Showing 117001 words to 120000 words out of 188741 words
da kudinki fa idan akayi lunching๐๐ปโโ๏ธ๐บ๐ .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*
๐๐ผ Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu ๐๐ผ๐๐ผmusamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)
Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan๐๐ผ (magnifique)
Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account ๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ (da wa kika ja Madame?)
Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba๐๐๐ sai kun zo
A hankali Rauda ya furta" ABDALLAH? Kai ne?"
jin shiru ba amsa, ya Sakata yin adu'a ta sake kunna sauran fitilun dakin ta nufi gadon tana tarare hijabinta ta hau hannunta na rawa ta yaye bargon tana Kiran sunnan sa, domin tana yayewar fuskarsa ta bayyana da shadar dake jikinsa , sai uban zafin da jikinsa ya dauka tamkar garwashin wuta
hankali tashe ta ajiye wayar tana sake kiran sunnansa ta ce" Abdallah, dama kana cikin gidan? Baka da lafiya ama ka kasa fada min?"
Da kyar ya bude idannuwansa da suka yi kore sharrr ya sauke dubansa a saman fuskar ta
murmushi ya kakaro da kyar yana fitar da huci a saman lebensa ya furta" An kawo min ke? Alhamdulilah ya rab da ka amince min har na ganta a dakina, wifey zo , zo jikina Please"
Kasa zuwan ta yi, saboda bata taba aikata haka cikin hayacinta ba, sai dai kallonsa take yi tana murza yan yatsunta muryarta a raunane dan yannayin idannuwansa sun rikitata a hankali ta ce " Ka tashi mu je asibiti Please, ka tashi"
Nokewa ya yi yana kallonta ya ce" Na ki din, dan kawai yan lokutan da suka rage min su kare min ina barci, dan na tabata idan na je allurar barci zasu maka min shikenan na yi asara na tafi ba tare da na kalli fuskarki ba?, Please zo jikina, kin ganni fa, babu abinda zan iya yi maki koda a tsaye nake, zo in rungume ki, kin manta kin ce min idan muka yi aure zaki rungumeni da kanki, dan Allah ki ture kunyar nan da kike ji kin ji?"
RAUDA ta ji hankalinta na neman tashi sosai, a tsorace take kallon sa, irin yadda ya dage sai ta shiga jikinsa kuwa wata irin kunya ce ta gaba dabaibaye ta, kana ganninsa kuwa zaka tabatar da yana cikin matsanancin hali ne, dan haka ta rasa yaya zata yi masa, gaba daya ta mike ta ringa bincikar wayarsa a dole sai ta ga numbar likitansa , lokaci daya tana tambayarsa numbar likitan nasa? maimakun ya fada mata sai yace da ita dan Allah ta taimake shi ta yi masa kiran numbar Mah
shatakai ta tsaya tana kallonsa, sai dai gannin ya ja wani irin numfashi kanta ya sara ta shiga saka numbar Mah , a lokacin kuwa Mah din sunna hanya dan sun ajiye Atu kennan za'a nufi gida da su wayarta dake hannun Salima ta yi ta ringing
Salima ta duba mai kiran, tana ta sake dubawa kamar numbar Abdallah dan haka sai ta daga tana mikowa Mah ta ce" Mah kamar numbar Abdallah"
Mah ta amsa tana fadin" ABDALLAH kuma?, hello asalamu alaikum"
RAUDA ta yi iya yinta dan ta yi magana sak ba tare da ta yi kuka ko gargadar murya ba, ama abin ya faskara
A hankali ta furta" Amen wa alaiki salam Mah, Rauda ce"
Mah ta yi saurin fadin" Babu, kuka kike yi? lafiya?"
RAUDA ta sake juyawa tana kallonsa, a hankali ta ce" Mah, Abdallah ne, bashi da lafiya kuma yace a yi kiranki wai"
Mah ta ji gabanta ya fadi, tana kallon direban YUSUF ta ce" Mu koma gidan baby, baby ganinan ki zauna ki daina kukan ganinan in sha Allah"
RAUDA ta ja numfashi sai kawai ta fashe da kuka ta juya tana kallonsa lokaci daya tana sakin wayar nan ta koma saman gadon a hankali ta karasa inda yake kwancen a hankali ta bude hannayensa ta shige jikinsa, jikinta na rawa ta rintse idannuwanta, muryarta na rawa ta ce" Ka manta, ka ce min RAUDA in dai ina raye, ba zaki yi kuka ba, Nine mijinki, Nine yayanki, Nine komai naki, to menene kuma kaima kake wani abu kamar wanda zaka bar Ni? shikenan Ni duk wani makusanci nawa sai na rasa? Abdallah, kar ka yi min haka Please"
Murmushi ya yi, a hankali ya sake rungumeta a jikinsa, ama bakinsa ya gaza furta koda a ne, dan sosai abin ya fara motsawa, sai dai yadda yake jinta a jikinsa ya zame masa wani nau'in salama a cen cikin zuciyarsa, wato zuciya da abinda take so
A bangaren Mah kuwa direba na tuki kamar zai tashi sama, ita kuwa tana tambayar Salima da tace ko ciwonsa ne ya tashi cewar wani ciwo fa? wani irin ciwo?
Salima ta yi tsuru tsuru, dan RAUDA ta yi mata magiyar kar ta sanarwa Mah a lokacin da Salimar ta san cewa yana fama da matsanancin ciwon zuciyar da likita yace idan har bai yi gaggawar zuwa aka cenza masa ba tabas kowani lokaci yana iya mutuwa, shi kuwa yace ba zai yiwu ya je a Barka shi a cire masa zuciyarsa ba a saka masa wata bayan a cikin kashi dari daya ke rayuwa da irin aikin nan, salon ya yi biyu babu, a lokacin nema ta ji matsalarsa ta rashin haihuwa kuma a ranar ne ta gane Rauda wannan ba damuwarta bace dan itama burinta kennan rashin haihuwar
"Salima?" Mah ta fada a lokacin da motarsu ta shiga katon get din gidan tana kallonta
Salima ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Mah, yanada ciwon zuciya ne, wanda ya kai matakin karshe, shine nace ko shine ya tashi?"
Dif Mah ta yi tana kallon Salima, ciwon zuciya? matakin karshe? subahanallah, kuma yake zaune bai je asibiti an masa aiki ba?
kasa cewa komai ta yi ta bude motar ta fita har tana buge kafarta saboda tunanin halin da Rauda ke ciki ita kadai da shi, domin ko masu aikinta ba'a kawo ba Bah yace wai sai ta yi sati a gidanta an kawo masu aiki
Salama Mah ke yi tana kiran sunnan RAUDA, hakan ya sa RAUDA mikewa a hankali ta sake juyawa ta kalle shi, sai ta ga ya sakar mata murmushi kasa kasa ya furta" zaki iya kama hannuna na dan daga?"
RAUDA ta gyada kanta, a nutse ta dauki pilow biyu ta jinginar masa a jikin bed din sannan ta kama shi da kyau ta jinginar da shi a jikin pilow din ta gyara masa bargon sosai a kaffafuwansa, shi kuwa yana Binta da murmushi a hankali ya furta" Wannan kashin turaren naki akoy dadi, kin ji shi a hannayena har yanzu"
Ita dai bata tunanin kanta na iya daukar raha ko gane rahar da yake yi mata , har sai da ya sake fadin" Ki sanyo su nan Please" Sannan ta sauke ajiyar zuciya ta fice
Tana fitowa ta ga Mah tsaye, Salima a gefenta, ga dukkan alamu ita suke jira,
ajiyar zuciya ta sauke a sanyaye ta karasa jikin Mah da ta mata alamun ta zo
A tausashe sosai Mah ta ce" Jikin nasa ya tsananta ne kike kukan nan?"
Da kyar RAUDA ta iya budar bakinta, tana haki tamkar zata summe ta ce" Mah, Ni dai na ga yana ta wani iri, wai yace a kirayeki"
Mah ta furta" Ok,ki ce masa na zo"
RAUDA ta sada kanta ta ce" Baya iya tashi fa, da kyar yake magana, Mah baya iya tashi shi yasa yace ki je"
Bah ta lumshe idannuwanta saboda gabanta da ya fadi
Da kyar ta boye damuwarta ta mika hannunta ta amshi wayar dake hannun Salima ta ce" Bari na sanarwa babanku dan ya sanarwa Hajia kar ta ga mun jima"
Kai Rauda ta gyada, sannan ta karasa wajen Salima suka zauna Salimar na rike da hannunta tana fada mata ta daina kukan nan in sha Allah ba komai bane zai mike haka masu ciwon zuciya suke
Gannin ta kasa samun numbar Bah ana ce mata a kashe sai ta yi kiran ta Hajia, wace jimamin abinda take ciki ya sakata kasa gane jimawar da su Mah din suka yi, tana cen tana ta neman mafita a falonta ta daga kiran a tausashe ta furta" Andiya, kin dawo ne?"
Mah ta sauke ajiyar zuciya, a tausashe ta sanarwa Hajia basu dawo ba, har sun kama hanya kuma ga abinda yake faruwa
sosai hankalin Hajia ya tashi, ga tarin mamakin Mah sai ta ji tana fadin" Bari in nemo Bellon, idan ban ganshi ba kuwa zan sa a min iso wajen Malik dan na zo , kafin nan ku yi kokarin sada shi da likita, Allah ya bashi lafiya"
Mah ta amsa jiki ba karfi ta datse kiran, sannan ta dubi su Salima ta masu alamun su yi gaba
gaba na baya suka shigo dakin, a lokacin ya saka abinda yake tarawa idan yana tari ya gama yin tarin kennan yana goge abin jinnin da ya bata masa baki ya yi gaggawar cirewa daga bakinsa da sauri ya so boyewa, sai dai karfin jikinsa bai bashi dama ba ya saki abin a kasa, gashi du yadda ya so dagowa dan ya dauke ya kasa, hakan ya sa RAUDA da ta zubawa abin ido karasowa ta duka ta dauka ta bude
kusan a tare suka juyo suka zuba masa ido, Mah hankali tashe ta karaso tana fadin " Subahanallah, jinni ne daga bakinka?"
RAUDA kuwa sai ya kai zaune a nan kasa ta zuba masa ido, gannin yadda ya sada kansa , kunya ce ko menene? ya dai ฦasa kallon Mah ido cikin ido har sai da abin ya lafa masa ya dago yana duban Salima a hankali ya ce" Sister, Please daukowa Mah kujera Gatacen, nd ki bani wancen akwatin dake saman dayar kujerar"
Salima ta juya ta cika abinda ya ce din jiki ba karfi
Akwatin da aka ba Mah ta bude ta ringa fitar da takardu na dukiya daya cikin daya cikin daya, da wata takarda mai dauke da code na banki, da ky cike a akwatin, sunne suka saka akwatin yin nauyi
sunnan dake saman kowace takarda ya sakata dagowa, itama zuwa lokacin nata hankalin ya fara matukar tashi yana kallonsa ta ce" me kennan?"
Abdallah ya sauke ajiyar zuciya a tausashe , murya a jinyace ya ce" Zan so ace, tun ina cikin hayacina na cika abinda nake son cikawa, domin ke da kanki kin san idan aka zo wannan gabar kuma sauran saura ne, dan Allah ku yi hakuri, ba aurar maku yarinya bayan na san abinda nake ciki, da ace bata yarda ba duk irin yadda nake da burin aurenta ba zan tirsasata ba, Ni dai na san ina sonta domin Allah, shi yasa tunda na san da wahala ta rigayeni barin duniya na yiwa kaina wannan alkawarin na dukiyata itace maganarsa, Ni bani da dangi, koda ina da su ban san inda suke ba, basu san ko akoy Ni a duniya ba, iyayena sun yi aure ne irin na yawon duniya, mahaifina ya auri mahaifiyata, kuma Allah ya yi basu jima da auren ba suka koma ga mahaliccin su, dukiyata ta halal ce, ba gadonta na yi ba, nema na yi da zufata har na kai inda na kai, tafiyar nan da na yi na tataro komai nawa da burin yin rayuwa mai dan tsayi da ita na dawo nan kuma na yi shige da ficeta da lauyana an min abinda nake so, sai dai kashhhh, tunda satin aurenmu ya kama na zama ganinan, a kulun baya lafiyata ke yi, ko yau daurin auren nan da kyar makotana suka kamani muka je,ana gama daurawa na samu na dawo dan ba zan so ace tana cikin taron nan an je mata da maganar na fadi"
"Ya Salam, Abdallah, ama ciwo ai ba mutuwa bace ko? dan Allah ka daina magangannun nan mu je asibiti, ke ku tashi ku fadawa direba ya zo ya kama mana shi mu je asibiti" Mah ta fada tana tare hijabinta tana tare kukan dake son kwace mata, dan yadda yake magana yana jan numfashi ta bakinsa ko baka da imani sai ka tausaya masa
bai hanna su fita ba, sai dai sunna fita ya dubi Mah a lokacin da mike jikinta na rawa ta sake shiga neman layin Hajia ya ce" Mah, ciwona ya zama Cancer fa, dan Allah ku bar Ni na mutu a saman gado........................"
A lokacin ne kuma Mah ta juyo da sauri tana kallonsa, ta ki cewa komai sai nunawa direba da ta yi ya dauko shi su je, dan walahi ba zata taba iya barinsa a haka ba
Hajia kuwa sunna gama waya da Mah ta saka baban hijabinta itama tana neman layin Bah ama bata shiga hakan ya sa kawai ta nufi Part din Malik da fatan Allah ya sa bai kwonta ba, tare da yan rakiyarta
sunna karasowa basu tsaya kiraye kiraye ba suka bude mata ta wuce ciki
a bakin kofar nan mai madubi ta tsaya ta buga sannan ta murda ta shiga
A kwonce da yake idannuwansa kawai ya dago ya sauke a kanta sannan ya lumshe yana godiya ga Allah da ta zo a daidai lokacin da yake da bukatarta
Karasawa Hajia ta yi, ta zauna a kujerar dake daf da shi a sanyaye ta furta" Yau ko a leka Ni? Malik wuni guda?"
Shiru ya mata dan ya san dama sai an masa yan jaje,
Idannuwansa ya dago jin ta ce" Yaya muka ji da wannan sabuwar masifar? yau Ni Hajia Azal ta fado mana gida, Malik ba zan so ka ga yarinyar nan ba, kade kaden nan fa da ka ringa juyowa su ne, Ni kam safiya na yi ka saketa ta je gidansu, ba matar jikana bace y'ar nan ido a tsakiyar kai!"
Murmushi ya yi ya sake dago da kansa yana kallonta, kasa kasa sosai ya furta" Ta fado maki dai, kuma ba inda zata je!"
"na'am? me kace?"Hajia ta fada tana dubansa, dan yadda ya yi murmushin kamar wanda zai datsa mata magana domin haka yake yi mata lokuta da dama
kai ya cire ya ki bata amsa, a nutse ya ce" Bani da lafiya fa, kuma ina jin kamar wanda zan mutu, kin ga jikina karra rikicewa yake yi fa!"
a tsorace ta kalle shi, da sauri ta mike gabanta na faduwa tana sake duban yadda ya ringesa, ta kai hannunta wajen wuyansa, ai kam da gumi jikin nasa sosai dan haka ta nemi rikicewa tana fadin" Na shiga uku, ka ga cen wai mijin RAUDA ne akace ba lafiya shine na zo sanar maka ka sa a kai Ni, kuma sai in ji wai kana min zaka mutu?"
Idannuwansa dake lumshe ya bude a kanta, sosai ya so yin magana, sai dai ya rasa me zai ce, ya so maida idannuwan nasa ya rufe wayar Hajiar ta sake daukan kuka
a tare suka kalli wayar, Hajiar ta duba da kyau tana kankance idannuwanta ta ce "AMEERA din ce, bari na ji?"
Hajia ta daga kiran ta saka a amsa kuwa, sai ta ji Muryar Salima tana dirzar kuka tana fadin......
๐ญ๐ญ๐ญ๐ญ๐ญ๐ญ๐ญ๐ญ
Salima na dirzar kuka take fadin" Hajia, walahi fa inaga ya rasu innalilahi mun shiga uku!"
Hajia na tsaye ne, sai gata a zaune ta zube, idannuwanta na wani iri muryarta na rawa ta ce" Ke kuwa wani irin kina ga, dan Allah bani ANDIYAR!"
YUSUF dake ringeshe ya yi niyar dagawa Hajia hankali ne sai ya mike zaune yana kallonta , jin ta ambaci Andiya, kuma maganar rasuwa
Hajia walahi ita Raudarma ta summa, kuma Mah gatanan tana kuka, shine na yi kiranki dan walahi walahi Mah ta rufe shi ama direba ya taho gidan yanzu "
Me Hajia zata yi banda kwasar kuka, hannayenta saman kai wiwi take fadin" Mun shiga uku mun lalace wayo jikata ta rasa miji, innalilahi yau na yi wani rashin, la'ila ha ilalahu Muhammadu RASULULAH Sallallahu alaihi Wa sallam "
"Wai meye haka wai?" ya fada da dan karfi dan yadda Hajia ke rizgar ihu a kan abinda ba'a wani tabatar ba kuma bayan ba kyau yiwa mamaci irin kukan nan ya saka shi katseta yana mikewa tsaye
hankali tashe Hajia tace" YUSUF wannan yaro balaraben nan da ya gaisheni, shine ya rasu,dan Allah ka sa a kai Ni ka ji?"
Gaba daya jikinsa sai da ya mutu, a hankali ya koma ya zauna yana daukan wayarsa ya yi kiran direbansa amintace
jim kaษan ya daga da salama a ladafce ya ce" Allah ya taimakeka gani na shigo dan na iso da sako, Allah ya yiwa mijin Hajia karama rasuwa, na baro su Mah a cen dan na zo na ji abinda zaka fada"
Ya jima wayar a hannunsa, zuciyarsa na tsintsinkewa kafin a hankali ya furta" Allah ya masa rahama, ka wuce ciki a je da likitoci su duba shi da kyau, idan sun tabbatar a gyara shi a zo nan da shi , idan bai rasu ba maza a kawo shi in yanzu za'a fita da shi a min magana"
Daga nan ya kashe kiran yana kallon Hajia take ta margaya kai taba sharar hawaye
ajiyar zuciya ya sauke, sosai jikinsa ya mugun mutu, dukda a bincikensa ya san da ciwonsa da irin matakin da ya kai domin Taj sai da ya je har wajen likitansa, da likitan ya ki fadin sirrin abinda ke yawan kai Abdallah wajen nasa sai da aka sada shi da YUSUF din sannan ya fada tun a nan ya ba masu gadi damar duk lokacin da ya zo su bar shi ya shigo, sannan ya dauke kansa a kan duk wani shige da ficen su sai na ranar da ta shigo da dare nan ya ji haushin abin, shima a lokacin dan Hajia ta gama guma masa tashin hankali ne na wai ita zata zabar masa matar aure
A nutse ya ce" Ki yi hakuri, idan ya rasu baya bukatar koke koken nan, ki masa