Showing 60001 words to 63000 words out of 188741 words

Chapter 21 - AZAL HAUSA NOVEL

sajida   

12 Jan 2025

9826

ana salama da rakadi na sanarwar Hajia ke tafe

Har ga Allah sai da gaban Mah ya fadi, da sauri ta ware mayafin RAUDA da ta dan rankaya shi cen saman kanta ta yada mata shi sosai a saman kanta har ya rufe gashin kan nata sosai sannan ta masu alamar tana zuwa

Ta kamo hanya zata tafi falon ta ja ta tsaya saboda gannin kujerar Hajia na nufowa wajen table din tana bin kowa da kallo, bayanta kuwa tamkar jela matan Bah ne kowace yannayinta na nuni da kamewa da kula dan kar su aikata wani laifin

Ja ta yi ta tsaya ta shiga bin kowa da kallo, a lokacin ne Salima ta kamo hannun RAUDA suka fito sosai suka duka sunna gaishe da Hajia wace ke bin kowa da kallo ciki harda RAUDA

Hajia bata amsa ba, tana kallon kowa ne daya bayan daya sannan ta budi baki ta ce" Wadinnan fa? Ban sansu ba, da wannan"

Hajia mahaifiyar Salima ce ta ce" Bakin Andiya ne "

"Andiya?" Hajia baba ta maimaita tana kallonta da mamaki, ba komai ya sa ta jin mamaki ba sai gannin Hajia na fadin sunnan uwar Malik haka kai tsayen nan, ba maganar kishiyarta ko abokiyar gabarta, koda da cikinta ta haife ta an zo wajen da zata dan daidaita wasu abubuwan, ita bata ce su shirya ko su yiwa mahaifiyar YUSUF biyayya ba, No, abinda take so daya ne jal, a kiyaye girman sarautar kasarta, dan a kan wannan tana iya batawa da kowa a duniyar nan!

Mah ce ta budi baki a nutse ta ce" Eh bakina ne, su ukun nan ya'yan yan uwana ne, ita kuma wannan y'ata ce da nake riko"

Y'ata ce da nake riko ya saka daga Hajia baba har sauran zubawa Mah ido, ciki harda Rauda wace ta sake jin wani iri a kan Mah har ta ji wani abu ya tsirga mata zuciya mai kama da rauni da jin karfi irin na soyaya na son sukar maka zuciya

Abinda ke bakin Hajia ta hadiye bata yi ba a gaban mutanen, sai dai dayan bata hadiye ba, da kula sosai da kamewa ta ce" Ba damuwa, ama Wadinnan su ringa rufe jikinsu sosai, kuma su kiyaye kwaramniya idan Malik na nan, kafin a ware bangarensa daga naku!"

Tana gama fada ta juyar da kujerar tana dannata ta ci gaba da fadin" A irin wannan lokacin ko me kuke yi, daga ku har yayanku ya kamata Ku bar shi, ku yi jiran fitowarsa, idan ya fito gaisar da shi kadai zaku yi dan ba lokacin ya hadu da wani abin bacin rai daga gare ku bane, in ya tafi sai ku yi kai kawon ku kafin a gama ware masa nasa bangaren?"

Tana tafe a hankali ne da keken sunna biye da ita , Hajia na amsawa da in sha Allah, Mah ta yi shiru, da aunty amarya

Sai da suka nufo sashensa shi da mahaifinsa Hajia baba ta yi shiru ta dakata ta masu alamun a bude mata wajen Bah

Bude mata Hajia karama ta yi suka shiga ta karasa wajen da Bah ke kwonce

Ido ta zuba masa zuciyarta na neman tsinkewa
Da kyar ta danne abinda yake zuciyarta a kan danta ta yi masa addu'a sosai ta juyo da keken suka fito, dan ba zata tambayesu jikinsa ba domin dukkan abinda yake ciki ta sani a wajen likitansa da Mah

Da suka karaso kofar dakin YUSUF dakatawa ta yi ta dubi Mah ta ce" Ki shiga ki tashe shi, dan na san yana barci, dan Allah ki masa a hankali kar ki bata masa rai, ki rarashe shi ya yarda ya yi wanka sai mu shigo da Sarkin nadi a shirya shi"

Mah ta gyada kai a ranta tana ayana' Hajia da YUSUF kennan"

Har zata shiga Hajia ta sake jaddada mata ta bi shi a hankali, hakan ya sake riƙe wuyan matan Bah
Cen dama sun san soyayar da Hajia ke yiwa YUSUF daban ce da sauran duk wani jikanta, kuma sun sani sarai duk zafin Hajia tana shayin YUSUF , gashi yanzu ya zo wajen da duk iya shegen da ya shuka ba za'a zage shi ba ko a daga masa murya uwa uba a masa kallon banza? Ya Allah su kam haka zasu zo a banza su koma a banza kennan? Sunna ji sunna kallo yau matar da Hajia ta fi taana cikin ahali ce take yiwa magana da sanyin murya? Lalle akoy aiki ja gabansu

Mah na shiga da salama ta same shi kwonce saman gadonsa ya luluba da bargo , ac kuwa ya kure sanyinsa sai barci yake yi kamar ba shi aiki ke gabansa ba

Dakatawa ta yi daga nesa ta maimaita salamarta kamar sau biyu , ya yi shiru da nanauyan sauke numfashi zuwa saukakake alamun ya farka ama ya ki tashi

Mah ta ce" Ai sai ka tashi malam, kai YUSUF barci ka samu yi kennan? To tashi kakarka na kofa tsaye kuma gaba dayanmu ta tiso mu ka san ba zamu zauna ba sai ta ga ka fito ko?"

Idannuwa ya bude da suka masa nauyi yana tunanin me kuma tsohuwar nan ke nema da shi? Mah ta ce" Ba zaka tashi bane?"

Kin motsawa ya yi, dan yannayinsa ba abin kallon mahaifiya bane, hasalima sai ya sake luluba da bargon nan sosai muryarsa da amo irin na ingarman namiji sannan a shake na mai barci ya furta" Mah, zan tashi, ina zuwa , to ama me zan mata ita wancen din?"

Mah ta yi murmushi, lalle Yusuf yana neman fitina,
Ta juya dan ta bashi fili ta ce" Uwar tawa ce wancen din? Zaka fada ne YUSUF, ka tashi ka yi wanka za'a shigo a kimtsaka ne, saura na ji wata gardama Allah ma kuwa in dandali bakin mutun"

Shiru ya yi idannuwansa da launin ja na abin barci da guguwar da yake farkawa da ita a kulun na ALLAH
Sai da ya ji Mah ta rufe kofar ya sauke ajiyar zuciya ya sauko daga gadon yana jin takaicin Hajia, dan shi itace abar su gwara ba kowa ba

Wankan ya shige, wankan da ya dauki lokaci a ciki sosai domin sai da ya gama dukkan wasu uzurinsa sannan ya fito jikinsa da digo digon ruwa ya daura tawul daya a kugunsa yana rike da karami yana dan goge ruwan kansa ya karasa wajen kofar ya bude ya leka kansa ɗan ya ga a inda yai ga Mah , idannuwansa suka sauka a kan su su hudu, Hajia a saman kekenta , matan Bah a tsaitsaye babu wace ta isa ta koma ko ta zauna

Dan kura masu ido ya yi, gannin du sun sada kai banda Mah da ta kawar da kanta gefe , sai Hajia wace take kallon kofar ta ce" Barka da safia Malik, na tabo Sarkin nadin ne ko ba yanzu ba?"

Harara harara mai kama da jin haushi ya dan sauke mata, yana ayana' tana abu kamar wace nake da zabi salon nadan kiya ta hadani da uwata'

A bayane kuwa sai ya juya ya bar kofar a bude ya komawarsa cikiya shiga saka abinda ya danganci gajeran wando da riga ta ciki da su turaruka sannan ya dauki wayarsa ya shiga amsawa ISHAK tare da bashi damar zuwa fadar da wasu takardunsa muhinmai da suturunsa tare da litafin zanensa, wanda a ciki yake zana duk wani abin da ya danganci gini

Hajia ta yiwa Mah alamun ta fara shiga, sannan ta dubi sauran ta ce" Ku je falo har a gama sai na maku magana"

Da wani bakin cikin hakan suka bar wajen, Hajia ta saka wayarta ta sanarwa Sarkin nadi ya karaso, sannan ta tsaya har ya shigo ya karaso dauke da wata akwati mai shegen kyau mai ruwan maroon

Gaba ta yi ya bita har suka shiga falon YUSUF da salama a bakinsu su duka

Sunna shigowa Sarkin nadi ya duka har kasa kansa a kasa ya shiga mikawa YUSUF gaisuwa, dan a tsaye yake da tawul baba a kugunsa da riga fara yana ta faman dannar waya yana barin sakon msg wa tarin mutanen da suke da daraja sosai a duniyarsa har suke ta rokon son ganninsa da yi masa fatan alkhairi

Ido ya dan zubawa Sarkin nadi, sai kuma ya girgiza kai kawai ya dana kira ya amsawa ISHAK sannan ya katse ya juyo yana kallon Hajia wace ke masa murmushi tana kallonsa dan so take yi su yi zaman lafiya bata zo da rigima ba

Kai ya dauke yana sakar mata hararar kasa kasa, hakan ya sa Mah zarro masa ido da idannuwanta ta masa alamun ya gaisar da Hajiar, hakan ya sa ya karasa yana miko mata hannu ya ce" Cava?"

Murmushi Hajia ta sauke ta kama hannunsa tana kallonsa ta ce" Malik, ka ce zaka kai Ni asibiti baka kai Ni ba, kuma madarata ta kai gangara, sannan ka ga gadon nan ashe ya min tsayi sosai? Bana son sa Ni dai a min marar tsayi" duka maganar nan ta yi su lokaci guda dan burinta ta ga ya sake sakewa, ta san du rikicin da zasu yi da zarar ta yi irin haka yakan sasaubto har ya rarasheta

Kafarta ya zubawa ido, a hankali ya saka hannunsa ya dan bude zannin wajen ciwon ya saka hannunsa yana kallo ya dago muryarsa cen ciki ya ce" Ciwo take maki ne?"

Hajia ta dan gyada kai, hakan ya sa ya sauke ajiyar zuciya ciki ciki ya ce" To ki yi hakuri ai haka karaya take, an kusa kunceta kin ji?"

A ranta dadi take ji ta yi sharar fage dan yi doguwar fira da shi, a bayane kuwa ta amsa shi sannan ta sanar masa Sarkin nadi ne gayanan ya zo dan su fara lesson na nadi sannan ya masa nadin yau ya tafi

Duban Sarkin nadin ya yi ya mika masa hannu da nufin su gaisa sai ya ga ya sake dukawa yana neman fasa masa kunne da kirari

Gaban goshinsa ya dafe ya je bayan kujerar ta ya shiga Turawa har kusan gadonsa sannan ya mikkar da abin kujerar ya mikar mata da kaffafuwanta ya zauna bakin Bed yana gannin yadda mamansa ke nutse , bata da sakewa sosai idan Hajia na waje, ya maido dubansa wajen Hajiar ya ce" Hala kulun sai na je na wunin nan a fada? Tun safe sai dare?"

Hajia ta girgiza kai tana kallonsa ta ce" A'a, a yanzu zaka samu hutu fiye da kulun, zaka fita fada ne idan ka yi ra'ayi, ko in kana son wanzar da shara'a kai da kanka, fitarka fada ba kulun bane in ba baban abu da ya zamo dole kaine zaka tsawatarwa abin, ko karshen wata lokacin albashi dai da sauransu, kana da hutu sosai fa , shine nace wani bangaren kake so a gyara maka muhallin zamanka da iyalinka idan Allah ya nuna mana?"
Bai ce mata komai yanzu kai tsaye ba, mikewa ya yi ya amshi tufafin da Mah ta fitar masa ya shige ciki

Bayan ya shige din Hajia ta kalli Mah, dan a lokacin da aka bada tufafin Sarkin Nadi fita ya yi daga bakin kofar dakin ya dakata
Hajia ta ce" Wannan yarinyar tun yaushe kike rikonta?, ina iyayenta suke ne?"

Mah ta dubi Hajia, sai ta sada kai a tausashe ba da wani rawar murya ba ta ce" Marainiya ce, iyayenta sun rasu, ta dan kwana biyu a hannuna "

Hajia ta kalleta da mamaki ta ce" Shine ba'a taba sanar min da maganar ba?, dan ban isa ba?, bayan wannan ki sani a yanzu lokaci ne da zaki tashinma kanki ki kuma san ciwon kanki, dan Ni tunda nake ban taba ganin yan uwanki sun rabeki ba, yau shine harda barin ƴaƴansu sunna yawo da wata irin shiga a falo? Ki san abinda kike ciki dan a yanzu babu wanda ba zai rabe ki ba saboda daukakar nan!"

Mah ta yi murmushi bata ce komai ba, a ranta kuwa ayanawa take yi' Hajia, Ni ai ba mahaukaciya bace, kuma ina gannin zuwa yanzu idan ban biyawa wani karatun mecece duniya ba da wahala wani ya biya min, Allah dai shi kyauta kawai'

Shi da kansa da ya saka wannan tufafi ya jima yana kallon madubi kafin ya dauke kansa ya sake daukan turarensa mai tsadar gaske ya bi jikinsa sosai da shi sannan ya juya ya fito da hular a hannunsa da kuma macaji dan sumar kansa bai cajeta ba da ya fito a wanka

Da tatausar murya Hajia ta sanarwa mai nadin ya shigo ya bude computer hannunsa ya ringa hasko masa kalolin nadi har sai da aka tsaya kan wanda ya ji a ransa tabas ya masa ya bada damar a yi masa shi

Cikin nutsuwa yake naɗa masa yana masa bayani har ya gama ya dako madubinsa ya haska masa nadin tun daga baya har gaba bayan ya gyara masa rigar da takalmin da ya saka kafa ciki da Safa

Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Mah dake kallonsa da murmushi

A sanyaye ya lumshe mata ido wanda ke nuni da zuwa yanzu kam ya fara zubar da du wani makamin yaki, dan shi da kansa da ya kalli hoton nan a madubi abinda ya karanta ba YUSUF din da bane ke zaune, wannan din wani Yusuf din ne wanda Allah ya yi wanzuwarsa a cikin jikinsa..............

Daga nan ya mike Mah ta ci gaba da masa barin turare tana masa addu'a a cen kasan zuciyarta, shi dinma yana adu'ar ne, Hajia kuwa Tata a bayane take har Mah ta gama ta dauki alkhyabarsa ta ɗora masa , ita da kanta sai da zuciyarta ta ringa tsintsinkewa, saima da Sarkin Nadi ya kai kasa kansa a kas ya shiga zuba wani irin kirari mai tayar da tsigar jiki har sai da YUSUF ya masa alamun ya bari hakanan sannan ya mike ya je ya bude kofar ya rike yana fadin" Takawarka lafiya saraki, Takawarka lafiya hamshaki, Takawarka lafiya makaranci, Takawarka lafiya uban talakawa, tafiya salama zama salama mai jinnin Bello Abubakar, talakawa na gaisheka, masu kudi na gaishe ka, sarakai sun kawo gaisuwa, kai ne mai zamani mai tafe da karfin ikon Allah, makiyan ka fadawanka suke MALIK;, ku duka ga MALIK....'

Irin yadda yake jan MALIK din ya hanna da yawa dukar da kawunansu dan zumudin da kunnayensu ke masu da idannuwansu na son gannin MALIK din a yau da ya kwana ya tashi matsayin Sarki, ba nadin ba zatar da aka masa ta jiya ba, bale kannensa dake falon nan da bakin Mah , iyayensu sun dukar da kawunansu ne dan basa son ganninsa koda wasa

Tsayuwa ya yi idannuwansa suka shige cikin na Salima, wace hawaye suka wanke mata fuska, jikinta har tsuma yake na shauki da farin ciki, haƙoranta a fili muryarta har kamar ba Tata ba ta furta" BAH, URS MALIK!"

A hankali ya lumshe idannuwansa jin wani abu daban wanda ya zarce wanda yake ji a da a kan yan uwansa, a yanzu abinda ya ji wani mai girman da yake ji kamar ubansu yake, ko dan SALIMA ya sani a soyayar da take masa na yayanta ba karya ciki ta kire shi tashi daya da BAH ne?, a tausashe ya sakar mata murmushi bayan ya sake bude idannuwansa daga lumshewar da ya yi, sannan ya ringa daga masu hannu na gaisuwar da suke masa daga su har iyayensu

Juyawa ya yi bai tsaya ya tantance waye da waye a wajen ba ya tafi tare da tarin jama'ar dake jiransa da Hajia a tsakiyarsu har ya zauna sannan ta tafi nata bangaren ta ci gaba da zaman makoki

A cen kuwa bayan tafiyarsu iyayen nasu kowace shigewa ta yi giki, hakan ya sa Mah ta yi tsaye kan yan matan su zuzuba abincin kowa ya karya sannan kowa ya kama yan ayyukan gidan, har tana tsokanarsu cewar yau ba za'a kirayi mai aiki ko daya ba, masha ALLAH yan mata birjik haka, yau har Auta sai ta yi guga
Da wannan suka tafi wajen abincin suka shiga zubawa, Rauda ta kasa hakuri gannin Salima ta kasa daina kuka tana kallonta ta ce" Kukan me kike yi wai?"

Salima ta kalli RAUDA, dan bata yi tunanin zata wani damu da wani abinda ya shafi wani

Dan murmushi ta yi ta ce" Baku ga yayanmu ba? Baki ji kamar zaki summa ba da ya fito?"

RAUDA ta dan zarro ido tana kallonta, ta girgiza kai
Salima za kalleta da mamaki ta ce" Wai Allah?, baki ji kirjinki na bugawa ba?"

RAUDA ta sake girgiza kai harda dan dafe haba, dan ita gaskiya bata kalle shi bama bale har ta wani ji ko zata summa ko me?

Gaba ta yi da plate din dake hannunta na Mah, Salima ta bita da kallo baki bude har ta bacewa ganninta, Salima ta gyada kai kasa kasa tana zuba na su Musulima ta ce" Aman a wajen nan waye bai zubar da hawaye ba fisabililahi? Kai RAUDAH".........








😂😂😂😂🤲🏼🤲🏼🤲🏼🤲🏼🤲🏼
Azl 22
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*

Bismillahi rahamanin rahim

Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*

💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)

Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login