Showing 21001 words to 24000 words out of 188741 words
wani iri a zuciyarsa, yarinyar nan ba aikin fari take yi ba ba baki ba, ama kuma a wajenta ake amsar kudi, ya Allah ka sa Rauda bata wasa da mutuncinta duk rintsi
Kasa cewa komai ya yi sai jadada mata da ya yi yana wajen su liman , hakan ya saka mata farin ciki sosai a zuciyyarta suka tafi ita da kanninta a kafa har makaranta
A lokacin da ya shiga ya zauna suka gaisa da malam yana ta faman yi mata annuri ta dawo karkashin shuka ta zauna dan sai an tayar da su ta kai shi wajen inna ta koma gida, ta zauna ta shiga contact dinta a hankali tana dubawa da son ganin wanda ya dace ta sakawa Hi, wanda yake nacin son ganninta kuma ta san idan ya zo baya tafiya bai yi mata ALKHAIRI ba
A gaskiya ta irga mutane da yawan gaske, har sai da ta saki murmushi mai ciwo tana kallon cikin makarantar su Abdul a ranta ta ayana' Sai kace mai zaman kanta? Wannan ko mai sana'ar amsa a hannun maza ta biya masu bukatu ai sai haka, babu kalar wanda bani da shi Ni RAUDA ' ,
Sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta kore tunanin dan bata so ta dagawa kanta hankali a tunanin da ba zai fisheta ba
Mutun biyu ta iya tabowa saboda ba zata tabo sama da haka ba ta haɗa su a kofar gidan su a yi abinda aka taba yi, ta haɗa samari aka shiga fada Mama ta rufe mata gida a ranar sai gidan makota ta kwana Mama tace ba zata saka a zo a kwasheta a kaita police station ba!
Cikin ikon Allah biyun nan da ta zaba suka amsa gayatarta cikin dabara, domin babu wanda ta nuna da sanninta ta tabo shi, cikin yannayin kisar da ta koya dole dan ta kubutar da ranta ta iya yarda da son ganninta da suke yi da kyar, bayan ta shardanta masu tsakanin magariba zuwa isha'i da kuma bayan isha'i zuwa karfe takwas , dan daga nan ne zata je restaurant ta samu koda awa daya ne ta dawo gida , tunda Abdul baya nan bata da damuwar ta bar wani a gida bale ta dawo a gagauce, idan kuwa kwana zata yi a cen da wahala a gane bata kwana gida ba bale ya damu wani
Sai da aka sake su daga makarantar ta raka shi gidan inna, a hanya suka sayi yan fruits suka jewa innar da shi
Sosai inna take masa oyoyo tana dan goge masa yawun da yake dan zubarwa kadan ta rungume shi tana ta shiga RAUDA albarka tana fadin" Yau ya tuno Ni? Oh mijin Allah ya sa ka yarda koda kwana biyu ne ka min kar ka dora min rikicin aunty aunty"
RAUDA na kallonsa ta ce" Zai zauna Inna in sha Allah, ko Abdul din baba?"
Kai ya gyada ya shige dakan inna yana gigibo kayan wasansa da RAUDA ke kawowa ajiya nan in dai tana so ya mora, kaya masu yawan gaske dan da yawa ya wuce shekarun wasa da su ama ita idan ta gani sai ta kwaso ta kawo masa ta jibge, shi yasa a kulun inna dake matsayin kakarsa ta wajen uwa ke girmama Rauda da Binta da addu'a, ko mahaifiyarsa dake wata kasar tana aure a kulun idan ta samu halin yiwa Rauda alkhairi takan yi mata haka kuma tana Binta da addu'ar fatan alkhairi, dan ta mata komai da take kulawa da gudan jinninta
Da dabara RAUDA ta tafi , gudun kar ya ganta ya ce sai ya bita
Tana fitowa ta tari dan sahu ta masa kwatancen saloon din da take gyaran kai, wajen maman aisha
Tana zuwa ta tarda mutun biyu ne gabanta dan haka ta zauna ta shiga chatting tana gannin kiran Atu ta ki dagawa dan ta yi alkawarin sai ta yi sati biyu cir zata je gidanta ta mata fatan ALKHAIRI sannan zuwan ya zama sai da dalili domin ba zata taba ajiye kafa gidan aminiyar Tata ba, dan gudun abinda ke iya je ya dawo
Ana gamawa wace ke gabanta aka kama gashinta,
A lokacin da ake caje gashin kanta sosai na sha mamaki, ashe dunkulewar nan da ta masa ta dunkule ainahin yawansa da kyansa da tsayinsa
Wanke mata shi aka yi aka sakata cikin na'ura mai busarwa mai dumi sannan aka shiga gyara mata faratunnanta na hannayenta da na kafarta aka saka kafar cikin abin wankewa aka shiga wanke mata ita, dama bata da wani dati ama a haka aka wanke mata ita tassss har tana daukan santsi a takalmin da ta saka
Hannayenta kuwa cikin wata na'ura mai dumi aka saka su suka dauki dan lokaci aka ciro mata aka sake gyara faratunnan sannan aka shiga warware gashin ana tambayarta abinda take so a mata da gashin
Da dan murmushi ta ce" Maman A'isha kar ki masa komai daure min"
Maman aisha ta yi yar dariya ta ce" Dama na sani, shin yaushe zaki fara kitso ne da gyaran gashi a yi masa kaloli? Ni da inada ko rabin gashinki ne da an shiga uku
Murmushin dai ta yi ta bude bayan wayarta ta ciro kudinta ta bata ta mata Salama ta nufi gida a lokacin har yama ta yi sosai ana daf da kiraye kirayen magariba
Bata tsaya bata lokaci ba wanka ta shige
Tana fitowa ta daura alwallah ta shige dakinta ta kunna fitila da fanka ta rufe dakin
Sallah ta gabatar ta saka wata doguwar riga ta zumbula hijab ta fesa turare sosai ta dan murza lips a bakinta ta dauki wayarta ta amsa kiran da kusan na biyar Kennan ana mata shi ta sanar masa cewar gatanan zuwa ta mike ta fita
Bata wani jima a wajensa ba suka yi Salama ya zo mata da abinda suka yi magana ta waya dan ta sanar masa ne ba shi ta so kira ba sakonta take ta neman yadda za'a bata kafin ta kai kudin ɗinkin , cikin dabara dai ta yadda ba zai ce ta roke shi ba ta amso kudade ta dawo cikin gida tana ta tuna a lokacin da ya zo bata kudin sosai ya so shafar hannunta itace ta kiya saima da ta masa alkawarin zata neme shi yanzu bata so babanta ya dawo ya ganta a kofa ne ya yarda ya tafi da ta tabatar duk masifa sai ya yi wani abin ko shafata ko yace zai rungumeta koma sama da haka, dan abin yanzu ai kowa ya sani bani in baka ne soyayar in dai kwadayi ka saka a gaba
Na biyunma sai da suka so samun matsala da shi, dan shi a kulun dama sai ya zo mata da maganar aure, shi aurenta yake son yi, da kyar ta salame shi ta dawo gida ta ajiye kudin nan ta shiga kimtsawa
Cikin nutsuwa ta saka atampa riga da sket masu ruwan fari da ja da dan sirkin baki kadan, ta ciro takalminta mai dan tsayi kadan ta ajiye da jakarsa bakake sai dan yalolon mayafi baki mai shara shara sosai ta turare shi sannan ta sake kunce gashinta a hankali ta caje shi ta daure da dan ribom siriri baki sidik ta dauki jambakinta mai ruwan lebenta ta shafa ta ɗora masa man lebe kadan ta dauki wayarta baba ta saka a yar jakar nan da kudaden nan kaf ciki, ta sake yiwa kanta wankan turare sannan ta dauki wayarta karama ta yiwa mai adaidaitan dake kaita Anguwa da dare flashing ta fito a Nutse ta nufo falon tana jin Mama na yiwa y'arta fadan wai ko nata da saurayi ko mene?
A hankali ta ce"Mama na tafi"
Da sauri Maman ta kalleta, sai kuma ta dan tabe baki kadan ta ce" Sai kin dawo, kin dai san tarin bashin dake kanki, ki tabbatar da fitar ta maki anfani in ba haka ba WALAHI ina nan ina jiranki!"
Dan murmushi ta yi ta fice ba tare da tace komai ba, Maman kuwa ta ja tsaki ta ce" yar gidan matsiyata sai dan banzan kyau uwa ita ke karra kera kanta kulun a daki, ki je ko nemo min dan kudin nan baki na zai zamo na banza ba ina ji ina gani!"
Y'arta dake gefe ta tabe baki ta ce" Mama wai me yasa ita RAUDA kowama sonta yake yi ama Ni kina ta bani maganin farin jinni babu mai so na ko dai ba zan yi aure bane ni?"
Bakin uwar ta bige mata tana fadin" Ke dilla tashi daga nan dan ubanki ki yi wanka, tun jiya nake bin kanki ki yi wanka ki wanke wandon nan na jikinki wari yake yi daga kin zo kan mutun ama kina min kunnen kashi, ke idanma an nemo na sai kin gyara ba zai kama ki? Ban san wannan tsinaniyar daudar a inda kika samota ba, gashi ki dan yi kama da Umaru baki yi ba kin kwaso kankanki baki bar komai na babanmu ba ke mace sai dati da tsami, ki yi wanka ki zo ki yi kwaliya ki dan zaga baya gidan su kawarki ki dawo ko a dace da wani rantsatsen ya dauke min na maki gadon yar gata"
Tana tura baki ta cika buta daya da sabulu ta yi bayin kasa kasa tana fadin" WALAHI na zan yi wanka ba, shekaran jiya fa na yi, wani abinma ai barnar ruwa ne, wandona kuwa bashi da dati ko kadan abinda ba fitsarin kwonce nake yi ba bale ace na masa fitsari, wanke jikina zan na shafa turaren RAUDA da kayan kwaliyarta na ari kayanta na je na zo kafin ta dawo, ba dole a ki so na ba kin haifoni da muni!"...........
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*SAJIDA NIJAR*
*PAID BOOK*
_Bismillahir rahamanir-rahim._
*9*
*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*
*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*
Daga nesa da watsetsiyar restaurant din ta saka ya ajiyeta sannan ta shaida masa duk rintsi kar ya yi nisa zata tabo shi
A Nutse take jefa kafarta cikin takun salon tafiyarta mai tsarin gaske da ɗaukan hankali ta nufi hanyar shiga ta asalin Babar hanyar tana mamakin yau wajen babu tarin tarkacen yan mata da samari da cikar abubuwan hawa kala kala
Mai tsaron kofar ne ya dakatar da ita yana fadin" Yau Akoy baki a ciki ba'a shiga ko tare kike da ita ISHAK?"
A ranta ta ayyana ' Ku ga sakarci, ai yau ko wa ya siye wajen nan tunda na fito sai na shiga'
A bayyane kuwa sai ta yi dan murmushi tana dubansa ido cikin ido ta ce" Tare muke mana, bai ce maka zan bane?"
Gaba daya yannayin Rauda ya saka shi gaza yi mata gardama, irin sansanyan kanshin da take fitarwa da yannayin shigarta kuwa ya tabbatar masa tabas ita din kalar tafiyar manyan dake cikin wajen nan ce, dan haka ya kauce mata ba tare da ya ja ta wata maganar ba ya bata damar shiga ko tikitin shigar bata cira ba dan yau ai ba zancen ka ciri tikiti restaurant baki daya yau babu mai cin abincinsa sai wa'inda ke ciki sun tafi, dan yan oder kadai aka amshi odarsu, suma an fada masu sai fa daga bakin karfe goma sha daya zasu fara zuwa amsar abincinsu, duka kaf ma'aikatan wajen yau sun dukufa ne dan biyan buƙatar BIYA MARADI da bakonsa.
Bata ji Dar ko daya ba a zuciyarta har sai da ta shiga filin da ake cin abincin idannuwanta suka sauka saman manyan kujerun dake ajiye da asalin VIP da mutanen dake zaune, gashi su dinma hanyar shigowar suke kallo, hankalinsu a nan wajen yake sunna fira ne kadan kadan , inda muryoyi biyu suka fi tashi ta ISHAK sai ta bakon Yusuf wanda ya masa ja gabar kawo masa wasu motoci tun daga Chaina a jirgi, motocin ne da yawan gaske kuma manyan motoci ba kannanu shi yasa abokinsa wanda suke harkar motar tare kampanin kerata ya ga dole shi zai kawo motocin ya biyo su a baban jirgin da ya sauka yau din a kasar ta Nijar, to tunda ya zo bai ci abinci ba, yace babu irin abincinsu shine Yusuf din ya kawo shi nan ya ci su wuce, domin daga nan cen park dinsa zasu wuce sai kuma ya sayi tiket komawa dan ba zama ya zo yi ba shima
Bata san me yasa ba, bata taɓa tsintar tsigar jikinta da mikewa ko alamun jin tsoron shiga cikin duban mazama ba wai kwaya ukun cen da dake zaune ba sai yau, a hankali ta lumshe idannuwanta sakamakon jin Muryar wannan matar mai dauke da tufafin wajen tana fadin" Bismillah ki karaso"
A hankali ta dan hadiye yawu gannin kusan su Dukansu dake kallon wani abin da wannan mai kama da kwai dan haske wanda du jan dan Chainar nan baya ɗaukan hankali kamar nasa yannayin fatar , yana sanye da wandon da za'a iya kira 3/4 damatsunnan kaffafuwansa a wani irin cike ga gashi kwonce jikinsu luflufluf , sai riga mai ruwan baki sidik karamar riga domin ta lafe a jikinsa ta bayyanar da yannayin jikinsa irin na mai abdo, harda wata sarka a wuyansa wace tashin farko ta ayanawa ranta cewa Christa ne suka dago jin an ce da mace ta karaso, ISHAK yana tunanin ko Nafisar ce ta shigo bayan ya fada mata idan aka bata damar shigowa ta tsaya daga baya ta yi kiransa ya taso bosss na tare da bako kar ta zo inda suke ta zo? Sai dai kafin ya idasa tunanin ya samu kansa da zubawa wace ke tsaye ido itama tana masu wani kallon da zuciyarsa ta shiga dokawa da gudu gudu
Dawowar babar masu kula da bakin hannunta rike da wata kwalba da kuma wani kofi na kwalba fari kal mai dan tsayi ta ga Rauda a tsaye bata karasa ba ta samu kanta da tsayawar itama ta kalli Rauda ta juya ta kalli wajen su YUSUF ta karasa tana fadin" SIR ba bakuwarka bace wannan?"
A hankali ya dauke dubansa tun kafetan da ya yi da ido ya kalli kwalbar jus din dake hannun matar zai yi magana Ishak ya rigaye shi yana fadin" Bakuwarsa kuma?, ba Bakuwarsa bace!"
"Bakuwarsa ce" RAUDA ta fada a hankali a lokacin da ta karasa wajen kujerun da suke ta zauna a warariyar dayar dake facing dinsu tana hadiye yawun da ya kafe mata a baki dan ta samu kwarin gwuiwa "
A karro na biyu ya sake zuba mata ido, ita kuma matar gannin bai bada umarnin komai ba sai kawai ta budewa Rauda kwalbar nan da abin budewa ta ajiye mata bata cire marfin ba da kofin a daf da ita saman wani dan table din ta juya dan kawo mata takardar abinda suke sarrafawa ta zaba
Kirjinta ne ya yi wata irin bugawa sakamakon idannuwanta da suka shiga cikin nasa saboda tun dazun basarwa take ta yi danma kar ta yi ido hudu da wani ya koreta
" *A salame su, bana son takura!, mu je mana bana son shirme zaka tsaya kana magana da yarinya ka salameta idan kana salamarta bana son takura* " magangannun da ya fada a shekaran jiya Kennan tun a wajen kaiwa maza abinci da wajen hanyarta ta dawowa gida
A hankali ta ji lebenta na bushe mata Duda irin man leben da ta dan goga
Kasa kasa ta yiwa idannuwanta tana jin wani yannayi mai kama da muzantuwa ko rashin jin dadin zama a haka a kusa da su da kokarin rasa kuzarinta har kunnayenta suka jiyo mata murya a shake ta Dan Chainar nan yana fadin" Wauh, a yau na yarda da maganarka ISHAK, da kake cewa kuma a nan Akoy yan mata masu classs da iya gyaran jiki, ban taba gannin buzurwa a nan da ta yi gyara irin wannan ba, ka ga wannan wani level ne da sai macen da ta san kanta take yi, mu a cen mun saka shi cikin Layin tarbiyyar Yayanmu, koyar da su zuwa ana gyara masu jiki a saloon, ka ga hannunta