Showing 66001 words to 69000 words out of 188741 words
12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE
๐๐ผ Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching๐๐ปโโ๏ธ๐บ๐ .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*
๐๐ผ Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu ๐๐ผ๐๐ผmusamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)
Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan๐๐ผ (magnifique)
Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account ๐๐ผ๐๐ผ๐๐ผ (da wa kika ja Madame?)
Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba๐๐๐ sai kun zo
Mah na dubanta murya a tausashe da yannayin son rarashinta ta ce" My daughter, zaki iya hakuri mu ga abinda zai yi? Idan bai yi wani yunkuri ba na maki alkawarin raka ki da lokacina da komai da ya dace dan mu nemo su,zaki iya hakura kuwa mu ga abinda zai yi?"
Nauyin Mah ya rufe mata zuciya, duk irin abinda take ji a zuciyarta sai ta ji ta gaza yi mata musu, ko ba komai masoyi ai ba makiyi bane , sai dai wani irin abu da ya tokare nata zuciya na haushin YUSUF mai karfi ne, ta rasa me zata yi tunani a kansa bayan ta tabatarwa Mah zata yi jira Mah din ta shige wanka sai ta fice ta tafi dakin Salima dan ta fi jin nutsuwa a cen, bata san me yasa jininsu bai hadu ba da yan matan gidan nan, Yaren kuwa tsakaninta da su idan sun hadu su gaisheta ta amsa dan bata cika shiga sabgarsu ba, bale abinda ta kula in dai sun fito tare Salima ta ga mahaifiyarta takan daina yi mata magana har su bar wajen, bata san me ya sa ba, abu daya ta sani shine irin yadda ta rayu da Mama ta dauki darusa da yawa na zaman duniya, kuma bata tunanin akoy wani abu da zai iya tunkaro ta ya shige mata duhu
Tana komawa ta dauko Alkur'anin Salima ta zauna ta shiga karatu, tun tana yi a fili har ta koma a zuciyarta, a hankali ta ringa jin salama da sansanyan tunani a kan damuwarta, ita fa a yanzu ba zata ce damuwar rashin wani a kusa ta fi damunta ba, ta fi kyautata zaton damuwar rashin Sannin halin da mutanen da suke jinninta ta fi damunta, dama ita ba irin mutanen nan ne masu daukan wata Aba wai ita soyaya da mahimmanci ba, tun a lokacin da ta so yin soyaya da wani saurayi a aanguwarsu Mama ta zaunar da ita ta yi mata karatun ta nutsu ta wanke mata kwakwaluwa tassssss fa sanar mata irin soyayar nan ta masu gata ce, ba irinta ba wace ta ta fara irgen dangi ta isa ta kawo a yi kashi mu raba a biya haya da shinkafa da wuta da ruwa da dan na cefane, sai ta watsar take tafiyar da rayuwarta daidai da zamani, a tafiyarta kuwa babu kalar wanda bata hadu da shi ba, dan akoy wani da ta taba yi saurayi ya dauketa a mota ya nufi hanyar daji da ita wai zasu je su huta, ya rufe ta a mota ya nemi ilata mata budurci da kyar Allah ya kawo wani makiyayi ya kwaceta ya yi mata sumul tamkar ya santa ya fada mata cewar idan saurayin nada laifi ita ta fi shi laifi, kuma ta kula dan ba kulun Allah zai kawo mai kwatarta ba, in dai tace zata yi wannan rayuwar sunnan mutuncinta barare!, ta gani din, ta kuma yarda da maganarsa, dan mutane da yawa da take ganni da mutunci sun fito mata ta bayan gida a lokacin da suka gane gatanta a duniya mai rauni ne, wanda ke iya tsaya mata shi da kansa bai tsayawa kansa ba bale wani, sai su nemi shiga gonar da take ba tasu ba, da yawa ba maganar soyayar a tsakaninsuma sun nuna mata sunna iya yi mata maganin wata damuwa Tata da ta shafi kudi a duniya ta dan lokaci in har zata basu kanta, wannan dalili ya sa itama ta koyi wata irin rayuwa mai wuyar fassara, tana dukan aljihun maza ba sauki, ciki harda balarabenta da take tunanin tana iya aurensa dan ya nuna alamu da yawa dake nunin yana iya zamowa uban marainiya ba tare da ya wulakantata ba, a sanyaye ta jinginar da bayanta jikin gadon dakin tana ta tunanin shin ina Abdul zai shiga? Kar dai wa'inda suka dauki uncle ne suka dauke shi? Ama shi me zai yi masu na anfani ko me ya tare masu? Ya Allah ka tsare min uncle da Abdul a duk inda suke, ka sa a gansu cikin hayacinsu alfarmar mai alfarma a fadarka.
Likitocin nan sun gama duba takardun da aka yiwa Aba gwaje gwajen rashin tashinsa, dan tun a kwanaki hudu da faduwar sa aka daina saka masa maganin barcin, sai gashi har yanzu bai farka daga duniyar barcinsa ba, har an saka masa abin ciyar da mutun idan baya cikin duniyar mutane a makogwaronsa ana ciyar da shi da kalar abincin mai ruwa ruwa da kuma karin ruwan dake aiki a jikinsa
A lokacin likitan ya nuna dole sai an tafi da Bah asibiti saboda wani gwajin da ba za'a iya kawo na'urar har nan ta yi aiki yadda ake so ba, a dole aka saka aka kawo ambulance ya zamo Hajia na wajen , Hajia A'isha na wajen, wace tun abin nadin nan ta buya bata yarda su hadu da Hajia bale har ta amshi hukuncin da ta tabatar yana jiranta mai zafi daga Hajiar, sai yau da ta ji za'a fita da mai martabar a washe gari sai gata a cikin makusantan sa na kud da kud a tsaye a falon a lokacin da likitan ke ciki yana sake duba shi dan an kawo ambulance din ama ba zai yiwu a fita da shi a yanzu da dare ke shigowa ba , dan yannayin dare da abin hawa ga dajin dake tsakanin asibitin da fadar ba mai kyau bane, sai kawai aka hakura likitan tai kwana wajensa har ya gama abinda yake yi ya yi zaune a dakin sannan YUSUF ya fito ya samu ahalinsa dake jira ya sanar masu da sauki sunna iya tafiya sai gobe za'a kai shi,
Daga nan ya kama kujerar Hajia yana turata dan ya kaita bangarenta ne Hajiar ta dago tana dubansa a tausashe ta ce" Kar ka bari Nana ta biyo mu, kuma kar ka bari ta yi tafiya a bayanmu dan Ni ban yarda da ita ba kuma"
Komai a kunnayenta, a lokacin kuma ta yi niyar bin nasu ne, sai ta ji kaffafuwanta sun tsayar da ita sakamakon kallon da ya juyo yana yi mata dan ya gane ko ta ji kuwa abinda mahaifiyarta ta fada?
Gannin ta ji ya saka shi sakar mata murmushin da ya kayar mata da gaba, dan walahi har cikin kashinta ta ji wani sanyi mai wuya na ratsa ta saboda murmushin nan nasa, dan haka kawai ta ji a ranta ba murmushin alkhairi bane , gashi tunda girman sarauta ta hau kansa ya zame mata kamar wani dodo, har mamakin harshenta take yi a yanzu da take gaza kama sunnansa tashi daya, bayan a da da kai take kiransa dan badangarci da isa sannan ta fada masa abinda ta ga dama
Jiki ba karfi ta juya ta bi hanyar nata bangaren , dan a gidan take rayuwa da mijinta wanda da shi da babu du daya, dan babu abinda ya isa ya saka ko ya hanna a gidan sirikansa, zama ne ake yi tamkar itace mijin, shi kuwa matar, kuma mutun ne mai abin hannunsa daidai gwargwado, dan ya fi karfin masara da shinkafa, ama mugun katari ya afko shi da mace irinta , tun yana gannin zai iya tankwasata a hankali, har ta gama tankwasa shi, yana zaune yana raye ko iyayensa in ba su suka zo ba bai cika zuwa ba, kuma lafiyarsa kalau, kawai duniyarsa itace da ฦดaฦดansu
Kafa take jefawa har ta karasa cikin falonta ta nufi kicin da sauri jin kwaramniyar ta yi yawa a ciki dan kamar ana dukan wani abu haka take juyowa
Tana shiga ta kwalalo ido sakamakon gannin yarinyarta mace daya cilo wajen frij tana ta ciro abubuwa tana zubarwa da sauri sauri kamar wace ke neman wani abin da ta ajiye
"Dayana" ta fada muryarta har kamar tana rawa
A firgice Dayanar ta juyo tana ta kokarin murje idannuwanta dan ta ga mahaifiyar Tata da kyau sannan tana jan rigarta dan ta daidaita tsayuwar ta, idannuwanta masu tsarin halitar gidan su YUSUF sun yi luhu luhu sun yi ja na cikin kuwa sun karra girma da duhu, lebenta ya yi Jajajir kana ganninta ka san a bige take dan duk yadda ta so ta daidaita kanta kasawa ta yi sai numfashi take saukewa da karfi dan ta hanna a gane hallin da take ciki
Rai bace, murya sama sama mahaifiyarta ta karasa daidai lokacin da RISLAN ya shigo bangaren nasu da hannun yarinyarsa rike a hannunsa ya jiyo Muryar mahaifiyarsa da ta shaki wuyan DAYANA tana fadin" Dan ubanki shaye shayen kika koma? Nace dan ubanki wani abin kika sha kuma?, DAYANA gwara na kashe ki na huta da dan iskan halayar nan da kike yi a duniyar dan ki sakani a uku, gwara in san na kashe ki na huta ya isk........................"
Da sauri ya karasa yana kama hannayen mahaifiyarsa ya shiga kwalkwata a raunane sosai yana fadin" Subahanallah, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une Mama, dan Allah ki saketa, ki bari kar ki aikata aikin dana sani , kin rike mata wuya sosai fa"
Da kyar ya iya kwatar Dayana, ta rarafa a rikice ta hade bayanta jikin frij din kicin din tana ta fitar da harshe tana numfashi da kyar tana murza makogwaronta tana kallon mahaifiyarta
Nana ta nunota a kausashe ta ce" Karya kike ki jaza min abin magana again a gidan nan, dama ido a kaina, karya kike yi ki jaza min abinda za'a fita ana zagina, gwara ki san kin bar kasar nan da ranki da na fitar da ke daga duniyar , dan a shirye nake tsaf yakina yanzu na fara, koda ina son ki, koda kina neman nuna min kin fi karfina bakya jin maganata kar ki manta tushe, duk abinda yake kanki daga nawa ya tashi, kai kuwa uban me ka zo min yi gida? Ba na maka iyaka da fada ba marar anfani?"
Kai RISLAN ya sada, gabansa na faduwa ya kasa dagowa bale ya amsa
Nana ta ja tsaki a juya dan ji take yi kamar zata kifa ta fice da nufin zuwa ta sakarwa kanta ruwa ko zata ji nutsuwa a jikinta kafin ta zauna ta yi tunanin abinda zai fisheta
Dayana kuwa yadda ka san mahaukaciya ta shiga wani irin abu kamar tana karatu a makarantar allo tana ta maimaitawa a rikice tana fadin" Bata son shi, saboda shi take yin wannan abin, Ni kuwa ina son shi, kuma koda bata so sai na aure shi, tunda ina son shi, Ni dai so nake yi ya so Ni Ni dinma, ina son shi, shi nake so tun kafin ta sa na fara soyaya da uban Kulsum, ta kuma sa na auri Sarkin yaki, sannan yanzu tace kuma ba zan so shi ba? Babu inda zan je, ina nan, ina gidan nan, sai ya aure Ni!"
Tausayi da tarin tsoro suka saka RISLAN jin hawaye na sauka a saman kuncinsa
Mikewa ya yi ya kamata ya mikar da ita yana kiran sunnanta, da kyar ta saurara tana kallonsa a tausashe ya ce" Na san kin san me kike yi, kuma kina jina kina gane me nake fada, yanzu Dayana kina tunanin wannan halin da kike neman maidowa rayuwarki wanka kika daina da jimawa ne zai sa ya aureki? Na zata kin ce shisha kadai kike sha, itama ina ta kokari dan ki daina ashe baki daina ba? Dayana kina tunanin namiji ko lalatace ne zai so ajiye uwar iyalinsa lalataciya?, haba Dayanar dad, ke fa ba yarinya bace , zuwa yanzu ya ci ace kin fara gane ba komai ne alkhairi a duniyar bawa ba, kuma tsananta abu ko menene banda abinda ya shafi neman ilimin addinin musulunci bashi da kyau, me yasa zaki yaki kanki da kanki? DAYANA YUSUF fa ba mijin balagazar mace bane, kuma ke kin san ba shine mai halayar da ake masa kallo ba, kuma kin san tushen labarin abinda ke kokarin nutsa shi cikin sabon Allah ko menene, kuma kin sani sarai har yanzu ba'a yi nasarar abinda ake so din ba, shine ke zaki zo ki yi kokarin sake riko sabon Allah din da nufin Allah ya baki abinda kike so? Haba Dayana sai kace wa'inda muka zo wajen da zamu dawama?"
Kwarai tana gane yarensa, kuma tana jin komai a kan gaba
Hakan ya sa ta fashe da kuka tana jin kamar kanta zai fashe dan abinda ta sha din bai gama sakinta ba, ita ta rasa yaya zata yi da ranta
Rabonta da fita daga falon gidansu ta je farfajiyar gidan nan tunda ta samu ta fita ta ganshi da rawani mahaifiyarta ta hannata fita, shin yaya Mama ke so ta yi da ranta ne? Ita bata ga amfanin wannan tsana da Mama ke yiwa wanda ta san ya gama gamawa da zuciyar yarta, koda yake ba wata damuwa kowa ya yi abinda ya ga dama ita abu daya ne ta sani zata hada kayanta ta kaura wajen Hajia, ta san Hajia ba zata koreta ba, matsalar su ita da Mamanta ne ba da su ba!, kuma ta tabata a cen zata samu ya dubeta dan walahi itace matar YUSUF!
"Easy Man easy, kana nufin yanzu zaka shiga dajin nan? Haba oga, ka bari su su shiga mana, me yasa zaka shiga saboda wannan casss din da bai shafe ka ba?" ISHAK ke fada cike da mamakin yadda YUSUF ya iya fitowa daga fada cikin normal shiga da rigar dogari a sama, har ya iya fitowa ya zo madaidaicin gidan da Bah ya taba bashi as girft a lokacin da ya ciyo gasar harda tun yana da shekara goma sha biyar, gidan na nan a da haya ake masa daga baya ya bar gidan ana kular masa da shi yana kwana a ciki in kwana ya kama shi a garin
Da mai gadin suka gaisa ya shigo ya samu dakarun aminansa masu tsaron gidansa na jeji da manyan mashin din nan na maza na shiga jeji da abun kai da bindiga da dai duk wani abin da ya dace ace an shirya, a ciki kuwa ISHAK na ciki dama dan a nan ya sauka yanzu kuma ai shi zaman garin abokinsa ya kama shi, bai yi tsamanin zuwan shi ba sai ganninsa ya shi ya shigo yana cire rigar jikin nasa ya haura sama ya shige wanka, yana saukowa ya sauko da wani dogon wando baki sidik da riga mai hannaye kannanu wace ta ba damatsunnan hannayensa damar bayana gudum gudum da su, ya sauko yana kiran Taj yana bashi damar shigowa
A nan ne ISHAK din ya gane inda suka nufa dan a lokacin ne YUSUF ya tambayi Taj ya tabata numbar ya santa? Domin a dazun numbar wanda ya yi kiran kawai ya ba Zaj yace a yi kiran layin a yi tracer a san inda suke, nan da sati Daya ya bashi, sai gashi Taj din yana fada masa wannan numbar ai ya santa farin sani ma kuwa, wasu yan jagaliya ne, yan kauyen dake kusa da garin da suka waye da shaye shaye, dan sunna shiga birni ne dan siyan kayan maye su dawo , shine yace to kuwa a yau zasu same su su zanta dan Mah ta kwontar da hankalinta a kan rigimar ฦatuwar y'ar nan da ta dasawa wai ko *BABY* ko me? Abu kamar a yi amai dan sam bai hauta ba gaskiya
Bindigar da ya daura a damtsen hannunsa ya gyara da kyau ya wurgawa Ishak wayar hannunsa ya masa murmushi ya ce" Ka dan zauna min ina zuwa, in aka ji na fita daga bakinka ne man hakan ba zai birgeni ba ka ji?"
Daga haka ya yi ficewarsa ya bar ISHAK tsaye baki bude ya rasa tudun dafawa
๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค๐ค
Azl 24
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE
๐๐ผ Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching๐๐ปโโ๏ธ๐บ๐ .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*
๐๐ผ Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu ๐๐ผ๐๐ผmusamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)
Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a