Showing 18001 words to 21000 words out of 188741 words

Chapter 7 - AZAL HAUSA NOVEL

sajida   

12 Jan 2025

9865

kan lokaci ai har ya manta, dan haka ya sada kai yana cike da jin da kunya

Ajiyar zuciya liman din ya sauke a tausashe ya ce" Mu je ka gabatar da sallah, itace abinda take gaba da komai a yanzu, bismillah"

Kamar kanninsu ko dan gidansu suka saka shi gaba, ba da niyar tozarci ba, a'a da niyar taimakonsa, dan kuwa kasancewarsa mutum dake rayuwa cikin halin maye bai Hanna masa girmama duk wani mutumen Anguwar ba, datijawan Anguwar na binsa da Adu'ar shiriya, da kuma fatan Allah ya shiryi matarsa, dan babu wanda bai san wacece ita ba, dabi'unta a bayyane suke ba a boye ba, irin yadda take yiwa Rauda kuwa da kanninta ya zamo kowa na yi mata wani kallo, gashi dai kiri kiri tana son mayar da yarinyar kamar wata mai zaman kanta, a koda yaushe cikin zance da masu motoci a kofar gida, a koda yaushe tana karbar baki a kofar gida

Makocinsa na hannun dama ne da liman din suka zauna sai da ya gabatar da sallar asubahi har karfe bakwai na safiya ta gota sannan suka zauna tare da shi, cikin nutsuwa da kula suka ringa yi masa nasiha da nuna masa irin illar wannan rayuwar, abinda ya riga da ya sani, ya kasa zaunawa ya yiwa kansa fada ne saboda bashi da mai tunatar da shi

A tausashe Liman ya ce" 300Babu yadda rayuwa bata zuwarwa bawa, kuma komai girman laifinka idan ka tuba Allah mai karbar tuban bawansa ne, babu abu mafi hatsari irin maye, maye bashi da anfani Malan Umar, mai yin maye bashi da daraja kuma bai san abinda yake yi ba , kana da ya'ya yan mata, ga namiji masu bukatar taimakonka, dan Allah ka ceci kanka ka daina wannan halaya, ka rufawa kanka asiri kar ka samu matsala a wajen aikinka, domin rayuwa yau kana gannin idan mutun bashi da aikin yi damuwa ce, gashi kai din nan uba ne kuma Magidanci ne malam Umar"

Makocinsa Elhaji ashiru, mutun ne mai abin hannunsa daidai gwargwado kuma mai kyauta da taimako, ya jima yana da burin gannin sun samu kusanci da makocin nasa dake gaishe shi idan ya ganshi ko a ina ne Allah bai yi ba sai yau, ya Dube shi da kula sosai ya ce" Kowani bawa da irin tasa jarabawar makan Umar, kuma kowa lalube yake yi , babu abin tsoratarwa da wannan duniyar sai irin yadda babu wanda ya san ranar mutuwarsa, idanma babu mutuwa malam Umar Akoy tsufa wanda ke yiwa mutuwa fadan garaje gareta ta bar bawa da shi ta gani, malam Umar duniyar nan mutun ya yiwa kansa abin kirkima yaya ya kareta bale yana wasa da damar da Allah ya bashi? Bama kamar sallah da kiyaye hakokin ubangiji, ga nauyi a wuyanka a rataye, kaine uba kuma uwar ya'yan nan, ka yi kokari ka fi karfin zuciyarka ka fuskanci rayuwarka ka daidaita abinda ya dace ka daidaita, idan kana bukatar taimako ko na menene ka same ni in sha Allah Ni zan kawo dukkan talafin da ya dace, kana da halaya masu kyau, domin kaf Anguwar nan babu wanda zai ce ga abokin gabarka ko wani abin ya haɗaka da wani saboda dukiya ko ya'ya, hakan kuwa baban ALKHAIRI ne shi yasa yanzu na zo shiga gidana daga masallaci na ringa jin hayaniyar nan na kasa hakura na tabo liman muka yi jiranka, ba dan mun saka maka ido a shige da ficen gidanka bane, a'a, damuwa muka yi da dan uwanmu musulmi muka kasa hakura sai mun sauke nauyin hakin makotaka "

Sosai uncle din Rauda ya karra jin zuciyarsa ta yi sanyi, hakan ya sa shima ya gyara zamansa yana sauraron nasiharsu da kuma tunatarwa a kan gobe kiyama da kiyamarsa, ya shiga halin tunanin idan mai kasancewa ta same shi a irin wannan halin? Me zai cewa ubangijinsa? Tsoro ya kama shi ainun hakan ya sa ya zauna tare da su sunna ta zamtawa


A cikin gida bai san ya fita ya balowa RAUDA gagarumin rikici bane

A lokacin da ya fita Mama ta gama kukanta ta mike ta nufi dakin su RAUDA ta bankada kasarin dake kofar dakin ta shiga rai bace ta mika mata hannu ta ce" Bani!"

Gaban Rauda ya yanke ya fadi, dama ta san a rina wai an ari zanin mahaukaciya

A hankali bayan ta sake riƙe hannun kanninta dake ta rawa ta ce" Mama jiyan dare na yi gudun kar ya min shi yasa na dawo gida dan kar na yi dare ki kasa barci ba'a rufe gida ba"

Sai da maman ta dan kankance ido tana kallonta kafin ta shigo gaba dayanta ta ja yar kujerar tayani tsegumin da ita ta sanyota dakin ta zauna tana kallon Rauda ta ce" Ama ban taba gannin yar bakin ciki, marar mutunci irinki ba, ban taba gannin munafuka algunguma irinki ba, dan ubanki na taba zaman jiranki idan kika fita ne? Nan ko zance kike yi sai ki kai karfe goma sha biyu na dare a waje kina yi na taba zaman jiranki ne? Ko saurareni da kyau na rantse Miki karya kike yi, kin ga a yau idan har baki bani abin kirki ba sai na maku horon yinwa ta wata guda cir kuma sai kun bar min gidana , tunda kin san ba ubanku ke biyan haya ba, ke in banda raini da wulakanci da bakin ciki har nice zaki kawowa wannan maganar? Ai ba ubanki ya kawoni duniya ya tafi ya barni da wahala ba bale na zauna ina ciyar da gandamemiyar kamarki a banza ba, na fada maki kirarki ta ki nemo min kudi ce, ba ruwana da wa ta yaya! Matsalata kudi, idan kuwa tsiyar da iyayenki suka mutu cikinta zaki nuna min ba matsala, dama ke kin san har ki mutu ba zaki mallaki abin kanki ba, ama Ni WALAHI sai kin nemo min in ba haka ba......."

Da karfi ta janyo Abdul Hakim ta rike hannayensa ta kashe shi da marin da ya saka RAUDA saurin mikewa ta janye shi jikinta na rawa ta kafe fuskar Mama da kallo Maman kuwa ta mike tana kallonta itama ta ce" Dukana zaki yi yar mararsa mutunci? To WALAHI na fada maki idan baki nemo min kudi ba sai na halaka wannan kafin na halaka uban baki kema na halaka ki, ba kin fada min saboda su nake taka ko ba? Zan ci gaba da taka ki ko bayan na halaka su in dai kika yarda kika yi wasa da umarnina y'ar matsiyata mai shegun idannu kawai, ki miko min shi ya je ya kai surfen masara tunda ba ubana dake kabari zan taso ya kai ba!"

A hankali RAUDA ta sake tare hannunta tana kallonta a tausashe da yannayin tsarin halitarta ta ce" Ki ba almajiri ya kai zan biya, ki bi Ni bashi zan kawo maki"

Dan tsura mata ido ta yi kafin ta juya ta fita tana sababi da aibata RAUDA, da yawan lokuta takan so ta kai hannunta jikin RAUDA sai dai tun ranar da RAUDA ta riki y'arta ta yi mata wani tsinanen duka dan ta ga Maman na zagin iyayen Rauda ana zama lafiya itama ta kalleta ta zageta ita kuma ta nuna mata bata da hankali Maman ta yi ta yi ta kwaceta ta gaza karshema da Raudar ta yi kukan kura ta hankade Maman da y'ar Tata sai da Maman ta fi wata tana zuwa ana murza mata bayanta dan ta baya ta je ta fada ta ji rauni sosai, shi yasa idan Raudar ta mike tana huci sai Maman ta ringa kiyaye abinda ke saurin sakata fita a hayacinta wato zagin iyayenta

Mama na fita Abdul Hakim ya rukunkume Rauda yana fashewa da kuka ya ce" Aunty tsoronta nake ji, kasheni zata yi"

Itama zuciyyarta ce ta karye ama ta ki nuna masa a hankali ta zaunar da shi ta zauna ta dora kansa saman cinyarta tana shafawa a tausashe ta ce" Dama Akoy wanda ya isa ya karar da kwanan wani in ba lokacin mutun ne ya yi ba? Haba boy din aunty, ka daina fadar haka ka ji? In sha Allah babu abinda zai sameka sai abinda Allah ya kadarta maka ka ji? Fada minda me zaka karya yau? Zaka je ka siyo ne ko na je na siyo maka? Yau zaka je makaranta kuwa an kanena?"

Ajiyar zuciya ya ringa saukewa a jejere da sauri ya gyada mata kai ya ce" aunty zan je, kin ga Malamin mu na islamiyya yace ko me aka yiwa bawa ya barwa Allah, sakayar Allah ta fi ta kowa, Allah zai saka masa ya saka shi a aljanna ama kuma yace bawa ya kasance mai yafiya, na yafewa Mama aunty kin ji?"

A hankali ta dauke hawayen gurbin idannuwanta ta lalubo kudin dake cikin rigar Mamanta ta mika masa dan idan bata saka kudi a nan ba tana kwonce za'a lalubeta a kwashe Abinda ta ajiye, gashi nauyinta da na Abdul Hakim a wuyanta yake, Mama na ikirarin hana masu abinci dama ba basu take yi ba ai
a tausashe ta ce" Maza karbi je siyo mana abinda ranka ke so bari in zuba maka ruwan wanka idan ka dawo ka yi sai mu je na kaika makarantar daga nan na kaika wajen inna kaka zaka je?"

Cike da farin ciki ya amsata kan zai je kafin ya mike ya tafi da gudu daga gidan danma kar ya hadu da Mama ko yayarsa su daki banza su kwace kudin

A hankali RAUDA ta karasa bayi ta yi wanka da brush ta fito ta daura alwallah ta shige ciki dan gabatar da sallar da aka sakata yin lati dan dole, inda yar gidan Mama ta bita da kallo a lokacin da ta shige daure da zani daurin kirji cinyoyinta du a fili da cen wajen wuyanta da hannayenta dai da kuma gashin kanta
Baki ta tabe kasa kasa ta ce" Du kyanki sai na auri mijin da ya fi ki in ji Mama, aikin banza kyan banza!"

Bayan ta gama sallah carbinta ke hannunta tana ta istigfari, a hankali a hankali ta fashe da kuka tana hade bayanta da jikin bangon dakinsu mai dauke da dati, dan a gidan idan Akoy wajen ajiye kowani tarkace dakinsu ne, duk yadda ta kai da gyaran dakin a banza ne tunda datin cikinsa ya ishe shi

A hankali take kukanta mai gunji da ratsa zuciya

Shin ina zata saka ranta ne?

Ina ake so ta kai kanta ne?

Dan ta hadu da maraici shine ta yi laifi?

Me ta yi da zafi?
Tana bakin kokarinta dan gannin ta faranta ran Mama, ama ba zata taba cin arzikin mutuntawa ba bale arzikin a dauketa tamkar y'a?
Me Mama take tunani ? Dama ita bata sakawa ranta zata yi aure ba a duniya saboda ba zata taba yin aure ta haihu ta mutu ta bar abinda ta haifa ya ga irin izinar da take gani na rayuwa ba, haka kuma bata taɓa sakawa ranta zata yi arziki ba, sai dai nacin da Mama ke mata na yau da kullum kan natawa cewar a duniya babu matsiyaci irinta dangin tsiya dan iyayenta da yan uwanta sun rasu a halin talauci wanda Allah ne ya halicce su haka Shikenan sai ya zama abin zagi? Idan ta samu zama irin wannan takan ji kamar zuciyyarta zata tsaya
Ita a zuciyarta babu gurin farin ciki
Babu gurin tunanin samun jin kai a duniya
Mutun biyu ke sakata cenza tunani lokuta da dama BARA'ATU da ABDUL HAKIM, ita Bara'atu ta riga ta san lagonta har tana sakata daria da murna, shi kuwa Abdul Hakim yana da uwa da uba a duniya da dangi ama irin rayuwar da yake fuskanta mahaifinsa ya ki bada shi wa dangin mamansa ya sa ta dauka itace duniyarsa, itace uwarsa, ubansa danginsa

Da sauri ta shiga share hawaye tana cire hijabinta ganninsa ya shigo da salama hannunsa dauke da bakar ledar da ya siyo kayan karin nasu sai farin ciki yake yi ya nemi waje ya zauna yana fadin" aunty harda kifin babale mai ayaba yau na siyo mana"

A dole ta kakalo murmushi tana gyara zama ta ce"iyeah bari na wasa hakorana Sarkin cin dadi ya samo mana kayan dadi"

Shima farin ciki ne ya mamaye zuciyarsa ya bude yana mika mata nata, da nasa sannan ya bata cenjinta

Murmushi ta yi ta rike cenjin a hannunta tana tunanin yau ko da isheta zuwa wannan gagarumar restaurant din mai sunna ABUSA? dan tana so ta yi sabon kamu ko ta samu masu nauyi, ama kuma ba zata yarda ta tsaya daga nan ba sai ta samu baki ko uku ne yau din dan ta dan samu kudin ta ba Mama ko a bar mata Abdul ya kwana cikin nutsuwar zuciya ba zagi bare hantara

Sunna gama cin abincin ta haɗa ledojin ta raka shi bakin bayi ta tsaya ya shiga wankan
Yana fitowa ta bashi brush dinsa ya wanke bakinsa sannan ta raka shi daki ta kuma tsaya ya saka kayansa na islamiyya domin yannayin kwakwaluwarsa kin daukansa suka yi a boko , dan yannayin na Abdul Hakim sama sama ne

Cikin nutsuwa suke Tahowa daga dakinsu zuwa falo tana rike da hannunsa yana magana kasa kasa

Murmushi ta yi kasa kasa ta ce"



Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA

🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶

*SAJIDA NIJAR*


*PAID BOOK*


_Bismillahir rahamanir-rahim._


*8*

*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*

*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
KARKU BARI A BAKU LABARI🥳



Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*




Murmushi ta yiwa maganar da ya yi, kasa kasa ta ce" Ba Abul bane bawa, Abdul ne, kuma kai bawan Allah ne ba na mutun ba boyboy"

Dan rabewa ya yi jikinta a lokacin da zasu fice sakamakon gannin Mama ta dosa falon
Itama dakatawa ta yi har maman ta shige sannan suka fita kusan sunna sauke ajiyar zuciya a tare

A Nutse suke tafiyar, tana rike da hannun Abdul har suka karaso kusan masalaci daidai inuwar su malam da su Liman

Kamar yadda ta saba gaishe su a mutunce ta duka ta gaishe su sannan suka yi gaba

Sun dan yi gaba kadan Muryar babansu ta saka su dakatawa suka juyo kusan a tare

Da dan mamaki saman fuskarta ganninsa sanye da farar jalabiya kuma yannayinsa na nunin wanka ya yi harda kanshin turare ta ce" Baba?"

Shima murmushi ya yi yana kawar da mamakinta, dan sarai ya karanci mamaki ne ya kamata ganninsa a Anguwa a irin wannan lokacin , a da idan suka yi fada da Mamansu ya koma gidan giya Kennan sai ya yi niya dan kansa ya huce zai dawo gidan

Da kula yace" Ina zaku je?"

Dan murmushi ta yi tana jin kamar kwallah na neman cika mata ido ta ce" Makaranta zan raka shi, daga nan na kai shi wajen inna ya masu kwana biyu in bai tada rigimar sai an kawo shi wajena ba"

Murmushi baban ya yi cike da jin tausayinsu dan ya san saboda sun yi rikicin ne zata matsa shi nesa da ita kar Mamansu ta dake shi, yana laluba aljihunsa ya ce" Bari na ga ko na alewa na baka ɗan gidan auntynsa"

A aljihunsa babu wani abun kirki ko kwondala babu dan bai yarda ya zauna da kudin da ya yi niyar yi mata siyayar kayan makarantarta a gudun kar matarsa ta sace kudin ,
Da yar kunya ya dubeta zai yi magana ta yi gagawar fadin" Baba munada cenji a nan fa, zan bashi ko Abdul din baba?"

Abdul ya gyada kai yana bangalar darkyar da ta wuce misali yana kallon baban nasa, shi dai ya san babansa ne ama ba wata shakuwa a tsakaninsu sai ta shinfidar fuska, to yaushema baban ya zauna bale har ya wani shaku da shi?

Umar sai ya ji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login