Hakan ya sa idan ba sa komai ta ke zama malamar Ummita. Su yi ta karatunsu musamman yanzu da ake cikin hutun dogon zango na makarantun boko. Idan ka cire Tasleem da Futuha sai samarin, babu wanda ke zuwa makaranta. Gidan sai yake yiwa Humaira daWi fiye da a baya.

Ranar wata Asabar da yammaci su na zaune a Wakinsu, Humaira ke taya Ummita gyaran sif Winta, gaba Waya sun sauke kayan Ummitan saman gado. Humaira sai tsokanarta take yi akan da tuni yanzu an sanya ranar aurenta da Yusuf, ita kuwa tana kai mata bugu da ninkakkiyar rigarta. Sai kuma ta ja guntun tsaki ta zauna gefe tana murmushi.

"Ke nifa ina da mijin aure a hannu, kawai dai bai taSa zuwa gidannan ba, ba na so kowa ya sani sai na kammala karatu."

Humaira ta zaro ido da wani irin zumuWi ta ce.

"Don Allah dagaske? Waye wannan mai sa'ar?"

Ummita ta Wan harareta sai kuma ta mi?e ta ci gaba da ninkin da take yi.

"Oho, idan ta yi wari kya ji."

Duk irin magiyar Humaira dai ba ta samu Ummita ta furta komai ba, da ta ga hakan ba mai Sulla bane sai ta sauya ta ce.

"Toh abu Waya za ki faWamin, Allah kuwan daga shi ba zan ?ara tambaya ba. Na san shi, na taSa ganinsa? Eh ko aa?"

Dariya Ummita ta yi.

"Wai ni za ki yiwa wayo ko me?"

Itama dariyar ta yi.

"Allah ba wayo ba, kawai ina son sani."

Ummita ta Wan yi shiru, ta sani idan har ta ce mata ta san shi to za ta ?ara damuwa da son ji ita kuwa duk data yarda da Humaira ba ta shirya kowa ya ji yanzu ba. Sai ta girgiza kai.

"A'a toh."

Jin haka Humaira ta taSe baki.

"Toh shikenan, idan ta yi wari ma ji."

Kafin Ummita ta tanka sai ga Muhsin ya shigo a guje.

"Adda Humaira, ki zo inji Mami za ku gaisa da Yaya Kabeer."

Humaira ta ji kanta ya yi wani dum, wani irin Sacin rai da bakin ciki na taso mata da ba ta san silarsa ba. Nan da nan ta haWe fuska tamau kamar ba ita ke dariya yanzu ba.

"Ka ce gatanan zuwa." Ummita ta amsa jin ba ta da niyyar amsawar. Ta sani Humaira ta tsani Kabeer, tun ganin da ya yi mata a gidansu tare da Mami yake bibiyarta. Amma yadda fuskarta ta sauya ita kam ba ta taSa ganinta cikin wannan yanayin ba.

"Ke lafiya? Daga ance maki Kabeer ya zo?"

Tsaki ta ja ta mi?e a fusace cike da wata iriyar tsiwar da ita kanta Ummita ba ta san ta da ita ba ta ce.

"Aikin banza da wofi, na tsani naci da takura wallahi. Mutum sai shegen naci, itama Mami ta biyemishi har da wani aikowa a yi kirana." Ta kara jan tsaki. Maganarta na karshe kan kunnen Raihana da ta shigo Wakin tana danna waya, baki buWe take kallonta.

"Ke, Mami za ki yiwa rashin kunya? Har da tsaki?"

Ko kallonta ba ta yi ba ta juya ta ci gaba da ninkin kayan da alama ba ta da ko niyyar tashi balle ta je. Ummita ta kalli Raihana itama ta dube ta, a fusace Raihana ta karaso ta fisge rigar dake hannun Humaira ta yi jifa da shi. Humaira ta mike a zuciye ta ce.

"Malama na fada! Nace na fada! Kabeer din banza da wofi! Ba zan je ba din akwai abin da za ki iya yi? Ko waye ya tilasta ni shiga lamarinsa sai na gasa mishi maganganun da zai yi dana sani!"

Raihana gaba daya ta tsorata, kamar dai Humaira kamar ba ita ba. Kawai sai ta gifta ta fice daga Wakin ba tare da ta tanka ba don dama Raihana akwai tsoro. Ummita ta mike ta kama hannun Humaira a sanyaye.

"Humaira, lafiyarki kuwa? Me ya yi zafi?"

Ba ta ce komai ba kawai ta zare hannunta a cikin na Ummita, zama ta yi ta yi shiru sai huci ga gumi na tsastsafo mata. A haka Mami ta shigo dakin, Raihana duk ta ba ta labarin abin da ya faru, kallon Humaira take yi a nutse, sai kuma ta karasa ta zauna gefenta. A hankali ta dafe hannunta. Humaira ta kalleta, kawai sai ga mamakinsu ta fashe da kuka.

"Mami don Allah kiyi hakuri, wallahi na tsane shi, ki ganinsa bana son yi. Kiyi hakuri don Allah ki janye batun zuwa mu gaisa da shi."

Wani irin kuka ne da sheshshe?a tamkar wacce ake kokarin raba ta da numfashinta. Mami da Ummita wacce duk ta firgice suka dubi juna sai kuma ta rungumo Humaira.

"Kar ki damu, ya tafi ya bar gidan ma. Kuma na yi maki al?awari Kabeer ba zai ?ara takura maki ba. Kin ji ko?"

Sai a sannan ta gyaWa kai ta bar kukan, lokaci guda kuma ta fara dawowa hayyacinta. Ita dai Ummita ikon Allah ta zubawa ido tana kallo. Abin dai kamar a wasan kwaikwayo.
Dare ne misalin karfe Waya da mintoci, Wakin ya yi shiru ban da munsharin Tasleem ba abin da kan addabesu kullum ba abin da ke motsi. Humaira wacce abu biyu suka hana ta sukunin bacci, ta zubawa tagar Wakin ido tana kallon farin wata da ya hasko har cikin Wakin nasu. Garin babu zafi sai iska dake kaWawa kaWan kaWan hakan yasa rashin wutar bai hana mutanen gidan sukuni ba. Ta ja guntun tsaki ta mi?e zaune gami da runtse idanunta.

_'Humaira ba ki kyautata kalamai ga Mami ba. An sani maganar Kabeer kika tsana, sai dai yanayin da kika yiwa Mami magana kamar wata Humairar aka chanja ba ke ba. Idan kin yiwa Raihana wannan dama abokiyar yinki ce, amma ga Mami, kin yi kuskure.'_

Ta tuno kalaman Ummita, wannan na daga cikin abin da ya damu zuciyarta, Mami fa, matar da ta ke ba ta kulawa da zuciya Waya. Ta maye mata gurbin Dada da Mamarta wacce ba ta buWi ido ta gani ba. Ta kuma zame mata abokiyar hira a lokuta da dama idan tana zaune ita kaWai a gidan. Hakan za ta dinga ba ta labarin Nijar itama ta ba ta na ainahin garin iyayenta wato Agadez su yi ta nishaWi.

Abu na biyu da ya tsaya mata a rai bai wuce na mamaki da tunanin abin da ta yi Win ba. Eh ta san ba ta son Kabeer, ta tsani ma ganinsa, amma tsanar har ta yi yawan da za ta kasa Soyewa har haka? Ita kam abin ya sha mata kai.

Tana nan zaune dai ganin Satawa kanta lokaci da tunani take yi da b zai magance mata komai ba sai kawai ta maida kai filo a hankali bacci ya sure ra. Duka wannan zaman da ta yi har zuwa kwanciyarta akan idanun Raihana wacce munsharin Tasleem ya hana ta sukunin bacci. Tsoron yarinyar ya ?aru a zuciyarta, ta kasa kwakkwarar motsi ga fitsari cike fal a mararta amma ina, ga ni take ai tana mi?ewa Humaira za ta tashi ta sha?e ta don ta gama ba zuciyarta cewar iskokai ne da Humairar. A wannan daren dai bacci Sarawo ne ya sace Raihana.

***
Ta kammala shirinta tsaf kamar koyaushe za ta wuce wurin koyon girki, ta fito falon. Ummita na zaune tare da su Muhsin a falon, Raihana kuwa na gefe Waya ta hakimce tana abin da ta saba, latse-latsen waya. Ganin Humaira yasa ta kalle ta sau Waya ba ta ?ara ba don ita ba ta so ma su haWa ido, har ga Allah tun can tana tsoron mai aljanu. Tana kuma shakkar yi musu rashin kunya tun wataran tana jss 2 da wata abokiyar karatunta ta sha?e ta akan ta zauna a kujerarta ta kuma yi magana amma ta ?i tashi. Da ta fusata ta sha?o wuyanta sai da malaminsu ya kwace ta. Abba har makarantar ya je, iyayen yarinyar suka ba da hakuri aka kuma sauya musu aji. Tun daga nan ta ke tsoron duk abin da zai danganta ta da mai iskokai. Ko kusa da su ba ta raSa.

"Har kin fito kenan?" Ummita ta tambaya tana kallonta fuska a sake. Itama murmushin ta yi.

"Na fito, ina Mami?"

"Tana sashinta." Daga nan ta nufi sashin Mamin, a falo ta iske ta tana waya tana dariya, ganinta yasa ta yi sallama da Waya Sangaren ta ajiye waya. Cike da walwala ta ce.

"?ar Mami har an fito?"

Kunya ta kamata, ita kunyar Mamin take ji wallahi, ta karasa ta durkusanta gaida ta.

"To, wata sabuwar gaisuwa ce nan ban da wacce muka yi Wazu?"

Mamin ta faWi cikin wasa da dariya, Humaira dake sunne kai ta Wan murmusa, ita ta manta ma sun gaisa Win. Mamin ta ?ara magana.

"Au, ashe gidan Laila za ki ko? Bari ma na ba ki sa?onta ki tafi da shi." Mamin daga haka ta mi?e ta nufi Waki, can ta fito Wauke da leda wacce Humairar ba ta san ma ko mene ba ta karSa. Ta ba ta kuWin mota tana fadin.

"Abbanki ya riga ya fita na mance ban karSar maki na motar ba, ki je kawai idan ya dawo sai na karSa."

Ta gyaWa kai ta sa hannu ta karSa da godiya, ganin ta ?i motsawa balle ta tashi ya sa Mamin tattaro nutsuwarta gareta.

"Lafiya Humaira? Akwai magana a bakinki ko?"

GyaWa kai ta ?ara yi a karo na biyu, cikin nutsuwa kuma ta soma magana.


"Mami dama akan abin da ya faru jiya ne, ina neman gafara."

Murmushi Mamin ta yi ta girgiza mata kai.

"Kar ki damu, ni nasan ba laifinki ba ne. Hakan ya sa na yi maki uzuri. Ki cire komai a ranki kedai ki tattara nutsuwarki ki cigaba da maida hankali ga darussanki. Laila na ta yabon kwazonki don haka ki ?ara dagewa, na maki al?awarin Kabeer ba zai ?ara shiga sabgarki ba, kin ji ko?"

Sai a sannan ta sauke ajiyar zuciya ta samun nutsuwa, ta amsa da toh daga nan suka yi sallama ta mike ta fita, Mamin ta bita da kallo tana murmushi.

***
Tu?i Wan sahun ke yi cike da nutsuwa, sosai tu?in ke mata daWi yayin da iskar dake kaWawa a garin ke ?ara jefa ta cikin walwala. Damuwar da ta kwana da shi a ?ar?ashin ranta, tas ya wanke ya koma annashuwa. Don haka murmushi take yi ma ba tare da sanin tana yinsa ba. Ba zato ta ji ta yi wani irin hantsilawa sai ga ta a bayan Wan sahun nan hannayenta rungume a kan wuyansa kai kace wacce aka goyo. Shi kuwa Wan sahun kansa ya ?umu da jikin gilashin da karfi har sai da gilashin ya tsage, saura kaWan adaidaitar ta wuntsila amma Allah ya ta?aita faruwar hakan, sai ya koma baya da ?arfi har tayoyin na bugun ?asa da ?arfi, wannan ya sa ta koma mazauninta, lokaci guda ta saki ?ar guntuwar ?ara sakamakon cikinta da ya bugu da ?arfen jikin mazaunin direban yake mata zafi dalilin buguwar da ta ?ara yi dalilin komawa baya. Ta runtse idanu daidai sadda ta ji salatin jama'a a kansu. Gaba Waya ma ta kasa buWe idanunta tana dafe da cikinta, ta yi shiru kawai don hayaniyar ma ba burge ta take ba.

"Sannu ?anmata, sauko."

Ta tsinkayi Waya daga cikin jama'ar wurin na fadi, wasu kuwa na hayaniya su na fadin ai laifin mai motar ne. Can kuma ta ji an ce.

"Alhaji kai ne da laifi, kai ka bugi motarsu garin cin burki a kurarren lokaci."

Ta buWe idanunta a hankali jin wani daddaWan kamshi a gefe, a hankali ta sa hannu ta Wauki jakarta da ta tarwatse a ?asa, duk tarkacenta sun zubo. Wani matashi ya shiga tattara mata ita kuwa tana son ta fito a adaidaitar kamar yanda Wan sahun ya fita ya zauna gefen kwalta, amma ina tururuwar mazan dake wurin ya sa ko motsin kirki ta kasa. Da murya irin ta manyan mutane ya amsa.

"Baba, ba abin zafi ba ne. Na sani ni keda laifi, ina mai ba da hakuri garesu. Zan kuma yi kokarin gyara Sarnar da nayi. Ku yi hakuri don Allah."

Humaira ta juya ta kai duba ga mai maganar, daidai lokacin da shima ya Wan rankwafo don ya yi mata sannu da kuma neman alfarma akan ta sauko su je asibiti. Kalma Waya ta kasa fita a bakinsa da ya yi nauyi. ?afafunsa suka soma ?o?arin kayar da shi. Zai iya rantsuwa ba kaffara son budurwar yarinyarnan yake da idan da ace Uwargidansa ta yi haihuwar wuri to fa ya ci ya yi haihuwar fari da ita. A Sangaren Humaira kallon da ta bishi da shi bai wuce na son ganin marar hankalin da bai iya tu?i akan ?a'ida ba har yake shirin kai ta barzahu. Babban mutum wanda ba gigin kuruciya tattare da shi, ya sha manyan kayansa har da babbar riga da hula. Kana ganinsa dai ka ga wanda ya ba arba'in baya. Ganin yadda ya ?uramata idanu sai nan da nan ranta ya yi masifar Saci, ta ja tsaki wanda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login