Showing 72001 words to 75000 words out of 188741 words

Chapter 25 - AZAL HAUSA NOVEL

sajida   

12 Jan 2025

9819

Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*

💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)

Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique)

Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?)

Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo



Idannuwansa da take kallo tsai ba gargada ko tsoro ya sakata gane irin kallon da ya yi mata mai tafe da dan kakausar zance wanda ya ankarar da ita a yanzu fa wannan din wanene, idan akace sarki kuwa ko mahaukaci ya san me ake nufi

A hankali ta shiga risinar da nata idannuwan a ranta tana ayana' Sai kace wace na yi sabo ji yadda kakarsa ke hararena dan Allah, ita kuma Salima ta wani wangale baki kamar mutum zai fada ciki!'

Kayan ta kai ta ajiye ta koma kicin din ta zauna sai turo baki take yi,a ganninta wannan sam ba adalci bane, yaya zai fara mata magana mai mahimmanci ya wani gimtse dan daukan alhaki? Ita fa dama tunda ta ganshi ta san mutumen nan zai yi daukan alhaki, da wasu idannuwansa tamkar na Sarkin kwartaye!

A tsayen nan da yake bai koma ya zauna ba sai da ta bacewa ganninsa sannan ya zauna daf da Hajia wace ranta ke mugun bace ta kalli Mah da ta yi summar tsaye, ba dan komai ba sai dan a gaban Hajia aka fadi haka, in daga su sai su ne ai zasu waske ne su bada hakuri ita da yarta, ama a yanzun bata san me zata ce dan su kwaci kansu ba

Hajia rai bace ta ce" Dama wace kike rikon nan bata da hankali?"

Mah ta sake sada kanta, a sanyaye sosai ta ce" Ki yi hakuri Hajiya, yarinta ce"

Hajia ta dauke kai tana sauke hatatarta a saman Salima, da sauri ta bar wajen itama ta koma kicin din , Hajia ta ce" ta wuce misalin yarinta tunda ba yarinya mai shekaru uku bace , wannan din raini ne, wanda ba zan dauka ba, dan ko matansa basu isa su yi irin maganar nan da shi haka ba bale wata wai BARE!"

Mah ta sake sada kai a tausashe ta furta" A yi hakuri in sha Allah ba zata kuma ba"

Shi kuwa Hajiar ya zubawa ido, har sai da ta juyo dan ta sake tambayarsa maganar mata hudu ta ga irin kallon da yake yi mata ta dauke kanta, dan ta sani sarai saboda ta yiwa mahaifiyarsa magana da zafi zafi ne zai sauke a kanta, ita kuwa sai dai ya yi hakuri a gaskiya darajarsa ta fi karfin ta ga irin haka ta yi shiru ko daga wajen uwar tasa ne bale wata wai y'ar riko

Daga nan fa maganar ta cenza salo, domin tunda Hajia ta yi maganar nan sai ya zamo ta bata komai, ya yi mata shiru du tambayar da take masa kan abinda za'a saka masa a zanen sai yace da ita ta yi yadda ya mata ya kame bakinsa yana kallon yadda mahaifiyarsa ke kai kawo

Gannin ransa ne ya bace Hajia ta salami mai zanen nan tafe zata tabo shi a idasa daga baya

Yana tafia ta dubi YUSUF ta ce" Malik, shikenan ban isa na yiwa mahaifiyarka magana ba? Kennan Ni ba uwa bace a wajenta?"

YUSUF ya dubi Hajia da kula sosai ya ce" kin tabata idan kina mata magana a matsayin y'arki kike yi mata ko a matsayin sarakuwarki wace kike mutuntawa kike yi mata?"

Hajia ta zuba masa ta kasa cewa komai

A hankali ya shafa gashin kansa gannin Mah ta fito dauke da abin spoon a tausashe sosai gannin Mah a wajen dan kar ta dakatar da shi ya ce" Babu ruwanki da gaban wa take, babu ruwanki da me zata ji a zuciyarta, babu ruwanki da Ni tawa zuciyar ta ɗan da ta haifa, idan ta dan bata maki ko wani abu da ya shafe ta ya bata maki zaki yi mata sumul ba daga kafa ba jin nauyi ko gannin darajar ta...."
Ya dan dakata dan ya ga Mah ta tsaya tana masa kallon me kake yi haka?
Sai dai Mah ta yi hakuri a yau bashi da niyar dakatar da abinda ya fara sai ya kai aya idan ya so in Hajia ta ga zata iya zama ta yi nazari ta yiwa kanta fada ta daina toh, in ta ga ba zata iya ba tabas zai ci gaba da yi mata abinda ya fara ba fashi
A tausashensa ya ce" ko ba komai ita din nan mai girmamaki ce, tana girmamaki ne dan kin girmeta kuma kin haifa mata miji har ga ƙaruwar ɗa a tsakani, Hajia mutun ce fa, da zuciya a jikinta, koda ta hanna kanta raina ki, ko rama abinda kike yi mata a duniya a lahira kina da abin kare kanki ne?, yaya kike so ki sameni yadda kike so bayan kina hamayya da abinda na fi so a duniya? Hajia bana hada mahaifiyata da kowa, a kanta kuma ina iya dukawa ko waye dan ta ji sanyi....................., Hajia, dan Allah ki dubeni ki dagawa uwata kafa ki bata lafiya, idan ba zaki iya yin magana da ita a sanyaye ba ki kyaleta, ki bar min ita,a hakan zan fi girmamaki fiye da tunanin ki......Please......."
Ya karashe yana kamo hannayen Hajia, wace ta yi tsuru jikinta na daukan nauyi tamkar wace ta sha aiki ta gaji, ita kuwa tarin nauyin yaron ne ke lulubeta, a bayane kuma tana gannin kwarai haka din ne, mahaifinsa fa ya sha kwatanta mata, yakan ce mata Andiya bata taɓa nunawa YUSUF ya tsaneta ba, YUSUF nada muguwar shakuwa da mahaifiyarsa, ko shi yana girmamashi duk irin abinda yake masa ne dan yana gannin yadda yake kula da mahaifiyarsa, ya sha fada mata ta ringa yin hakuri ta ringa kiyaye idannuwan Yusuf idan zata yiwa mahaifiyarsa fada, yana dawowa inda take ne dan ya zame masa dole, ya sha fadin ba shi ba gidan nan, idan mahaifiyarsa ta sako kafa ne yake sakowa koda bai shirya ba

A karro na biyu kennan da RAUDA ta sake yi masa kallon tsaf, kallon da bai tafe da jin haushi har sai da Salima ta zungura kafadarta sannan suka wuce da dan sauri suka nufi dakin Mah dauke da kayan karinsu su Dukansu harda su Musulima

A dole Mah ta nufi ciki itama dan ba zata so Hajia ta kuma dago da idannuwanta ta ganta a wajen ba, dan tsaf take iya sauke mata abinda jikan ya yi mata a kanta, domin itace kuka dadin hawan Hajia, wani da jan fada wani da shan duka za'a yi a wajen nan ,shi yasa ta nufi dakin Bah ta ja kofar ta shiga tatarar dakin da gyarawa tana dantse lebe da tunanin cikin ya'yan nata biyu waye ya fi ja mata magana a yau? Dayar da ta cewa Sarkin ya rantse a gaban kakarsa ko shi dan neman da yake yiwa kakar kashedi a kanta? Allah shi kyauta

Ta dan jima a dakin tana aikinta dan har bayi ta wanke fesssss ta rufo ta kunna gawayi ta saka turaren wuta mai daɗi tana sakawa a lungu da sako na dakin ya shigo da salama hannunsa dauke da plate dauke da abincin ta da ya zubo mata

Juyowa Mah ta yi, sunna hada ido ta zabga masa harrara sannan ta dauke kanta harda kyaftu tamkar wace ke nunin da zata kama shi ne

Murmushi ya yi ya kai abincin saman dan table din dakin ya ajiye yana kallonta ya ce" Mah, zo ki ci Please"

Mah ta juyo ta kalli abincin, ta ajiye burner din ta karaso ta zauna daf da shi ta kai hannunta tana shakunar kuncinsa hadi da hancinsa ta ce" Baka jin magana, uwata sa'ar wasanka ce?"

Dan murmushi ya yi ya ki bada amsa dan da haka yanzu zata yi fushi

Mah ta bude tana kallon abincin da ya zubo ta yi yar dariya ta ce" Yaushe ne zaka fara samun ziyarar abokanan naka? Ko sai an gama ginin?"

Hannayensa ya watsa , masu yi mata alamun shi din da kansa bai sani ba, dan haka sai ta dan gyada kai itama ta shiga cin abincinta hankali kwonce

Cen ta koro da ci ta ga yana murmushi hadi da girgiza kai, da kula ta masa alamun lafiya?, sai ya sake girgiza mata kai bai ce da ita komai ba, to me zai ce? Jama'a rana tsaka Mah ta dauko ƙatuwar budurwa ta zo zata ƙaryata shi a cikin gidansu? Wannan abu da me ya yi kama? Rabonsa da ace ya tabatar da maganarsa har ya manta gaskiya, dan ko Bah in dai ya fadi abu yana yarda tunda ya san ba zai masa karya ba ai, rayuwa kennan idan baka mutu ba ka sha kallo

Sai da yama liss Mah ta sanarwa RAUDA eh da gaske an ga Bah dinta, sannan ta bata damar ta je gidansu ta sanarwa maman nasu kuma su dawo da bakonta wanda da kyar ta sanarwa Mah ya iso Nijar din kuma yace zai zo bata san yaya zata fada masa tana nan ba,

Da kula sosai Mah ta ce" Zaki tafi da ke da Salima ne, idan kun je ki yi kokarin sanarwa bakon inda kike, ki fada masa sak gidanku nan ne, kuma Ni ce mamanki, ki kula, ki kama mutuncin kanki, ko wanene shi in dai da gaske yake ya fara neman izinin ganninki wajen manyanki kafin ku ga junna a ka'idance, a yanzu na baki damar nan ne dan yadda kika kwatanta min darajar da ya baki ya sa shima na bashi darajar gannin y'ata a haka, ki sani kina da daraja wace take tafe da darajaza daga bakin lokacin da kika amsa sunnan y'ata, ki kula da mutuncinki, ki kula da mutuncinki, idan ya baki wani kyauta kar ki amsa ko menene , ki bari sai kin sanar a gida kin ji?"

RAUDA na tsaye ne Salima na ja mata zif din Abayar da ta saka, dan irin egypcien Abayar nan ne budadu masu kyau da tsari, Mah na yi mata maganar dan idan sun tafi itama zasu fita ne da su Hajia matan Bah gaba dayansu dan zuwa ganninsa a asibiti

Har ga Allah bata san ta shagala da kallon Mah ba sai da Salima ta ankarar da ita sannan ta sada dubanta ta amsa Mah din kafin ta karasa ta yi tsaye wajen turaran wutar da Mah din ta saka masu tana fadin su tabatar sun turaru sannan kar Salima ta yi tuki direba zai kai su ya dawo da su, ƙafarsa kafarsu du inda suka shiga ya bi su

Daga haka Mah ta fice , Rauda ta gama tauraruwa ta dauki mayafinta blue mai haske sosai ta yafa a kanta , hakama Salima ta rufa mayafin abayarta sannan suka fice

Tunda suka kama hanya Salima ta kula da yannayin sanyin da jikin Rauda ya yi, har ta kasa hakura wajen Danja ta yi mata tambayar abinda yake damunta

Da dan murmushi Rauda ta ce" Me kika gani Salima?"

Salima ta ce" Na ga daidai lokacin da kika fito daga wanka da yanzu ba daya bane yannayinki, ina fatan lafiyarki kalau?"

RAUDA ta yi mata murmushi bata ce mata komai ba har suka karaso kofar gidan suka sauka daga motar direba ya parker yana jiransu, domin bakon Salima ya fi minti talatin a motar a zaune yana jiranta, motar da Salima na gani ta gane ko wace irin mota ce domin Bah ya hau ta, ƴaƴansu ya bashi ita a lokacin da ya sauke su

Tunda suka sauka daga motar ya bude ya fito, fuskarsa ke dauke da murmushi yana kallonta har ya karaso inda suke tsaye yana sake sakin fuskarsa da walwala sosai ya ce" ina farin cikin sake gannin ki masoyiyatah"

RAUDA ta yi dan murmushi tana dauke dubanta a kansa ta maida kan Salima wace ke yin murmushi tana kallon Balarabe sak abinsa, hausarma gatanan dai, ama zai yi Sa'a Bah gaskiya

Da dan murmushi a fuskarta ta furta" Marhaban bika fi'akhi"

Murmushi ya yi sosai har kamar ya rungumeta ya yi mata irin gaisuwarsu ta larabawa, ama ta jima da sanar masa ta fi so su kiyaye hakan su yi koyi da abinda addini ya kawo

Yana kallonta ya ce" Na gaza hakurin sai gobe na gan ki, ku je cikin mu zauna ko?"

Da da ne, zata iya jan shi cikin gidan koda ta shekara bata nan, ko ta je motar tasa su zauna su zanta, ama a yau sai take jin wani iri kamar ba zata iya ba,
Saima da ta kalli Salima, sai ta ga kamar wace take mata gargadin zuwa ta shige motarsa
Kai ta dauke a tausashe tana kallonsa ta dan langwabar da kanta ta ce" Ka yi hakuri na Barka kana jira, ka san yanzu ina cen gidan.....gidan....."

"Gidanmu, take nufi, gidan garin Tsatsunburum, Ni yar uwarta ce, yanzuma mamah ce tace mu zo mu sanar maka, ana son ganninka a fada " Salima ta karɓe zancen, a tausashe ta sanar masa sakon da ta kula Rauda ba zata iya fada ba, dan tunda ta fara maganar nan ta shiga dan juye juye da dan shafa agogon hannunta ta tabata zancen bata gama karbar sa ba sai kawai ita ta sanar

Harda ajiyar zuciya Rauda ta sauke dan kuwa Salima ta taimaketa ainun, domin bata san yaya zata fada masa ba, dan kusan duk wani wanda zai fita da ita bayansa ne, shi din ya san komai nata, ciki harda marikiyarta

Abdullal Jabar abin ya daure masa kai ainun, sai dai wannan magana ta ana son ganninsa a fada ta saka shi rikicewa da farin ciki, kwarai Allah ya amshi adu'arsa, ga dukkan alamu abinda ya roka kan kar ta wahalar da shi ko ta ki shi Allah ya amsa

A hankali ya juya bayan Salima ta sake tabatar masa da maganar da yake tunanin haka ne, cike da shauki da farin ciki, Rauda na biye da shi har kusan motarsa, sannan ya sake juyowa yana kallonta da tarin mutanen dake ta kallonsu ba yaran ba, ba manyan ba ya ce" dama kina da alaka da HONORABLE BELLO?, "

RAUDA ta sada idannuwanta, a hankali ta ce " bayan tafiyarka, Allah ya hadani da shi da matarsa da kuma dansa, shine suka daukeni , matarsa tace ita din uwa take a wajena zata rikeni tamkar y'ar da ta haifa, hakama mijinta ya yarda"

"Wai kina nufin harda SS YUSUF ?" Ya fada yana zarro idannuwansa cike da mamaki

Dan tsaida maganarta ta yi tana kallonsa
Sai ya basar, gannin kallon da ta yi masa, ya dawo kan maganar da ta fada din ya ba abin mahimmanci sosai

Kwarai ya ga cenji, domin babu irin yadda bai yi ba kan ta tsaya ta amshi tsarabarta ta nuna an hannata sai ta tambaya a gida, karshe dai suka rabu da cewar gobe da dare zai je ta sanar a gidan nasu , ya juya ya tafi yana jin kwarai nutsuwa na shigarsa, a yanzu ya san idan ya buga da karfi Rauda tashi ce , burinsa zai cika kwana kusa kennan? Allah kennan mai yadda ya so da bawansa a lokacin da ya so

Tana juyowa idannuwanta suka sauka kan Salaha dake tsaye a dokin kofar gidan, jikinta sanye da wani zani baki wanda a ido kawai idan ka kalla ka san ya yi dati, rigarta kuwa kamar irin kannanun rigar nan da ake sakawa a ciki ne du ga nono nan ya bayyanar da kansa sai wani dan kwalin atampa ta yafa tana kallon Raudar da bakonta

Da sauri ta koma gidan gannin Raudar ta nufi gidan da wata bakuwa

Tana shiga da karfi ta ce" Mama, walahi gatanan shegiyar ta dawo, an gama yawon ta zubar din, kin ga balaraben da ya ajiye ta? Ni dai ko randa ta taba ba zan sha ruwan randar ba, kar na gogi kanjamau, kin ga wai yadda ta karra fari? Ta yiwu ita ta sake maki miji kina nan kina kuka a banza a wofi , ai na fada maki ki daina kukan nan tunda kin dauko Abdul zata zo ne!"

Turus RAUDA ta yi jin magangannun da Salaha ke yi

Ai kau idannuwanta suka sauka a kan Abdul dake zaune gaban pampo yana wanke wanken kwanoni, kana gani ka san ba a hayacinsa yake ba, tsoro ne fal a fuskarsa kuma wankewar sai yi yake kamar an aiko shi

A raunane sosai ta ce" Abdul"
Ya ji ta fa, ama yaron nan ya gaza waigowa dan a tunaninsa ba ita din bace kunnayensa ke masa gizo

"Munafuka, annamimiya, yau sako ya je maki baya nan kin zo nan nemansa ko? Kwarai ni na dauke shi ko zaki tuna da ubanki wanda ya rike ki ki zo ki nemo shi, in banda rayuwa irin ta wanda baida imani ke har kya manta Umaru? Ko fitar nan da ya yi ai sanadiyar ki ne, dan kin kawo masa kudin karuwanci gida, shine zaki tafi ki yi kwonciyarki ance a masarauta ko? Sai ki zo ki samo min mijina idan ya so ki biya Ni bashin da nake bin ki sannan ki dauki wancen mahaukacin ,dama rikonsa sai ke ai!"

Bata tsaya bi ta kan magangannunsu ba, magangannun da suka saka Salima daskarewa a waje daya cike da tsoro da mamaki,

idannuwanta rufe ta karasa wajen da Abdul yake da sauri ta dago dago shi, jikinsa da dati da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login