Showing 63001 words to 66000 words out of 188741 words
ko dayan farkon nan๐๐ผ (magnifique)
Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account ๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ (da wa kika ja Madame?)
Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba๐๐๐ sai kun zo
Cikin hukuncin ubangiji a haka cikin sama da kasa da fari da baki har aka wayi gari aka yi adu'ar sati ta mamacin, wace a tsakanin satin nan babu abinda Mah da YUSUF basu gani ba na mamaki daga mutane daban daban-daban na waje da na cikin gida , abubuwa na girmamawar da a da basu samu ba, zumuncin da a da Mah bata samu ba ta gan shi, dan har aka yi kwana bakwai din nan ras da rasuwar nan ya'yan yan uwanta na nan sunna kwana a dakinta su tashi a yi dukkan ayuka da su, kuma da zarar karfe goma ta yi a fara ba mutane damar shigowa yan uwanta tasu zo su wuni da ita sai da magariba suke juyawa, tun tana dari dari har yanzun ta saba gannin wulagawarsu ta kuma gano eh da gaske suke yi yanzu suke zumunci da ita, sunna nufin yanzu take mutun, itama sai ta ari yannayin wasan su, a ranta ta yafe masu ana zumuncin da ake son yi na nesa da nesa da dariyar hakorin,ama bata jin daga nan zasu samu yadda suke so daga gare ta, domin sunna sun harda su shawara su ringa yi tare da sauransun nan, hakan take gannin idan har ta yarda ta yaudari kanta da kanta kuma ta zama sakarya kennan!
Yau tunda sassafe yan matan nan suka samu matsala sakamakon abinda daya ta dora a Tiktok saman sunnanta na Tiktok, wato Mrs mai martaba.....hakan ya sa Musulima yiwa abin dariya har ta kasa rikewa sai da ta fadi sunnan a lokacin da ta fito daga wanka daure da tawul rai bace ta ce" Iko sai Allah, wai duniya ana kani'iba in ji bahaushe, in ba cune cunen kaza ba me ya kai bakinta cikin zazafar miya?, ana gannin abubuwa a duniya masu ban mamaki, su matan mai martaba manya!"
Sosai abin ya yiwa Akilah ciwo a zuciya, har ta kasa hakuri ta dubi Musulima ta ce" Da kyau tunda na iya na iya bambance abin kunya da wanda ba na kunya ba, kuma tunda lamarin nan halal ne tabatuwarsa alkhairi ne ina da yakini, sai dai kuma in wace ta fi kowa kiyaye Sannin mai kudi ne ta dawo son hada zuri'a da mai mulki dan a yanzu ta gane dan kana da kudi baka da mulki shirme ne ya sa har take iya yafe zagin da ta yi a baya na nasaba to sai ta auna shirinta tsaf mu gani, domin na fito a shirye jinnin dake yawo a jikina kuwa ba na abu ya BARNI bane sai dai na bar shi, dan ko wane ka dauka an dauko, kuma Ubangiji ya kawata halita!"
Hindatu ta yi mamakin su gaba dayansu, sai a nan ta yarda da furucin mahaifiyar kan kasantuwarsu a gidan nan, tana kallon su suka yiwa junna tas ta hanyar gorace goracen abubuwan da iyayensu suka sani a tsakaninsu, sai dai basu daki junna ba, dan karrara Mah ta nuna masu gaba da suke bata so, ba zata iya dauka ba bale a kai ga dukan junna? Lalle ta yarda sunna son abinda take so, hakan ya sa ta sake zage damtse dan ita ta fi ganewa ta bi ta kasa ko zata samu biyan bukata!
Haka aka yi wunin nan, yan matan kowace na falon da ta fi so tana chating dinta Salima na karatu a dakin kayan karatunsu Rauda kuwa tana zaune da wayarta ta dauko layinta wanda kowa yake da numbarta ciki harda aminiyarta Bara'atu ta saka layin tana murmushi a ranta tana ayana' ta yiwu Bara'atu sai ta min gaba, na tabata ta neme Ni, ki yi hakuri kawata, ban kashe wayata dan kar na yi zumunci da ke ba, na yi haka ne dan na baki damar fuskantar gidanki da mijinki a tsanake ta yadda ko menene zaki fi fahimtar abinki da kanki, dan na san halinki kin ga damar da ya fita ki kirayeni mu dasa fira har ki manta da girkinsa, gashi magidanci kike aure ba saurayi ba bale nace ya saba, a hakan tsaf yana iya fara jin haushinki balle idan matarsa na cika masa kullu'
Har zata tura kiran numbar Bara'atu da layin, sai ta fasa ta ajiye ta shige wanka dan tana so ta je dakin Mah ta gaisheta rabonta da ita yau tunda safe da suka gaisa, ta yiwu ta sameta a dakinta ko kuma ta tafi wajen BAH?
Wanka ta tsalo ta fito daure da tawul ta dauki pant baki ta saka da riga mai siraran hannaye doguwa irin mai dan lafewa a jiki din nan, rigunnan da Mah ta bata ne a cikin akwati wa'inda ake daura masu lafaya masu laushi ne, ita sai take saka su ta dora masu zumbulelen hijab, takan jita sakayau ba wani damuwa dan harda tsaga garesu wace ke hanna rigar hardeta
A nutse ta dauki turarenta mai sunnan bonbon mai blue din gidan nan mai sansanyan kanshi da dadi ta shiga fesawa a jikinta tana karawa tana dan murmushi dan tana son kanshi a rayuwarta sosai sannan ta dauki hijab mai ruwan blue mai duhu sosai ta zumbula ta fitar da hannayenta ta hannayen ta saka bak'ar Safa dinta mai kwaliyar nan wace ke nuni kamar ka yi kunshi sannan ta juya hankali kwonce ta dauki wayar ta ringa gannin Msg na shigowa ta whatsup din da ta dora layin ta yi murmushi dan layinta ne da aka fi sanninta da shi, dama ta san sai ta tarda tarin msg a ciki, ta sauke layin da suke waya da Mutumen ta dan dazu yace yau zai taso daga maroko ya zo Nijar , tafiyar wuni daya da kwana ne a jirgi dan jirgin yawo ne dole ya shiga domin ya kasa samun special har gashi tana so ta sake daga hankalinta, shi kuwa abinda ya fi komai rikitashi a yanzu kennan
Layin Ameenu mai adaidaita ta shiga kira tana kokarin rufe dakin da ky, sai dai yana ta ringing ba'a dagawa hakan ya sa ta nace ita kuwa a dole sai da ya daga a lokacin tana tura kofar dakin Mah da salama ta shiga ta tarda dakin a tatare fess dan har kanshin turare yake fitarwa na wuta, domin yan matan Mah basa wasa da tsafta dan babu wace take son saboda kazanta ta rasa maki
A lokacin da Ameenu mai adaidaita ya daga wayar ya yi salama , Rauda ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Malan Ameenu ina ta kira shiru ko ka bar wayar a gida ka fita nema ne?"
"Raudar ce ke magana?" Radau Muryar Inna ta shiga kunnuwan Rauda hakan ya sa da dan zumudi ta ce" Lah , Ameenu wajen su inna ka zagaya? Dama kiran nan da na yi maka dan nace maka ne yau zan nemi alfarma wajen Mah a kai Ni na ga Abdul sai na taboka mu tafi, ashe ka rigayeni zuwa, dan Allah bani su , ta bani shi na ji rigimamena, na tabata yana nan yana mata rikicin a kai shi aunty"
Magana take yi da zumudi, ta zauna saman cafet hannayenta na dan shafa gefen fuskarta a hankali tana murmushi har ta ji salamar inna da Muryar innar wani iri, sai dai bata saka komai a ranta ba duba da yannayin girma da kuma rashin lafiya da mutun ke iya kuwa da shi, dan haka ta ce" Barka da yama Inna, ya gida yaya kwana biyu? Ina mutumen inna na kawo maki ban dawo ba ko?"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tana jin wani irin nauyi da tsoron abinda zata fada fiye da yadda ta sanarwa uwarsa kai tsaye ba wani kwane kwane, sai take jin kamar Rauda zata fi koya shiga tashin hankali idan ta ji abin nan, sai dai ba yadda zata yi dole zata sanar mata da fatan Allah ya sa hakan zai zamo sanadiyar maganin damuwar
A tausashe sosai inna ta ce" bari, bari y'ar nan wahali kin ganshi ya zo Malan Ameenu ya sameni bana nan, dan yanzun nan daga gidan mai anguwa na sake fitowa, yau din nan ruwa bai shiga cikina ba bale abinci, na rasa ta inda zan dafa matsalar ban bale har na ga mafitarta, na bayar a min rokon Allah nima ina ta yi, mijin rabona da shi tun jiya da na kai shi makaranta na dawo daukansa malan yace ai ya jima da fita shi ya zatama Ni din ce na je daukansa, y'ar nan na yi kuka na yi kuka na yi cigiya ban ganshi ba, yan anguwa sunna ta tayani dan ko yanzu da Ameenu ya zo mun leka Ni da innar baraka ne gidan mai anguwa dan tun jiyan muka je muka kai cigiya harda gidajen rediyo ama shiru kake ji ba'a da labarinsa ba'a ganshi ba"
A hankali RAUDA ta dakatar da murza gaban goshinta da take yi, muryarta na gaza fita, da kyar da dan karfi daidai lokacin da Mah suka nufo dakinta ita da MALIK, sanye cikin shigarsa ta sarauta, dan shigowarsa kennan saboda likitan da aka kawo daga kasar waje sun zo da likitoci biyu shine suke son takardun Bah da aka masa bincike na lafiyarsa kaf, takardun kuwa a wajen Mah suke a cikin akwatinta ta dakinta dan tunda ta zo idan aka bata ko menene basa takan zo nan ta adana gudun kar a batar a dakin nasa dukda ba kowa ke shiga ba sai ya su ya su, shine ta mike dan ta zo ta dauko ama yannayinta sai a hankali, domin karfin Hali ne Mah ke yi fiye da kowa a gidan nan, dan bata so ko kadan ta nunawa YUSUF bata da lafiya ko wani abin dan ta tabata idan ya ga haka zai tare a kanta ne, bayan yanzu da da ba daya bane, shine fa da ta mike ya kula kamar tana layi ya mike bai yiwa kowa magana ba yake biye da ita ita din da kanta sai da ta ganshi ta yi masa murmushi, shima ya mayar mata ama ta ga alamun ba zai koma ba sai kawai ta yi hakuri suka jero suka nufo dakin nata dan ba wani nisa tsakanin dakinta da bangaren Bah, sunna kawowa daf da kofar zata bude ne ta ji maganar RAUDA sama sama hadi da ruwan murya mai nuni da kuka Raudar na fadin " Inna, wai Abdul din ne ba'a gani ba tun jiya? Tun jiya bai kwana a gida ba ama ba'a sanar min ba? Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une ganinan zuwa Inna ganinan "
Tana fada ta mike daga zaunen da take ta shiga neme nemen abinda bata ajiye ba, sai da ta tuna jakarta karama na dakin Salima da sauri ta nufi hanyar fita tana tunanin tabas ba zata rasa kudi a jakar ba
Tun kafin ta bude kofar Mah ta bude ta shigo dakin hakan ya sa RAUDA ja baya da sauri dan bata tsamaci gannin mutun ba, sai kuma YUSUF ya shigo shima kamar yadda Mah ke kallon RAUDA haka shima ya dubeta ya dauke dubansa yana ษorawa saman fuskar Mah wace ta fara magana tana kallon RAUDA da fuskarta ta cika da hawaye a tausashe sosai ta ce" Lafiya na ji kamar kina kuka ga kuma fuskarki da hawaye?"
A hankali Rauda ta kifta idannuwanta, hawayen suka sake zubowa, ta kasa rike abinta sai kawai ta karaso ta rike hannun Mah dan ta sabar mata da haka tana kallonta ta ce" Mah, Abdul ne , Abdul ne ba'a gani ba wai tun jiya kin san wajen kakarsa na kai shi, to ban san ba'a ganshi ba tun jiya, shine take fada min yanzu da na kira, dan Allah Mah ki yi hakuri yau na fita na je na neme shi, sannan ki bani dama na sake bincikar uncle dina, zan dawo Mah ama zan nemo su, dan Allah ki barni na je dan su din duniyata ne, Abdul bashi da cikakkiyar lafiya kar aje ...kar aje ya fada wani waje ya rasu........." sai kawai ta barke da kuka ta yi cikin Mah ta rukunkumeta.....
Ita dai idannuwanta a rintse ta ji kamar zasu fadi kuma sai ta ji su basu fadin ba , tana dai jin Mah na dadaba bayanta tana mata shiiiiiitttt kamar wata baby bayan a halin nan da take ciki bata jin shiiiiiiiii zai saka ta yi shiru, sai kawai ta idasa rikicewa tana kuka bilhaki tana kiran ta shiga uku
Har sai da abin ya ishe shi sosai ya girgiza kai a riken da yake da su ya dan yi gyaran murya da kakaurar muryarsa ya ce" Dan dagata mana ke kar ki kayar da ita"
Dif ta yi da kukan da take rairawa wai ita ta ji dadin rungumar uwa, har sai rusheshiyar Muryar nan ta wani katse ta, dan haka ta dan dakata sannan ta dago a hankali tana za sauke ajiyar zuciya, nan ta ga daga ita har Mah din a saman kaffafuwansa masu ษauke da takalmin fata da damatsunnan hannayensa dake sanye cikin lalausan yadi blue an yi gari da yar ciki ษinkin sarakai, sai rawaninsa da har ya shafi kanta suke, daga ita har Mah din, karfin rungumar da ta kai ta damki damtsunna ashe nasa ne, hakan ya sa da sauri ta saki ta yi baya tana jin faduwar gaba da dokawar zuciyar da Salima ke yawan fadi a kan yayan nasu
Mah ta dan daki gefen hannunsa ta ce" YUSUF kar ka tsoratar min da yarinya mana, zo nan yar gidan Mah taho babyna" Mah ta fada tana karasawa wajen kujerar dakin ta zauna
Shi abin ya ba mamaki, wai Babyna, ita sam bata wani ji mamaki ba domin ba yau Mah ta fara kiranta da sunnan ba, dan haka ta karasa ta zauna daf da Mah din ta sada kanta
Mah ta kama hannayenta tana kallonta da kula ta ce" Bana son yawan kukan nan RAUDA, saboda mace kike kalubalan rayuwa Allah na iya zubo maki masu girman gaske kin ji? Tabas na san akoy tashin hankali, ama zan fi so ko menene ki fara dubansa da jajircewa, dan kuka da saka damuwa a rai na saka mutun ya kamu da ciwo marar magani dan ciwon stressa ya fi komai kashe bawa , maganinsa kuwa shine baban abinda yake mystere kin ji?"
A hankali RAUDA ke gyada kanta
Mah ta ce" Zaki iya yin hakuri a jima a yi magariba mu je tare ko a saka direba ya kai ki sai na tardo ki?"
A tausashe ta ce" Mah, ina so na je sai na fara dubawa kafin ki karaso"
Mah ta yi murmushi ta ce" To ina da ina zaki duba din?"
RAUDA ta gyara zamanta ta ce" Zan duba makarantar su, mu yi maganar da malamin su, sai kuma mu duba ko'ina a anguwannin na tsakanin gidan da makarantar tasu"
Mah ta gyada kai ta ce" To shikenan, tashi ki bude cen akoy abayoyi ki saka abaya a cikin hijabin nan kar ki fita daga ke sai rigar nan a kasa dan ana ganewa rigar bata da nauyi, bari na yiwa direba magana sai ya ga inda ya ajiye ki in an jima ya zo ya daukeni mu nemo Abdul dinmu ko?"
RAUDA ta mike ta ja hijabinta ta yi masa diban albarka a gaban mutane , a gaban mutane jama'a dan sam.ta sha'afa a dakin nan ba daga ita sai gyatumarta bane, da maza a tsaye kikam jama'a ta je wajen akwatin ta bude ta shiga dubawa har ta ciro bayar da aka ce ta dauko ta juyo ne ta ga kato a dakin nasu wanda sam ta manta yana wajen, Mah na bashi takardu tana masa bayani hankalinsa a kan Mah din
Da sauri ta juya ta diba ta yi bayi da dan gudu har kamar zata kifa, hakan ya sa Mah dagowa ta rakata da kallo, shi kuwa ya yi tsai har sai da ta mako kofar bayin gam ya rintse idonsa sannan ya bude ya gama amsar sakon Mah yana kallonta a tausashe ya ce"Mah ina zaki je?"
Mah ta idasa bashi takardun ta ce" Binta zan yi YUSUF ka ga maganar uncle din nan nata tunda abanka ya kaiwa comitionna bamu ji komai ba, gashi yau fa kwana tara cif , ga wannan tashin hankalin kuma , bana so wannan abin ya taba lafiyar marainiyar Allah, ina mata fada ne dan na karfafi gwuiwarta, ama a gaskiya tana da kokari dan ba kowa zai iya jurewa haka ba,"
A tausashensa, ya sake budar bakinsa yana magana ta fito daga bayin ta je dan ta saka hijab dinta, ya ce" Ki tura min numbar wanda aka kirayan, zan shiga maganar, sannan ta zauna zan saka a dubo mata *d'anta*! Domin babu inda uwata zata je ba tare da Ni ba."
Yana fada ya juya yana tafiya ne, maganar da yake tunanin a kasa kasa yake yi ta cika dakin ne, hakan na nufin RAUDA ta ji abinda ya fada daya bayan daya a tare suka bi shi da kallo, kafin Mah ta juyo inda take tsaye ido na mata ruwa ta karaso tana dubanta ta ce"
Hi people
Azl 23
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har