Showing 135001 words to 138000 words out of 188741 words
fisheki ba?, me aka yi aka yi namijin da ya cika takama da jiji da kai? RAUDA babu so a wajen da ba za'a iya fadarshi ba, ke mace ce mai daraja, furta so ba rashin daraja bane, ko alamuntawa, sai dai ke taki darajar abar dubawa ce RAUDA!, kin jurewa lokacin da baki da mai maki fadama bale yanzu? me aka yi aka yi soyayar kanta? RAUDA ki kama kanki, kar ki yi abin Allah wadai, RAUDA ki kama kanki!'
A hankali ta lumshe idannuwanta daga kallon fuskarta, a nutse ta janyo kujerar gaban madubin ta zauna ta sake dago fuskarta ta tsurawa kanta ido
A nutse ta shiga yiwa kanta kalaman da zasu fisheta, wa'inda ta tabata in dai ta rike to kuwa tsaf zata tsira da mutuncinta, a tausashe ta shiga ayanawa kanta magana kamar haka' Ke mutun ce kamar kowa RAUDA, kuma Allah na iya jarabtarki da abinda ke iya yi ke iya rikitaki a rayuwa har ya zo ya nemi zame maki AZAL, sai dai idan har kin rike addu'a babu abinda zai same ki, mummunar kadararki zata juya ta dawo kyakkyawa......., RAUDA kin kasance mutun mai tsare tsare da addu'ar kalar mijin da kike so a rayuwa, misali bakya son namiji mai shegen son mata ko aure aure dai da sauransu, to a kan me zaki dubi mutumen da kafin darajar sarauta ta hau wuyansa ya kasance mai rike da darajar sarautar bakin layi wace kowace yan mata ke wawarsa?, Haba RAUDA a yanzu da igiyar daraja irin ta sarauta ta hau kansa ke da kanki kin sani karya ne ace dayar nan ce, bayan wannan ki duba ki gani, ke da aka raba ake girmamawa aka ba daraja yau ke ce da zagin matarsa?, idan Mah ta ji ki ce me? hana RAUDA me ya kaiki wannan gangancin? me yasa ba zaki ci gaba da tafiyar da rayuwarki yadda take ba?, Eh lalle YUSUF shine AZAL din ki!, sai dai kuma addu'a da neman tsari ai yana maganin komai ko RAUDA?, kema mutun ce mai rai da lafiya kina iya gannin mutun ki ji ya maki, ama kuma kamar yadda kike iya gani ki ji ya maki kina iya kawar da kanki a kansa, bale idan mutumen nan kin gane take takensa, shikenan ke da shi sai ki yi ta neman tsari, ke wai menene soyayar kanta? ake rayuwa ba soyaya kuwa lafiya, to kema daga yau ba ke ba wannan maganar, bale ke da Allah ya taimaka ganninsa sai idan kin so? baki ganshi Bama bale har hankalinki ya nemi gushewa RAUDA!'
Magana take yiwa kanta idannuwanta a lumshe a cikin zuciyarta, kuma har ga Allah maganar ta Ratsa ilahirin jikinta ta yarda da hakan, domin a yannayin nan da take ciki kunnayenta suka ringa jiyo mata Muryar Jakadiya baba tana bada umarnin a kama alkyabar uwar gidansu, a yi me a yi me
A hankali ta dago idannuwansa sakamakon shigowar da Salima ta yi tana kiran sunnanta
Ido hudu suka yi ita da Salimar
Salima na dubanta ta ce" Dear, me yake damunki ne? yau ko baki da lafiya ne babyn Mah? taso mu raka aunty Amnah mana Gatacen sun fito Su Bah na yi mata nasiha"
Murmushi RAUDA ta kirkiro a hankali ta dan rausayar da kanta tana kallon Salima ta ce" Sisi am, zan yi sallah ne na dan yi karatu, ki je zan tardo ku idan baku dawo da wuri ba in sha Allah "
Gyada kai Salima ta yi ta yi mata murmushin itama sannan ta juya ta ja mata kofar a nutse
Mikewa RAUDA ta yi ta je ta rufe kofar da ky sannan ta nufi bayi tana sake dannar kanta , fadawa kanta take babu wani abinda ke damunta da su baki daya, sake fadawa kanta take yi ko me zata gani ko ta ji ba damuwarta bace in dai abinda ya shafe shi ne da matarsa, kuma in sha Allah daga shi har matarsa ta yiwa kanta alkawarin zata fita a harkar su , ba ita ba su bale ranta ya ɓaci!
Tana gama wankan da zata je barci ta saka tufafinta doguwar riga a saman pant dinta kadai ta daure gashinta sannan ta shiga gabatar da sallar isha'i, tana gamawa ta dora nafilar sannan ta cire ta shafa turarukanta ta je saman gadonta ta sake kakabewa ta yi kwonciyarta tana dora wayarta saman abin gadon bayan ta kashe fitilar dakin
Da addu'a da juye juye da kyar ta samu barci ya fara fizgarta, hakan ya sa bata san ta dauki lokaci a kwoncen ba, kamar wace ta je duniyar da bata san abinda take yi ba ta dawo haka ta tsinci kanta, har sai da ta ringa jin amon kiran wayarta sama sama sannan ta bude idannuwanta tana jin gabanta na faduwa ta lalubo wayar da sauri ta duba screen din ta ga sunnan Mah ke yawo a sama
da sauri ta daga muryarta na shakewa ta furta"Mah?"
Mah dake zaune a falo ita da YUSUF takaici ya isheta, sai shayinsa, ta shiga ta dafa masa wai ba shine ta saba bashi ba, ta tambaye shi wani irin dandano yake so yace shi bai sani ba shi dai wanda ta saba bashi idan ya zo, ita kuma tunda RAUDA ke hada mata tea bata taɓa Sannin me da me take haɗawa ba, ita dai ta san da ta mata wani mai dadi tace ta ringa yi mata shi kulun bale da ta sanar mata tana haɗawa harda kafi amarya kanshi saboda yana karra lafiya sai kawai tace a rike hadin
da Kula da kuma yannayin tausayinta Mah ta ce" Daughter, kin yi barci ne? idan kin yi barci yi kwonciyarki kawai"
Dirowa ta yi daga saman bed din har tana yarda hularta saboda murya Mah sai ta ji kamar bata da lafiya ne, ko abin barci ne ya sa ta ji haka? ita dai da sauri ta ajiye wayar tana fadin" Gani nan zuwa"
Bata tsaya daukan hijab ko wani abin ba, tsoronta daya kar aje jikin Mah ne, dan lokaci zuwa lokaci ciwonta na tashi, shi yasa ko yanzu ta fice daga ita sai doguwar rigar nan da ta sauka har kasa, sai dai tana da tsaga daya jal daga gefen cinya, gashin kanta daga gaba ya kwonta lambuk daga baya kuwa du ya nanade irin na masu gashin nan, dama dama tana da dan dogon hannu kadan rigar, ama bayan wannan rigar mai lafewa a jiki ce sosai shi yasa harta sawun pant dinta ana gani
Da sauri ta bude dakinta, kafarta sanye da takalmin daki na kusa da gado mai gashin mage mai kalar pink ta nufi dakin Mah da sauri
Har zata kama ta bude kofar, Mah ta furta" BABY?"
Da dan sauri ta juyo inda ta ji Muryar na Mah, sannan ta juyo da dan sauri kadan ta karaso ta kai zaune daf da Mah tana fadin" Mah jikin ne? ina ke ciwo? kafar ce?"
Mah ta sauke murmushi tana jin kaunar RAUDA har cikin zuciyarta ta kama hannayenta ta ce" Baby Lafiyana kalau, sorry daughterna na tasheki ne ko,?"
Sai kuma ta juya wajen da yake hakimce cikin shigar kayan barcin shima masu duhu da santsi tana kallonsa ta ga lokacin da RAUDA ta sauke ajiyar zuciya jin lafiyar mah kalau ta ce" Ji fa rikicewa, shi yasa nace ta yiwu ta yi barci, tashi ki je ki yi kwonciyarki, ko ki nuna min yadda ake yi na nuna masa ya je ya koyawa matarsa ta dafa masa, barima ka ji mun cire ka a kwanon abincin part dinmu tunda mun maka aure!"
Tamkar an dakatar da ita haka ta ja ta tsaya a zaunen nan gabanta na wani irin mummunar faduwa
Da kyar ta iya daidaita kanta bisa kwarin gwuiwar da ta ba kanta ta dan saki murmushi ta mike tana dan susar kai ta ce" A'a Mah bari in je in dafa"
NA SAKA BONANZA TA NOVELS DINA BAKI DAYA A KAN FARASHI MAI RAHUSA 1K IN SHA ALLAH, KI TUNTUBENI BISA NUMBANA LAMAR HAKA 93811618
Azl 48
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE
💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*
💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)
Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique)
Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?)
Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo
Mah ta bi yadda du ta dan daburce kadan, a yanzu ta gane a yadda ta fito bata san da wani bayan ita a falon ba, tana kallonta ta nufi dakinta da sauri tana jan rigarta har ta shige, minti kadan ta fito sanye da zumbulelen hijab dinta wannan karron yannayinta ya nuna ta samu nutsuwar tafiyar ko dan ta suturce jikinta ne ko meye? a nutse dai ta nufi kicin din ta bude madubin ta shiga ta rufe
Murmushi Mah ta yi a nutse ta juyo dan yi masa magana, sai ta ga idannuwansa a kan kicin din duda bata nan , dan ta jima da rufewa, kuma yannayin fuskarsa ya dan kame kadan da yadda suke shan rikici tun dazu a kan tea dan da ya taba wanda ta dafa fuska ya tubure shi dai ba wannan ba kuma ya saba idan bai sha ba kansa ciwo yake yi masa, da tace Baby ke dafawa kafada ya daga irin shi dai ba ruwansa ko waye shi dai tea dinsa ya sani
Mah ta dan yi murmushi ta dan motsa dan tana so ya ji abinda wata fada
Cikin dabara ya dauke dubansa ya dan murza hancinsa sannan ya dubi Mah a nutse ya furta" Na gaji sosai yau Mah"
Mah ta yi murmushi tana fadin" Sannu d'an Mah, kana gani yarinyata ma ta gaji ka sa na tasota, yarinyar nan Allah Ubangiji ya nuna min ta samu miji na gari ta yi aurenta itama ta haifi wa'inda zasu bauta mata da jikinsu da lafiyarsu kamar yadda take hidima da Ni"
Dif ya yi, maganar da Mah ta yi ta saka shi yin shiru na yan dakiku kafin ya dago dubansa ya kalli Mah sau daya sannan ya dauke duban nasa yana dan dantse lebensa, a ransa yana ayana' Uhum, yanzunma ai ta haifa sai ya mata hidimar, Ni banma san takabar nan ta meye take yi ba, ko kafin ya rasun sai da ya mata wani abu shi marar jin tsoron Allah?, koda yake ba wace bata jin tsoron Allah sama da yarinyar cen, tana kallon mutun ido cikin ido ta iya raina masa wayo da yin tamkar bata san me yake yi ba, har Ni zan hanneta abu ta aikata, kuma ta ci gaba da kallona ido cikin ido, gata in kasheta ko? ba abinda zan maki RAUDAhhhhhh, ama bana jin in zan iya yafe maki, ba aure aure ba? bismillah ki sake yin wanin sai me daga ke har maman naki!'
"Magana nake yi YUSUF" Mah ta fada da dan karfi tana dan daga hannunta, dan sau uku kennan tana magana bai ce mata komai ba
kallonta ya yi da dan sauri yana furta" Na'am?"
Mah ta fara magana RAUDA ta fito dauke da wata mahaukaciyar butar shayi da kofi na kwalba a saman plate dinta , a lokacin ne Mah tace" Yaya ina ta addu'a har sau uku ba zaka ce min amen ba? na yi maganar Allah ya ba y'ata miji na gari , baka ce min Ameen ba, na yi maganar Allah ya baku zaman lafiya ya kade duk wata fitina baka ce min amen ba, na yi maganar taimako da aka bayar wa mazan masu mana hidima Allah ya karra budi shima baka ce min ba fa"
A hankali RAUDA ta ajiye plate din a saman dan madaidaicin teburin dake dauke da taya biyu kadai wa'inda ake kafe su idan ba'a so teburin ya motsa, kuma ana sakin su idan ana son motsa shi, a nutse ta sake su sannan ta turo teburin har gabansa ta kafe masa shi, a nutse ta dauki dan karamin kofin ta zuba tea din sannan ta dauki zuma ta bude ta tsiyaya madaidaiciya ta saka dan karamin cokali tana motsawa a hankali ta dago idannuwanta jin ya yiwa Mamanta shiru bayan ana masa fada ko dai ya tafi ne?, sai ta ga yar yatsarsa ya kai wajen sajensa a hankali yana dan shafawa lebensa na fitar da alamun murmushin fadan da Mah ta dage tana yi dan kawai bai ce wai amen ba
Mah ta turo baki tana dauke kai, shi kuwa a hankali ya furta" Amen Mah"
Sai kuma ya juyo dan tunda ta fito ya ga fitowarta har zuwa yanzu
Hannunsa fari sal ya miko ya amshi tea din, idannuwansa a kanta da kallon da ya sake sakawa zuciyarta idasa hautsinewa kafin ya dauke dubansa yana sauke ajiyar zuciya a hankali ya kai kofin bakinsa
Da dan sauri ta furta" Bai huce ba fa!"
Mah da ta yi kamar bata nan da gangan dan zata so ta idasa ganewa idannuwanta ta sake dauke kai dan sai ta ji kunya na son kamata bayan ba wani abin suka ce ko suka aikata da zai iya bata kunyar ba, haka kawai dai ta ji inama ace rana ne sai ta bugawa wani kira ta bar wajen ko sa gama rainawa junna hankalin
Idannuwansa ya sake sakawa a cikin nata, da kaifin da sukai masa shi kansa zuwa ita da ta ji kamar zata lume ciki, yana kallonta yana danne harshensa da hanna kansa yi mata tambayar nan daya jal, cewa wai takabar me kike yi? ke takabar me kike yi? dan Allah takabar me kike yi? ama ya kasa dan ba zai so a masa wata fasarar ba, ga Mamanta nan zaune, sai kawai ya yi mata horon da ya fi sakata yin laushi ta hanyar amfani da idannuwansa ya ci gaba da surbar tea din da ta bashi bayan da zafin sosai
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta dauke idannuwanta a kansa ta juya ta karasa wajen Mah a tausashe ta furta " Good night Mah"
Mah ta dubi fuskarta, du ta yi yaushi kana ganninta zaka ga cenzawar yannayinta, ta yi mata murmushin itama tana fadin" Good night baby, Allah ya miki albarka, ama daga yau ba za'a kuma taso ki saboda tea ba, zaki koyawa matarsa ne!"
A ranta ta ayana' Allah sai dai kar ya sha!'
Shi din kuwa ya ayana' Ita din dai zata dafa shi, wa ya sa ta saba min!'
A raunane RAUDA ta kai zaune tana sake jin irin yadda kirjinta ke yi mata zafi da ɗaukan mugun abinda ta gama yi masa fada dazu, sai dai kasancewar addu'a ce baban makamin da ta gama yarda zai zamo makamin yakin duk wani abinda ke kawowa zaman lafiyarta farmaki sai ta ringa jin sassauci da salama a cikin zuciyarta da kuma dangana, karshema sai ta dauko yabon mamaci ta yaba a zuciya ta bige da yi masa addu'a kamar yadda ta saba har barci ya kwasheta tana yi masa addu'a bata sani ba.
Ya dan jima tare da Mah, har sai da ta kore shi sannan ya mike ya nufi hanyar da ya biyo ya fice ya nufi bangarensa
Ya bude ya shiga mamakeken falon da ya raba bangare bangaren ginnin har sau biyar
Kwarai ya san dama a nan ne za'a fara ajiyeta matsayin bakuwar wajen, kuma ya tabata da wahala ya tardora a rufe kamar yadda bakin amare ke yi, dan tuni ya gama gane wannan fa idan ba'a gama raba hajar a titi Bama da sauki sauki dan yannayinta yannayin tafiyar kayanta
Tun da ya shigo AMNAH ta ajiye wayarta, waya suke yi da mahaifiyarta duk irin tsayin daren nan da kuma kasancewarta amarya tana sanar mata dukkan abinda aka yi daya bayan daya ita kuma tana shawartarta abinda zai fishe su
Murmushi ta sake yi masa tana dan sada dubanta, dan duk yadda take son kallonsa ido cikin ido sai ta ji ta gaza jurewa, bata san yaya aka yi shi baya jin nauyin kallo ko kadan
kansa ya dan kawar yana sauke ajiyar zuciya, da kyar ya danni kansa ya karasa saman falon ya zauna yana sake dubanta da tunanin abinda zai yanke a yanzu
Dubansa ta yi da wata murya ta kisa ta furta" Barka da shigowa ur majesty"
Idannuwansa ya dan lumshe a hankali, hakan ya tabatar mata amsar kennan, sai hakan ya sake saka mata dan shaku da gudun cika surutu
ya jima a hakan, yannayinsa a mace gaba daya sannan ya mike a nutse da nufin tafiya nasa bangaren
Mikewa ta yi zungwai zungwai ta bi bayansa har sai da ya dan dakata ya juyo a nutse yana dubanta
Ba da niyar wulakantarwa ba, dan ya riga ya amsa ko mecece, kamar yadda ya gama yarda cewar ya rungumeta shine zai sa