Showing 111001 words to 114000 words out of 188741 words
Abdallah? aure! RAUDA kin san menene aure kuwa? menene dalilin da zai saka ki aure shi ki halaka kanki a banza a wofi? an gaya maki shi idan baya son ki zai aure ki ne?, rayuwar aure fa ba rayuwar wuni guda bace wace za'a ce ka je kawai wuni daya ne ka jure , a kan me kika yarda kika....."
"Dan Allah ki rage muryarki, kar ki yi Mah ta ji, dan wanda kike tambaya ta ko wanene nima ban san ko wanda nake tunanin bane, haukana ke sakani tunanin shi ne, saboda abubuwan da suka hada Ni da shi, kuma walahi walahi Ni dai a yanzu Ban san shi din bane wanda kike tambayata a kai ba, ina zargin haka din ne kawai, kar ki yi Mah ta ji ki!" RAUDA ta fada muryarta a raunane, tana langwabar da kai dan ta ga ATU zata zuba mata hauka, bayan ita dai ta san eh lalle abinda ke cikin zuciyarta mai karfi ne da take tunanin an wulakanta mata zuciya, ama bata san takamaiman abinda take yiwa din in shine wanda ya yi mata msg ko ba shi bane
Salima da ta yi mutuwar Zaune tana kallon su cike da rashin fahimta ce ta taso da sauri ta amshi message din ko zata gane abinda suke yiwa din?
a lokacin da ta diro ta karbi wayar ta karanta numbar dake kai, kanta ya mahaukacin daurewa zata karanta sakon da numbar ta kunsa RAUDA ta saka ihu, har tana manta cewar wai bata da lafiya ne, ta diro a haukace ta warce wayar, daidai lokacin da Salima ta budi baki ta fara magana daidai lokacin ne kuma aka turo dakin aka shigo, SALIMA kuwa na fadin" WANNAN DIN, AI NUMBAR MALIK CE, NUMBAR BAH KARAMI CE, ME YAKE FARUWA NE?"
🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹🙄🙄 Gandar rubutu ta kama mar'atusaliha
a zo a yiwa mar'atusaliha solidarity a ringa karbar BONANZA ta LITATAFAINA SU 22 CIF a farashi mai RAHUSA 1k, 1k 1k
93811618 ne numbana
Sarai furucinta ya sauka a kunnen Mah, sai dai ba zata iya tantance abinda yake faruwa ba a lokacin da ta shigo dakin ta gansu a tsaitsaye tamkar zakarun dake fada
A tausashe Mah ta ceX Lafiya? ko jikin na baby ne?"
RAUDA ce ta yi gaggawar ba Mah amsa cewar" Ba komai Mah, fira ne muke yi"
hakan ya sa sauran kallonta, har Mah ta idasa shigowa tana fadin" To alhamdulilah haka nake son ganninki, ku yi zaman ku wajen nan Bama zai zaunu ba, zuwa yamma za'a kai ki wajen Hajia baba in sha Allah kafin a kaiki dakin ki, Atu kina da baki ne?"
Bara'atu ta ja numfashi a hankali ta ce" Eh Mah, mahaifiyata da daidaikun mutane zasu zo ama idan sun zo din zan zo na kai su wajenki su zauna saboda nan din ba zai yiwu ba"
Mah ta karasa ta dauki abinda zata dauka ta fice
tana fita Salima ta je da gudu ta saka ky a dakin sannan ta dawo tana kallon RAUDA ta ce" Bani msg din na karanta, menene a cikin msg din? me yake damunki ne? yaya aka yi na ga numbar ta yayanmu ce? numbarsa ce, pvt numbarsa, nima na hadaceta ne saboda yawan kiran Mah da yake yi da numbar "
RAUDA ta jimke wayarta ta kai zaune saman kujera tana hankalce da su
Atu ta ja wani irin tsaki ta zauna tana dafe gaban goshinta, a kufule ta ce" ki warware min abinda yake damuna tun kafin na hargitsawa kowa tunani a gidan nan RAUDA"
RAUDA ta sake hade fuska ta ce" Ke wai me kike so na fada maki ne?, abinda kike tunanin ba haka bane, kuma Ni na bada amsa ne a cikin lalube"
Jikin Bara'atu ya karra yin sanyi, Salima kuwa ta idasa shigewa a cikin duhu, dan gaba daya ta rasa inda tunaninta zai sauka a irin wannan lokacin
Shiru Bara'atu ta yi mata, ita kuwa ta yi tsuru tsuru, wayar nan a damke a hannunta, ciwon dake zuciyarta sai ta dane shi ta hanna shi kuma fitowa domin ba zata taba yarda wani nasa ya san abin nan ba, ba zata yarda ba sam!
Salima ta jima tare da su, a dole ta sake tafiya saboda baki ne da ita sosai kuma sunna ta kiran wayarta
Tana Fita Atu ta sake tado zancen tana kallonta cikin ido ta ce" Ki dan bani haske, RAUDA me hakan yake nufi? soyaya kuke yi da shi?"
RAUDA ta girgiza kanta a hankali, sannan ta sake dago idannuwanta ta zuba mata su a raunane sosai ta ce" Kina tune da ranar da na ki zuwa makaranta safe da yama, har washe gari kila zo gida tunda sassafe kika ga ko Lafiyana?"
Atu ta daga mata kai, dan a lokacin sai da RAUDA ta yi kwana uku cif bata fita ba
RAUDA ta yi murmushi tana girgiza kanta ta ce" A ranar da na fita da wani saurayina da dare yace zamu je mu siyo abinci, da muka je siyan abincin ashe da aka zuba nawa an zuba magani...., kuma ban san yaya aka yi ba dai shi ya gani, ban sanshi ba, ban taba haduwa da shi ba ama ya biyo bayan saurayin nawa har mota sai da ya shiga ya fido shi ya tambaye shi abincin dayan na waye?, shi kuwa irin da abin garajen nan yace bai sani ba waye shi? ya sake tambayarsa a kausashe , ke dai in kare maki zance a ranar da ya ce min sai in gyara zama dan an zuba magani a abincina, Ni shi nake kallo, jin furucin nan na fito hankali tashe na so yiwa saurayin nan nawa rashin kunya shima ya so ya nuna min sakaran halin namijin dake fada da mata, Atu ban shirya ba ya daukeni cimak ya maida bayansa ya ci uwar saurayin nan, da kyar aka raba su, sannan ya rufeni da fada harda kashedin ya gane fuskata na yarda ya kuma gannina da wani dan iskan zan fada...."
Ta yi murmushi ta ci gaba da fadin" Babu wata alaƙa da ta shiga tsakaninmu ta wani alamu, tun daga ranar ban kuma ganninsa Bama sai ranar aurenki, sarai na gane shi, sai dai irin yadda yake ta hade rai da furucinsa kamar mun zo neman wani abu sai na share shi na dauke kaina, ko da muka kai ki mun hadu da shi a hanya ina dawowa, sai kuma ranar da na je restaurant na ganshi , kuma a ranar ne muka yi adaidaita daya muka yi accident. ......, a kaf maganar nan da nake yi maki maganar da ta hadani da shi bata fi sau hudu ba, na farkon nan da ya min, na biyu a cikin adaidaita da ya nemi na bari a kai shi wajen Mah, na uku fadan da ya min dan na fita da dare wajen ABDALLAH, sai ranar da yace kunshina ya yi kyau!"
Ta karashe tana dantse lebenta, Atu kuwa zuwa lokacin kirjinta har sama sama yake yi saboda yarin tashin hankalin da take gannin RAUDA ta gama sakata
Murya da gagawa ta ce" Kina nufin, da gaske MALIK din ne ko dai ba shi ba?"
RAUDA ya kalli yannayinta, kamar firar na neman rikita mata lissafi, kamar kuma wace take iya kai mata naushi, dan haka ta sake gyara zamanta tana kallonta ta ce" Shine mana, ke sunansa YUSUF ne"
"Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une!" Atu ta fada da karfi har sai da RAUDA ta zabura ta mike tana duba bayanta domin yadda ta yin walahi ta zata wani abu ta ganni a bayanta
Rai bace Atu ta ce" Ke zauna dan ubanki! zauna nace, yanzu Ni kika yiwa wannan danyen aikin? Ni kika watsa haka? innalilahi yanzu jira kike yi bayan yaba maki kunshi da ya yi ya ce wance ina son ki? an gaya maki manyan nan haka suke? RAUDA Sarki ne fa, kuma tun kafin nadin sarautarsa mahaukacin mai kudi ne, wanda yake tafe ko a cikin abokansa cikin izarsa, ke kin ji in Alhaji na maganarsa irin yadda yake fadi? shine kike jira yace maki me bayan abinda ya nuna maki a aikace?"
RAUDA ta ja tsaki , zuciyarta na tafasa tana jin kai ita fa sarai tana iya murje komaima ta yi kamar bata taɓa Sanni ba a kan shirme, itama a dan zazafen ta ce" Sarki? sarki kika ce? ohk...., ya yi, ya je ya yiwa wasu sarautar ba Ni ba, ke kina so , so kike ki ce min, saboda tsabar balaki da wulakantar da kai, Ni mace nice zan hankalta da ana so na har na lalata auren wanda ke son nawa fisabililahi na zabe shi? Allah ya kiyaye, walahi ba zan taba yarda da wannan abin ba! ke bari ki ji, koda abinda kike tunanin haka ne wato yana so na, na ƙaryata, dan kuwa so din in har da gaske ya kama mutun shi yake salamawa ya sama ma kansa mafita ba wai Ni a yi tunanin Ni ce zan samawa kaina ba, i love Abdallah, Ni na san da ina son ABDALLAH, kuma zan iya rayuwar aure da shi har karshen rayuwata, ki Kadara wannan abin da kika karanta shirme ne kawai, kin gama bari ki gani....na goge, haka kuma na goge shi daga rayuwata, wace ya aura kuwa ya je ya zauna da abinsa shi ya gano!"
Daga nan ta yarda wayar a nan ta fice ta nufi bayin Mah dake cikin dakinta na barci ta bude ta shiga da sauri
tana rufe bayin ta saka hannayenta bibiyu ta rike kanta, bugawar da kirjinta ke yi na neman fin karfin ta
a hankali ta silale jikin kofar ta sake saka kanta tsakanin cinyoyinta ta fashe da wani irin kuka mai nishin nan, a ranta tana ta astagafari da ambaton sunnan Allah, ayanawa take yi' Allah kai ne Allah, Allah ka cire min abinda ke raina ya zamo kamar bai taba wanzuwa ba a ruhuni na, ya Ubangijin samai da kasai ka saka min soyayar mijina fiye da ta kowa a zuciyata ka bani ikon yi masa biyayya da dukkan lokacina a kansa, ya Allah ka ji kaina idan har ba zan iya manta abinda ke raina ba ka amshi raina na zo gareka tun kafin na kona kaina, ina tawasali da sunnayenka tsarkaka ka tsare Ni da fadawa halaka a kan makauniyar soyaya.....'
A falo kuwa, jiki tamkar an zarre mata laka ta zauna kasa tana sauke ajiyar zuciya, a bayane, sai dai muryarta kasa kasa sosai ta ce" RAUDANA, ta wani fannin zan fi farin cikin ace kin watsar din, domin matar da ake maimaita matarsa ce ba zan taba so wani abu ya hadaki da ita ba a rayuwa, dan kuwa kudin iyayenta sun bata dama sosai na daukan duniya a matabata, na ga status din matar ƴaƴanta tana dora yau ne daurin aurenta, buri ya cika yau ta auri sarki? eh lalle abubuwa zasu karu har su wuce da, sam halayarku ba iri daya bace, ita ko gaisawa bata yi da talaka, bata hulda da mace mai muni ko baka, domin ko mai aikinta fara ce kyakkyawa, yarinyar nan ban san a inda ya ganota ba, ama idan ana kiran mutun dan Adam da AZAL tabas itace, tana da raini fiye da tunanin mutun, kuma idan tana waje ta tsani ace wani dan Adam ya fita a wajen, sai ta yi yadda ta yi ya zamo itace sama da uban kowa....., uhum Ni kam ina tausaya masa dan ko Tata mahaifiyar ita ke yi mata biyayya bale uwar miji, da wahala ta girmama mahaifiyarsa....." ( kai, 🤔, Mah,? lalle da an yi kulli kulin kubura da yar mutane muna gefe muna shan lipton)
....................................................
"HEY" SHAHEED ya fada a karro na uku kennan, tunda suka juyo suka dawo falonsa suka zauna , yana zaune ne ama tamkar gunki, ga fira a bakin SHAHEED din a yau, ama kuma abokin yin kamar baya cikin duniyar masu rai
"Lafiyarka kuwa?" SHAHEED ya fada , fuskarsa na nuna alamun damuwa
Rawanin dake kansa ya shiga kuncewa, har ya warware shi ya sauke hular dake ciki hakan ya ba gashinsa damar bayana , ya cire agogon dake hannunsa hadi da kai hannayensa wajen goshinsa ya ringa murzawa, kirjinsa na yi masa wani irin zafi, kwakwaluwarsa na tafasa, hankalinsa gaba daya tamkar ba nasa ba, duniyar kaf ta yi masa kunci fiye da tunanin bawa
A hankali ya sake kallon SHAHEED, muryarsa cen ciki ya furta" Ta yarda ta aure shi, SHAHEED ta yarda ta aure shi.........."
Daga haka ya dauko wayarsa, kirar samsung wace ake ninkata ya bude sai ga hoton kunshi a hannun mace ya haska saman screen din, a hankali ya shiga wajen msg ya bude ya mikawa SHAHEED sannan ya mike tsaye ya saka hannayensa cikin aljihun wandonsa ya ringa kai kawo yana ta faman kiran sunnan Allah, dan ya sani shi kadai ya isa ya sanyayar masa da zuciya a irin halin da yake cikin nan
SHAHEED ya karanta ya kai sau goma, du idan ya karanta kuma sai ya dago ya dubi YUSUF, sai ya sake karantarwar
"ya Salam, Dama a gidan nan take? dama a kusa da kai take?" SHAHEED ya tambaya, hakan ya sa YUSUF dakatawa ya dago idannuwansa ya zuba masa, lebensa kuwa ya yi Jajajir ya tasa tsabar yadda yake dantse shi
"Na san me zaka ce......, ya yaya ina ji ina gani ko?" YUSUF ya fada yana kallonsa, dan ya sani sarai SHAHEED a kan magana irin wannan kulun fada masa yake yi ya daina kiran soyaya Azal, ya gwada ya gani babu abinda ya kai soyaya dadi a gidan duniya, ama sai ya yi murmushi yace baya cikin wannan gangancin
"Koda ta tare sai ya saketa, ina zuwa!" SHAHEED ya fada a zafafe ya mike da nufin fita
YUSUF ya yi gaggawar riko alkyabarsa ya dawo da shi yana dubansa a tausashe ya ce" A'a, Please"
SHAHEED rai bace yace" Ka san kuwa a wani irin hali kake kokarin saka kanka? ka san irin girman rikicin da kake kokarin nuna zaka iya yi? waye kake son birgewa da nuna wannan halin? mace ce fa, ina mai tabbatar maka koda mutuwa zata yi tana iya rike damuwarta a kanka, ya Salam,, a kan me zaka bari ta aure shi?"
"Dan tana son shi!" YUSUF ya fada da muryarsa da take nuna yana daf da gazawa
sakin alkyabar SHAHEED ya yi ya juya ya nufi cikin bedroom dinsa ya bude wajen ajiyar magungunnansa ya ciro na ciwon kai ya bude frij ya ciro karamin ruwa ya bale ya hadiyi maganin sannan ya juyo yana kallon SHAHEED da ya harde hannayensa yana kallonsa ya ce" Idan ka ji ana cewa macen da ba za'a iya aure ba, gaba daya itace, dan da ka ganta a nan a kan kudi ko? Sai ta shaki wuyanka, dambe kuwa babu kalar wanda bata yi ba na gani, wanda na yi niya ta ga na ga tana yi nake bari ta gani a lokacin da take yi ama in fada maka ko a kwalar rigarta, kai dai halaya sak na rashin jin magana....ama ban taba jin haushinta ba dan na san dalilin da yasa take cikin wannan halin, SHAHEED tana da yaro , hakan bai taba damuna ba, da ido take min tatas sai dai ka ji ina sauke ajiyar zuciya....., kamaninta yadda ka san flower........" ya karashe yana sauke dan murmushi hadi da tatare girar goshinsa
Sai kuma ya gimtse lokaci guda ya ce" Na zata, zata ture, dan kofa saura minti É—aya a Daura mata shi zan katse, hakan ya sa wayar nan bata fita a hannuna ba sai yanzu da na baka...., ka ga shiru ba msg dinta ba kiranta, da ace bata sonsa koda kadan ne, da ta lalata wannan aure nasu..... shi yasa nace ba zan taba yafe mata ba, ta idasa sakani yarda cewa *SOYAYA ITACE AZAL DINA!*"
SHAHEED kasa furta komai ya yi, yana kallonsa ya cire rigar dake jikinsa ya nufi bed dinsa, a takaice ya ce" Please, ka hanna kowa zuwa inda nake, nd wace Hajia ta aura min ta sauka bangaren Mah idan na shirya raba bed dina ta zo!"
Daga nan ya rintse idannuwansa, ya ci gaba da juyawa a saman gadon nan
abu daya yake son ganni a gabansa a yanzu, itace, ya dubeta ido cikin ido yace nawa take so da har ta iya zabar kudaden cen a kansa? ta san me yake iya bata ko ya mallaka mata a duniya ne? ta san shi me ya mallaka a duniya ne?, yana so ace ya ganta ido cikin ido ta fada masa shi zata sake ba wani jikinta ba shi ba?, zata iya zuwa ta ga wani ba shi ba? ita ai ba yarinya bace, ba kuma makauniya bace, ya tabata a irin yadda ya karanceta ta jima da gane abinda yake ransa, yarda ne bata yi ba bayan shi ya yarda da wanda yake ganni a nata idannuwan? wayo Allah, ya Allah haka azabtar nan take? ashe zafi ne da ita mai karfin gaske? "RAUDA, BA ZAN TABA YAFE MAKI BA!" yake fada muryarsa a shake, jikinsa kuwa ya kama hautsinew da zafin zazabi!
SHAHEED , duk murnar da yake na auren abokinsa sai abin ya sare masa, shi da ace zai yarda, walahi a yanzu yanzu sai ta amsa sunnan matarsa, sai dai irin yadda ya kulaceta abin ya bashi tsoro ainun, kuma a yanzu ba zai taba yarda ace da shi laifinsa bane, Bama zai bada damar nan ba in dai YUSUF ne, ba zai yarda cewar shine ya dace ya kwato ta ta yadda ita da kanta ba zata ankara da ta shiga Wajen da fitarta zai yi wuya ba!, sai gashi wani ya riketa a lokacin da bai shirya rabuwa da ita ba
Hucin numfashi ya fitar da wayarsa ya yiwa Sarkin bulala texte
minti kadan sai gashi ya shigo ya duka kansa a kasa bayan ya kawo gaisuwa wajen aminin uban gidansa sannan ya yi shiru yana jiran sakon mai Damagaran
Sai da ya gama daidaita abinda zai isar ya ce"
39
Azl 40
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin