Showing 144001 words to 147000 words out of 186041 words

Chapter 49 - MATAR DAMISA book two complete novel

ASMEETI   

08 Oct 2024

53944

ta tsoritar da ita, duk Aljanun da sukayi gigin raɓan jikinta zasu iya ƙonewa, wannan sihirin yana nan a jikinta kuma haka shima kansa,
kuma duk mai Aljanu indai Sarki Raamud ya ganta saiya san tanada akwai, saboda ya zauna dasu kuma yanada alaƙa sosai dasu, kamar ita Hafzat yana ganinta yasan tanada Aljanu akanta amma saidai Aljanunta ba masu cutarwa bane shiyasa baiyi magana akansu ba, Aljanunta masu yawan ibada ne haka kawai tana cikin bacci zasu yanke mata baccin ta tashi tayo alwala taita salloli, kuma lokacin sallah yana yi bata barin lokacin ya wuce zata tashi tayi ga yawan azumi da tasbihi kuma intaji anyi karatun Alkur'ani sau ɗaya a gabanta zata riƙe a ƙwaƙwalwarta yanzu sauƙar Alkur'ani Hafzat sau biyar, tayi na waresh sannan tayi na hafs, shu'uba, ƙalun, warshu, durii, susii, ƙumbul, bazzii, ibni kasiir, duk tayi sauƙa akan su ...

Ayush kifar da kanta tayi akan table tana kuka jin yanda ake ta janyo mata Aljanu an ɗauketa mahaukaciya,
tana cikin kukan taji Abbanta yace "Ɓingel Abba zo mana..."
tana jinsa amma ko motsi batayi ba, ya sake ƙiranta taƙi amsawa nan ma! Junaid ya juyo yana kallonta cikin ɓacin rai yace "ke ba magana ake miki ba?..."
ɗagowa tayi tana kuka ta taso kamar mai tambayar ƙasa da haka ta ƙaraso cikin falon fuska duk tayi ja da idanuwanta, tsayawa tayi ta kasa zama saida Abbah ya sake yi mata magana yana ƙiranta cikin lallami yace "zo ki zauna anan maza Ɓingel Abbah..."
zuwa gurinsa tayi ya riƙo hannunta ya zaunar da ita a tsakiyar su shi da mommy, tallafo fuskar Ayush mommy tayi ta juyo da ita suna fuskantar juna tace "Ayush ki dubi fuskarki yanda duk ta kokkoɗe lokaci guda? dan Allah ki sanar mana meyake faruwa dake, idan bakya son Auren nan ki sanar mana mu zamu san yanda zamuyi, muna buƙatar ganin farin cikin ki..."
kuka Ayush take ta juyar da kanta gefe gaba ɗaya ta rasa meyake mata daɗi a ranta, Uncle Artaff ne shima yayi mata magana yace "Ayshert ki faɗa mana meyake damunki ne haka?.."
Junaid yace "ku rabu da ita kawai.." Uncle Artaff yace "a'a ka barmu da ita kawai dole musan ƙwaƙƙwaran hujjarta na cewa bata son Auren ."
Ayush hararar Junaid tayi tareda cewa "wai kai Uba nane kam.." ciki-ciki tayi maganar ba tareda sunji abunda tace ba saidai sunji kamar tana gunaguni,
Junaid kallonta yayi cikin rashin fahimta yace "me kika ce?.."
duk babu wanda yaji abunda tace sai mommy da Abbah dake a gefe da gefenta suke, murmushi mommy tayi tareda sunkuyar da kanta tana murza zoben yatsanta,
Uncle Artaff yace "kaga Junaid ya isa haka, yakamata kana sanyaya zuciyarka kaga matarka ce kar ka shiga hakkinta..."
sannan ya dawo da ganinsa kan Ayush ya kuma cewa "ehen muna jinki Ayshert..."
tana motsi da lips ɗinta kamar mai yin magana tace "babu komai.."
Hafzat tana zaune a ƙasan carpet tana tunanin dalilin da yasa Ayush bata son Auren nan kuma alhalin abun farin ciki ne...
shi kuwa Judan tashi yayi yabar falon ganin tattaunawa ne akan ahalin gidan bai shafeshi ba, bayan ya bar wajen itama Hafzat tashi tayi zata tafi kasancewar maganar manya ne, har ta fara tafiya mommy ta ƙirata tareda faɗin "Judan ya manta earpiece ɗinshi ɗauka ki kai masa, saida Hafzat taji rass a zuciyarta saboda tasan naci irin na Judan yanzu saiyace zai tsayar da ita, ɗauka tayi jiki a sanyaye ta nufi part ɗinsa...
itama Aunty Zainab tura yaranta tayi akan suje suyi wasa..

Uncle Artaff yace "Ayshert magana muke miki meyasa bakya son Hajia Fateema ta raɓi mahaifinki? Alhali ta temake ki a rayuwa ta baki gata, ta nuna miki soyayyar gaskiya, ta riƙe ki tamkar mahaifiyarki, inda ace cutar dake zatayi toh da tin farko bata kawoki gidanta ta zamar dake mutum ba,
da farko kinsa musu wuta a gida kuma kinsan Hajia Fateema tana gidan kinyi niyar ki ƙonata Allah kuma ya kawo mata agaji, idan ace wata ce da tinin kun raba hanya domin zata ɗauka ke maƙiyiyarta ce amma mai? saita danne hakan a zuciyarta ta gagara cireki a ranta kuma ta cigaba da zama dake, ta ɗauke ki tamkar ɗiyar data haifa a cikinta amma ke baki ɗauketa a matsayin mahaifiya ba, ganan yaronta shi da yake ganin mahaifiyarsa ce ai koda wasa bazai taɓa gigin cutar da ita ba,
kinzo kinyi nadama daga baya munji mun karɓi tuban ki amma meyasa yanzu kuma abun ƙaruwa da farin ciki yazo mata kuma kike mata ƙyashin samunsa ko hassada da baƙin hali! kenam kin nuna mata cewa ke butulu ce kenam? kuma a hakan mijinki zaiso ki bayan yasan bakya son mahaifiyarsa? Ehhh...."
ya ƙarasa maganar cikin fushi yana zazzaro mata Ido domin Uncle Artaff bai taɓa shiga ɓacin rai irin na yau ba, koda a baya datasa wuta a gidansu ma ransa ya sosu amma bai nuna mata ba saboda a lokacin basu san alaƙar da ke tsakaninsu ba,
Daman can Uncle Artaff (malam Lawan) ya fi su zafin rai sosai kuma zai fito ya gayawa mutum magana koda ran mutum zai ɓaci,
mai sanyin zuciya daman Máahmud ne baban Junaid shi wannan mai haƙuri kenam ko kaɗan bashida matsala, kuma ba'a taɓa samun wanda akace yayi faɗa dashi ba,
Sarki Raamud kuma shi saidai mugunta, duk wani aikin mugunta ya iya shi tin yana yaro, amma yanzu kam Masha Allah ya daina wannan muguntar nashin...

Ayush fashewa tayi da matsanancin kuka jin yanda Uncle Artaff yake gaya mata maganganu, daman da farkon yana sassauta mata ne saboda baƙin fuskokin da suke wajen bayaso yayi magana awajensu da kuma yaransa tinda yanzu sun tashi sun tafi iya yasu-yasune hakan yasa ya buɗe mata wuta,
Sarki Raamud shima sam baiji daɗin maganganun da ya gayawa Ɓingel ba, kawai dai ya sharar ne,
jin tayi shuru sai faman kuka take tayi yasa Uncle Artaff ya darara mata tsawa tareda faɗin "magana nake miki Ayshert yakamata ki kawo karshen ƙudire-ƙudiren da kike yi akan wannan Ahali biyu da kika zamo musu ƙarfen ƙafa, banda mugunta babu abunda kika iya kenam? wani irin baƙar zuciya gareki ne? kodai muguntar da mahaifinki yayi a baya ne ya dawo kanki?...."
Sarki Raamud gaba ɗaya zuciyarsa tafasa take da jin kalaman Artaff, mommy ce ta dakatar dashi tana bashi haƙuri da cewa "kayi haƙuri Malam, mu saurara muji daga bakinta..."
ta dafa kafaɗar Ayush tace "kiyi haƙuri Daughter kinji yanzu gaya mana abunda yake zuciyarki..."
Ayush ta gagara dakatar da kukan da ya kuɓuto mata domin anyi mata bahagon fassara da mummunan zargi akan wai bata son Mommy..."
daƙer ta iya dakatar da kukan tace "Ni Allah yaga zuciyata mommy abun alfahari nane, koda wasa ban taɓa jin haushin mommy ko kaɗan ba acikin zuciyata, mommy tamun halacci a rayuwata wanda har ƙarshen numfashina bazan taɓa mantawa baaa..."
tana kuka gaba ɗaya ta fita hayyacinta, eyes ɗinta sun zama jajawur har dishi-dishi take gani tsabar kukan data sha, ta cigaba da cewa "nasan kuna jin haushi na amma kuyi haƙuri idan na mutu shikenam, ina roƙon Allah yasa wannan cikin dake jikina ya zamo ajali na da zaran na haifa muku Baby...".
ta ƙarasa maganar tana kallon Junaid wanda kansa yake kallon ƙasi tin lokacinda uncle Artaff ya soma magana...
lumshe idonta tayi ta matso hawayen da suka kwanta mata akan idonta tana jan numfashi tace "Indai haka halina yake nima nayi Allah wadar da kaina, bansan meye butulci ba saboda tinda mahaifiyata ta haifeni babu wanda ya taɓa temako na sai mommy, itace macen farko dana buɗe idona na ganta a gabana a matsayin bare kuma har ta temakeni ta mayar dani mutum,
Bansan meyake damuna ba, haka kawai sai in yanke hukunci cikin rashin tunani da hankali, idan akace nayi gabas ni kuma sai nayi yamma, wallahi bansan me yake damuna baaa, bansan meyasa banason Auren mommy da Abbah ba, haka kawai nake jin ƙunci a zuciyata..."

Uncle Artaff kallon sarki Raamud yayi sannan yace "akwai wani abu wanda yake tattare da ɗiyarka kuma abun daga sashinka ya fito..."
sarki Raamud kallon Artaff yayi cikin rashin fahimta yace "nidai nasan Ɓingel batada Aljanu..."
Uncle Artaff yace "kai wannan kawai ka sani amma bakasan abunda suka ajiye maka ba..."
girgiza kai sarki Raamud yayi kwata-kwata bai fahimci abunda Artaf yake nufi ba,
Uncle Artaff ne ya kalli matarsa Zainab yace mata "a cikin jakar hannunki akwai wani abu a leda ki miƙo mun...". kamar yanda yace haka kuwa tayi sannan ya ce wa Ayush tazo gabansa ta zauna...
itama hakan tayi jiki a sanyaye ba ƙwari, durƙusawa tayi a gabansa tana hawaye, wani ɗan ƙaramin ƙwalba ya ciro ya buɗe murfin sannan ya tsiyayi wani farin Ruwa yace mata "buɗe bakin ki..."
ta buɗe bakinta cikin fargaba da tsoro haka ya bata wannan ruwan sannan ya mulmulka mata akan goshinta, yace "buɗe cikin ki.."
haka ta ɗage rigarta ya shafa mata wannan ruwan..
Ita dai ta gagara ganewa duk wannan na menene,
lokaci guda ta fara jin wani irin zafi da raɗaɗi ajikinta, kayinta ne ya soma juyawa kamar wacce tayi maye! hankalinta ne ya fara barin jikinta, ƙoƙarin tashi ta soma yi Uncle Artaff yayi saurin riƙota ya zaunar da ita,
cikinta ne ya soma juyawa nan take ta ƙwanta aƙasin carpet tana shure-shure tareda ƙwalla uban ihu, launin kalarta duk ya sauya zuwa yellow tarr, ga wani irin ihun da takeyi tana birgima a tsakiyan falon,
Mommy ganin yanda Ayush ta koma yasa ta ƙanƙame Abbah tsabar tsoro, shi kuwa Junaid hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ganin Ayush a cikin wannan halin, har ya motsa zai zo yanda take Uncle Artaff yayi saurin dakatar dashi ta hanyar ɗaga masa hannu kuma idonsa a rufe,
jin ihun da ake yi ne yasa su Hafzat da Judan suka yo falon da saurin su, ganin Ayush ta koma yellow yasa Hafzat rungumar judan jikinta na kakkarwa,
a hankali Uncle Artaff yazo ya ɗage mata rigarta sama yana tofa mata addu'o'i cikin ƙanƙanin lokaci saiga wani ɗan ƙaramin maciji ya fito ta cikin cibiyarta, a lokacin ne Ayush ta dakatar da yin shure-shure ta rufe idonta gaba ɗaya ko motsi bata ƙara yi ba,
Ganin haka yasa mommy tsorita sosai kawai addu'a take ta faman zubawa, Junaid gaba ɗaya jikinsa ne yahau ɓari ganin wannan masifar,
Duk waran babu wanda bai firgita ba,
suna cikin wannan halin saiga wani irin baƙin hayaƙi ya bayyano wani gabjejen mutum ne ya tsaya a cikin hayaƙin, tsayinsa ya kere fankar falon gashi baƙi ƙirin dashi sai ƙaho guda biyu akansa kamar rago, idanuwansa jajawur yana sanye da baƙar riga har ƙasi,
Mommy ganin wannan Aljanin yasa ta sumewa akan Sarki Raamud, itama Hafzat suma tayi ganin abunda yafi ƙarfin ƙwaƙwalwarta, Judan bai san lokacin da ya riƙota ba sauran kaɗan ta faɗi ƙasi dake a tsaye suke,
Aunty Zainab matar malam ma suma tayi akan kujera Allah yaso yaran basa nan da ƙwaƙwalwarsu ce zata zauce,
Judan rungumar Hafzat yayi ya ɓuya a bayan kujeru da ita,
Shima Junaid da gudu yazo gefen Uncle Artaff ya tsaya kayuwansu a sama suna kallon baƙin Aljani,

Cikin dirarren murya baƙin Aljani yace "meyasa ka ƙirawo ni ARTAFF?..."
Uncle Artaff yace "na ƙira ka ne saboda ka cire hannunka akan wannan yarinyar ɗiyar sarki Raamud..."
wani irin Dariya baƙin Aljani yayi sannan ya haɗe rai yace "indai akan wannan ne kayi kuskuren ƙira na domin sarki Raamud shi da kanshi ya sadaukar mana da ita..."
Sarki Raamud a tsorace yace "Ni kuma? yaushe mukayi haka dakai?.."
Baƙin Aljani yace "RAAMUD bayan kaje mana da buƙatun mu baka ko wani irin tsafi shin ya mukayi dakai? munce muna buƙatar jinin yaronka, kace bakada matar Aure balle yaro anan ka sanar mana cewa saidai jinin yaron ɗan ɗan-uwanka! Nace maka jinin yaron zamuyi amfani waran tayar da damisan ku!!!
ta hanyar Damisa kuma zaka samu ko wani irin tsafi, mu muka sanya maka hannu akan ko wani irin tsafe-tsafe da kakeyi, amma da sharaɗin duk lokacin da ka karya mana tsafin da muka baka to kuwa zamu bibiyi ɗaya daga cikin ahalinka ko ɗanka ko ɗiyarka amma baza muyi amfani da yaron daka kawo mana jininsa ba saboda shi ya gama mana amfani, bazamu ƙara shiga rayuwarsa ba saidai mu shafi wani daga cikin jininka kuma ta hanyar nan zan gama da ahalinka gaba ɗaya,
Bayan tsafinka ya karye mun bibiyi ɗiyarka wato jininka ba tareda saninka ba, kayi nasarar toshe kafar da zamu turo mata Aljanu amma saidai mun ajiye mata macijin huda a cikinta bayan ta cire zoben dish daga cibiyarta, daga lokacin ta zamo namu kuma muka tusa mata rashin imani a lokacin da muke so tayi mana wani aiki,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login