Showing 48001 words to 51000 words out of 188741 words
bai kamaka ba, mahaifinka ya mike ya fansheka, kai har kana da bakin ce min ya hau sarauta? Mahaifinka ne zaka bari ya hau sarautar? Ciwonsa ba na sarauta bane, domin abu kankani na saka shi fita a hayacinsa!, idan ya hau na dan lokaci ne, kuma babu wanda ya isa ya saka Ni ce za tsarin tarihin kasata, Nana ki fita a gaban idannuwana, MALIK ka je kaima ka je kawai!" Hajia ta fada muryarta na cinkushewa kuka na neman barkewa daga bakinta hankalinta gaba daya a tashe
Rai bace YUSUF ya cika hannunta ya mike har wayarsa kirar iphone ta fadi kasa ta yi ratsa ratsa ƙafarsa ya dora Mata sakamakon yada jikinsa ke wani irin abu na bacin rai, sannan ya juya har zai fito ya juyo yana kallon Nana wace ta mike din itama rai bace ya ce"
Azal17
Rai bace ya ce" Ki yi gangami, ki tara majalisar dokokin kasar nan, idan mun dawo daga rakiyar Aba a yi zabe, shin zasu yarda su dora mashayi, mazinaci, kuma wanda bashi da aure saman kujerar mulkin garin nan? Ko zasu zabi naggartace malami, mai mata da ya'ya?, kar ki yarda damar nan ta kubuce maki, domin idan kika yarda suka nada min sarautar nan sai na adabi rayuwarki a kan addabar tawa rayuwar da kika yi Nana!"
Yana gama fada ya yi waje ya koma bangaren mahaifinsa ya shige wanka yana ta ambaton sunnayen Allah, fiye da yadda ya saba ambata a da, dan tunda yake bai taba doguwar addu'a irin ta yau ba, burinsa yana fitowa ya ga mahaifinsa ya farka, burinsa yana fitowa ya ga komai ya zama tamkar mummunan mafarki a wajensa, dan ba zai taba iya misalta wannan mummunan labarin mai dauke da *AZAL* tiryan a kansa ba, ina shi ina sarauta? Ina shi ina sarauta jama'a?
Yana fitowa daga wankan ya saka tufafi a cikin tufafin mahaifinsa, yadi ne ya dauko marar nauyi ya suturta jikinsa, kuma yadin ya dauki jikinsa sosai , rigar cema ta so yi masa kadan wajen kirji da danatsunnan hannayen, sai dai kasancewar ya san a yanzu babu wanda zai yarda ya fita a dole ya saka , a ransa yana adu'ar a gama dukkan abinda za'a yi ya je ya kai mahaifiyarsa asibiti sannan ya wankawa wannan marar kunyar marin da zai saka ta san waye shi da har zata ja masa kashedi a kan Mahaifiyarsa dan raini.....wato abubuwa sun masa yawa ne ta yadda ya kasa tantance me zai yiwa fushi, sai yake kame kame a cikin zuciyarsa kala kala
Yana fitowa ya sake dukawa daf da gadon mahaifinsa ya rike hannayensa, a hankali ya dora gefen fuskarsa a tafin hannunsa na dama, yana so ya yi magana ama abin ya ci karfinsa zuciyarsa ta gaza bashi damar amayar da abinda ke ransa, sai kawai ya mike ya daidaita kwonciyar mahaifin nasa ga nufi waje yana ji zuciyarsa na sake tsintsinkewa ya nufi ayarin taron mutanen dake zaune a manya manyan shinfidu na alfarma kowa ka gani yana addu'a ne, ana zaune ga dukkan alamu shi din kawai ake jira domin a lokacin da ya karaso tun kafin ya je wajen da zai zauna manya manyan malaman garin da limamai suka mike sai sarakunan, hakan ya sa gaba daya jama'ar gari suka mike ya zamto kusan hankalin kowa a kansa da tarin idannuwa
Dakatawa ya yi yana bin mutane da kallo, sai kuma ya sada kansa yana jin bayanin limamin baban masallacin masarautar da kuma masallacin idi
Ajiyar zuciya ya sauke ya gyada kai ya kai dubansa wajen RISLAN da ido ya masa alamun ya karaso mana, hakan ya sa RISLAN karasowa daf da shi suka fara yin gaba dan zuwa dakin da aka killace gawar aka gama kimtsata
Su ne suka fara dauka daga gaba, sai mutane hudu wasu daga tsakiya biyu daga karshe aka fitar da ita aka ajiye aka salaceta sannan aka nufi makabarta aka binne aka juyo
Tunda aka wakilce shi wanda ya fara shiga kabarin mamacin yake jin tamkar hawan jinni na daf da buge shi, dan ya san me hakan yake nufi, ama kuma tarin abinda ke kai kawo a zuciyarsa a yau din ya fi komai karfi, dan duk yadda ya so hanna hawayensa zuba sai da ya zubar a lokacin da ya ga yau an turbune baba baba a karkashin kasa shikenan an kare, duk sarautar shi, duk arzikinsa, komai da komai ya tsaya a nan an kare, shikenan a yanzu mamacin sai shi sai halinsa, ko me ya aikata a duniya daga yanzu zai fara girba, ba zancen sai kiyama ya tsaya shi tasa kiyamar ta tsaya kennan, hakan ya sake rikita tunaninsa bale da ya rintse ido ya hango shi din waye sai ya ji inama zai ga mamansa a yanzu? Babu abinda zai hanna shi dukawa ya fashe mata da kuka da fadin yaya zai yi da ransa?
Tamkar a mafarki suka karasa fada, kamar a mafarki yake kallon yadda aka je dakin mahaifinsa da manyan sarakuna da likitan mahaifinsa wanda ya gabatar da jiga jigan dalilan da mahaifinsa ba zai iya rike sarauta ba, wace manyan garin da sarakuna makotan garin suka yi amana da bayanin likitan da kuma abinda idannuwansu suka gane masu mahaifinsa a kwonce tamkar ba rai yana amsar ƙarin ruwa kan wani, a irin lokacin ne suka tisa keyarsa, jiri na dibansa, ya saka hannunsa da sauri ya kama kofar baban falon mahaifinsa idannuwansa a kan matan mahaifinsa su dinma a tsaitsaye suke labarin zukatansu a bayane a saman fuskar su, tashin hankalinsu da damuwarsu ya kasa boyuwa a saman fuskokinsu sunna yiwa abin kallon wani iri, sai dai basu fida rai ba, dan tunda aka sanar cewa kafin a tabatar da ko waye sarki sai an yi zaman da akan yi idan abin ya zo da rikici, sun tabata da wahala a dora YUSUF sarki a yau
Cikin kamilaliyar murya bayan an yiwa dogarai dake rakadi alamun su fice sarki SHAHEED Dan Abubakar ya karaso daf da YUSUF dake tsaye ya saka kwayar idannuwansa mai dauke da abin kwali cikin nasa, dukda rawanin dake jikinsa da kuma shiga irin ta sarakai bai hanna shi sassauta rawaninsa , dudka tsaurinsa da rikon da yake yiwa rawani matsayin abin da ya fi komai kusanci da shi a suturar jiki sai da ya sassauta rufewar fuskarsa har fuskar ta bayyana a idannuwan YUSUF, fuskar da dama ba bakuwar Yusuf bace domin kyar ta san kyar ne, sukan hadu a filin basket ball a matsayin freind su buga kwalo , shi SHAHEED fuska a bayane ama babu wanda ya san waye shi sai biyu ko ukun mutanen wajen, shi kuwa YUSUF a matsayinsa da tasa darajar wace take hanna shi walawa dan ya tsani ya fita a ringa sada masan nan baya so
A tausashensa da yannayin isar sa ya ce" Faduwa zaka yi ne MALIK?"
YUSUF ya zuba masa ido, yana ji tamkar ya budi baki a gaban kowa yace SHAHEED bana son rainin hankali, ko ya rike shi yace ka rufa min asiri ka gudu da Ni? Ama ba dama dan kowa idannuwansa a kansa ne ciki harda Sarkin agadaz wanda ya yiwa likitan abu alamun kar ya fita dan a yau ko a sume ne sai sun tabbatar da wanda ya cencenci mulkin talakawa a kujerar da ta dace da shi, zasu ga su da wadinncen masu akidar waye asalin mai akida , sarki ko masu rike da mulki!
A hankali ya kai tatausan hannunsa wajen goshinsa dake yamutsa masa ya dan murza, hakan ya sa likitan matsowa da girmamawa ya ce" Ko zaka zauna na auna jikinka sir?"
Sosai ya so yin rigiza ya zube a wajen nan, koda zai dada keyarsa da kasa ne dan ya zamo ya samu summa mai kyau wace zata dan ja shi har a nada sarki RISLAN, sai kunnayensa suka jiyo masa magana ta aboki kuma tsara a wajen mahaifinsa wato Sarkin agadaz a tausashe ya ce" Ba maganar zama, in sha Allah koda a summe ne sai mun tabatar da shi a dakin taron cen, daga nan kuma sai mu tsaya da jajircewa da addu'a har Allah ya tabatar da shi a kan kujerar da take tasa, in yaso sai mu farfaɗo shi ya amshi abinda yake nasa dan aiki ne baba Malik"
Hankalinsa ya dugunzuma ya tashi, ama kuma sai ya rike kansa da kyau yana binsu da kallo har aka bar shi daga shi sai SHAHEED
Da murmushi SHAHEED ya mika hannunsa ya rike nasa na dama , da dayan hannun kuwa ya mayar da rawaninsa ya rufe sosai fuskarsa sannan ya masa alamun su je
Bashi da yadda zai yi sai daga kafa da bin bayansa, domin ya sani dole zai je dakin cen, sai dai abinda basu sani ba shi din da kansa zai zabi RISLAN ne a matsayin ja gabar talakawan Tsatsunburum
Sunna fitowa aka dora masa alkyaba fara dal mai tsayin gaske, bai ankara da sauran rigimar dake gabansa ba ya ga yamadidin mutane a kansa, duk kuwa da rasuwar da aka yi bai hanna busa ba, wato daya daga cikin abinda ya fi kona masa rai, dan ba zai taba mantawa a lokacin da aka naɗa baba baba sarauta an dawo daga binnar mahaifinsa aka saka masa busa, hakan ya sa ya fashe da kuka, yana yi tun karfinsa ama sai da aka naɗa shi, yana kuka Hajia na hawaye Honorable na taya dan uwansa kuka
A lokacin da suka nufi baban dakin taro a lokacin matar Honorable mai dakin tsakiya ta yanke jiki ta fadi, sumamiya domin dif ba numfashi a tare da ita
A rikice ƴaƴanta da abokiyar zamanta wace ta yi iya yinta ita din bata suman ba suka yi kanta , ƴaƴanta na kuka da kiran sunanta su hudu, yan mata uku namiji guda karaminsu , sai ya'yan uwar gidan da ita uwar gidan sunna kiran sunnanta da kokarin bata taimako, da kyar salima ta tuna da waya ta je da gudu ta dauka ta shiga kiran numbar likitar su mace wace ke duba su ta sanar mata ba lafiya a gidan sannan ta dawo ta samu itama Tata mahaifiyar kokari ne kawai take yi dan wani irin gumi ke karyo mata da tashin hankalin da ƙarara yake bayane a fuskarta, ko a jiya bata rintsa ba, a lokacin da Salimar ta tashi tana sallar dare ta ga mahaifiyar Tata zaune ta zubawa waje daya ido, da ta tambayeta sai tace mata rasuwar nan ce ta girgizata, shi yasa ta zauna sosai ta bata hakuri da sake rarashinta kafin ta je saman salayarta ta shiga gabatar da nafilfilun da suka gama zame mata jiki, dan salima babbar makaranciyar Alkur'ani ce, tana matukar ba musulunci mahimmanci, tana karatun lauya ne, wadda a yanzu take mataki na karshe, kuma mai biya mata yayanta ne, shi yasa a kulun take kokarin dan dawo da mahaifiyarta kan hanya a kan lamarin yayansu, duda mahaifiyarta bata fitowa fili ta nuna abinda yake ranta, ama ai su ko da ido ta yi magana sun san abinda yake zuciyarta shi yasa take sakata a addu'a tana nema mata sauƙin abin a wajen Allah, dan ta san ba komai ke rikitata ba sai tunanin yau ko mulki ya dawo hannunsu ba a dakinsu yake ba, dan da wahala a tsallake manya a diro kan kananun gidan, domin kuwa kannensu maza kannanu ne sosai, in dai da ran Bah karami kamar yadda suke masa kiranye, dan sunna kiran mahaifinsu Bah, sai su ce da yayansu baba Bah karfi da yaji Salimar ce ta sa sauran ma suke kiransa haka koda iyayensu basa so, ita a ganninta idan Bah karami ya samu sarauta su ne a cikin gata ba kowa ba, a yanzuma likita kawai zata zo ta duba iyayensu itama ta je dakin taro, fatanta Allah ya sa ta zamo cikin wa'inda zasu zabe shi matsayin uban talakawa, dan ba gudu ba ja da baya a san shine daidai da mulkin zamaninsu, halayyarsa wa'inda yake aikatawa na rashin dadi kuwa ita ta san in sha Allah zai daina, zai daina ne zai kuma nemi yafiyar Ubangijinsa a lokacin da lokaci bai kure masa ba, dan a kulun cikin adu'o'in wa'inda yake kyautamawa yake
Azal 18
"Ka zauna aka ce mana YUSUF" shine Muryar wace ta fi kowa bashi mamaki da ya gani a wannan waje, wace ke cikin tarin taron duk wani wanda ya isa ya saka shi ko ya hanna shi, ciki harda yayunta maza da mata, wa'inda rabonsa da ya gansu da idannuwansa har ya manta, wasu lokutan sukan wucewa ta kusan junna a mota ama baya taɓa barin shi dai su gane shi, kuma rabonsa da ya saidawa masarautarsu mota tun wani taro da suka yi suka daga hankalin mahaifiyarsa ta yi kuka ya kurce su a tsarin bangon litafin rayuwarsa, sai gasu summa a tsaye kamar yadda duk wani mahaluki ke tsaye ana jira sai ya zauna kafin su zauna, zaman da aka ajiye kujera daya tak a tsakiyar filin ake jira ya zauna masu ja in ja din taron su yi, wato MAH
A raunane ya sake duban Mah, a idannuwansa yana yi mata kallon kin san me suke nufi? Mah kin san ba zan iya ba, ama bakinsa ya kasa budewa bale har ya furta wannan kalamai, hasali ma shi a tunaninsa yaya aka yi ta mike ta iya fitowa? Wa ya fitar da ita? Yaya aka yi suka yarda aka fitar masa da uwa cikin zafin ranar nan? Sai kuma lokaci daya ya ba kansa amsa ta hanyar kai dubansa kan Hajia wace ke zaune cikin motar turawa ta asibiti tana kallon nasa itama
Gwauron numfashi ya sauke ya shiga takawa a hankali, cike da sabon abinda ya ratsa jikinsa da karfin ikon izar da Allah ke wanzarwa a duk jinnin jinnin bale kankat ja gabar
A hankali ya kai zaune saman kujerar ya lumshe idannuwansa da kansa dake sarawa kunnayensa na jin umarnin da aka bada daga Sarkin gida cewar kowa ya zauna
Baban wanda ke kare yancin talakawan a rukunin mulki ta gwamnati da yawun gwamna da duk wani mai fada a ji ne ya mike ya karaso ya mika gaisuwarsa wa kowa sannan ya budi baki cike da girmamawa da jajanta baban rashin da aka yi ya dora da fadin " Sako ya same mu a jiya da dare, a lokacin har mun yi shirin zuwa wajen jana'iza da sannin wanda zai maye gurbin mamacin, sako ya same mu cewar ba shi zai hau ba yaronsa zai hau bisa tabbacin da likitoci uku suka bamu cewar eh lalle sarauta ba tashi bace dan rashin lafiyarsa ba wace zai iya jure hawa da sauka bane na cece ku ce da firgicin sarauta na yau da kullum ina fata kowa ya gamsu da bayanina kuma ya yarda da maganar ? Idan da wanda yake da ja ko tunanin akoy wani lauje cikin nadi kan wannan bayani ya yi mana bayani ta yadda zamu katse komai kafin a yi nisa da maganar"
Shiru ya yi sannan ya ringa bin kowa da kallo, har kusan minti biyar, sai ya dora da fadi " Tabatuwar zancen daga gare ku zai saka Ni ajiye jayayata a filin da ya dace na ja "
"An sanar mana cewa ganganci zai saka a ba wanda bai cencenci rikon mulki ba, an ce mana ana so a ba mashayi mulki? Shaye shaye fa ake nufi? Ana nufin shan giya wace Allah ya haramta shanta? Dan kuwa duk wanda ya zamo cikin maye zai iya aikata aikin da bai sani ba , an hanne mu kusantar kanmu da sha, dan sha na saka mu aikata zunubi mafi girman da zamu yi dana sani a rayuwa har mu koma ga ubangijinmu, an tabatar mana rikicin na son rai ne? An ce bayan akoy wanda ya cencenci hawa mulki ake so a ba YUSUF BELLO?, a yau muna tsaye da karfinmu dan dakatar da wannan magana, mulki zai hau wajen da ya dace ne domin rikon talaka ake magana ba rayuwar bariki ba, kamar yadda muka sani talaka rikonsa sai mai Addini, sai mai jin tsoron Allah, wanda zai kiyaye hukuncin ubangiji ta yadda zai ji kan talaka, ina da ja da wannan magana!"
Yana kaiwa karshen abinda ya kawo shi ya koma kujerarsa ya zauna, a matsayinsa na wanda ya isa ya fadi abinda ya fadan shi da kansa ya fada zuciyarsa na rawa, sai dai ya zama wajibi a bi komai yadda ya dace , a ba talaka hakinsa dan ba zasu taba bari a dora wanda bai cencenci hawa mulki ba!
Tunda mutumen nan ya fara magana, maganar dadi take yi masa har aka zo abinda zai kira da cin zarafi da munanawa da kuma wulakantarwa a gare shi, a irin wannan lokacin da ake zaginsa da abinda Bama shine aikin nasa ba, dan kuwa aikinsa shi dai a saninsa taba mace ne, ama baya sha, sai dai ba kowa ya san haka ba, a hankali ya maida kansa ya sada dan ba zai iya duban idannuwan mahaifiyarsa a daidai wannan yannayin ba, shin me zata ji? Yaya zata ji? Ga yan uwanta dake zaginta da abin kulun, shin yaya zata iya jurewa? Bai taba jin takaicin munanan halaya irin na yau ba, dama ta sha fada masa shi mugun aiki ana kiyaye shi, dan idan aka tashi kalubalantarka ba'a ware cewar ka yi kaza baka yi kaza ba, za'a hade jiji da jan kanwa ne a yi maka tawa tsine a duniya, gashi dai ta sake shi
"Asalamu alaikum wa rahamatulah, sunana Jabiru jikan Baba sarki, kwarai nima ina ja da maganar dora mutumen da bashi da iyali wanda ake radi radin halayyarsa mararsa dadin da bai cencenci rikon daraja irin ta sarauta ba, ba zamu iya bashi sarauta ba dan bai dace ya zama sarki ba, a matsayina na dan uwan mahaifinsa wato cousint din Honorable Bello ina da ja a kan wannan magana!" Mutanen da ake yiwa kallon idan sarauta ta kubuce daga hannun famillyn Honorable hannunsu ne zata shiga kennan, wannan shine wanda idan ba YUSUF ba Honorable a wannan karni zai hau karagar mulkin da take ta jinni