Showing 93001 words to 96000 words out of 188741 words
Yaren gidan babu wata ba, kuma har ga Allah shi bai ga abinda RAUDA ta yi masu ba, ga waje nan su ce babu, idan ya dauke kafa ya nemi kin zuwa inda take ita sai ta zo inda take din, a dole ta hakura da duk wata kyara da hantara da gorin arziki ta toshe kunnayenta ta rintse idannuwanta dan ta riga ta gane ko me zata yi ba za'a raba zumuncinsu ba, sai kawai suke tafe a haka
a tausashe ta ce" Na jima a nan ai Atu, tun ranar da aka naɗa shi sarauta muka zo nan, kafin a nada shin kuwa na kwana ɗaya a wajensu, a takaice dai su din iyayen marainiya ne, mahaifiyarsa ce ta daukeni, mahaifinsa yace ya ji ya gani, shine suke rike da Ni"
Atu da jikinta ya fara wani irin masifar sanyi tana kallonta ta ce" Kamar yaya suka dauko ki? me ya same ki a gidan uncle din? "
ajiyar zuciya RAUDA ya sauke, a sanyaye ta shiga labarta mata abinda ya faru, tun daga batan Uncle, har zuwa sace Abdul da abinda ya wakana bayan hakanan"
a hankali Atu ta saka hijab dinta ta rufe fuskarta tana girgiza kanta dan kukan da take tarewa
da kyar ta iya sasautawa tana kallon RAUDA dake fadan ta daina wai meye na koke koken?
ATU ta ce" Shine kika ki zuwa inda nake? shine kika ki dauke Abdul ku zo wajena?, kin san ko baki zauna a gidana ba kina iya zama a wajen Hajia ko? kin san Hajia na son ki domin Allah ko? shine ko ko tuna Ni kika yi tafiyarki kin samu Mah da wancen kanwar HONORABLE din ko?"
RAUDA ta yi murmushi tana fadin" ke kam ba dai jaje ba, to wai ki yi hakuri mana, sai da na daina baki hakurin ku ji min mata!"
itama yar dariyar ta yi tana kallon Salima da ta shigo yana murmushi ta ce" An ce fa ki je ku wuce, tuni sun fita sauran sun tafi ma"
Atu ta mike tana fadin" Bari in fadawa dear ya BARNI na kwana a nan din nima ko ki zo mu tafi"
daga Salima har RAUDA ido suka zarro, da kyar suka rarasheta bayan ta amshi numbar Salimar tana fadin zata dawo ta kawo mata wata wayar kuma su tafi tare idan ta fadawa Mah
ita dai Rauda murmushi kawai take yi, suka rakata har wajen mota sannan suka dawo
sunna shigowa falo Salima ya amsa kiran mahaifiyarta, tana kallon RAUDA ta ce" bari ki ji, walahi wanke wanke na jiranki dan na kai maki su na tara maki, idan na fito daga dakin Mama daki zan wuce na yiwa Abdul lesson nima na yi karatu ehe!"
tana fada tana yin ciki da dan gudu ne, hakan ya saka RAUDA sakin murmushi tana girgiza kanta ta nufi kicin din hankali kwonce ta cire dan kwalin nan ta rataya ta daure gashinta a tsakiya sannan ta shiga gyara plate plate din wajen pampo ta dauko sabulu da sponge ta shiga wankawa zuciyarta fesss, ta samu duk wani nauyi ya ragu sai nishadi take ji a cen kasan zuciyar Tata, ko dan ta hadu da ATU ne? ko kuwa dan ta samu nutsuwa a fira da Abdallah ne? ita dai ta fi jin dadin a cen kasan zuciyarta idan ta waiga ta waigo ta ganta tsaye itama ana bata ba tare da an yi mata gori ba, ana ciyar da ita ba tare da ance ta kawo kasonta itama ba, ana yin fira da ita tamkar wata mai cikakken yanci, tana motsawa yadda ta so da tunanin kiran wata Mama har cikin ranta bayan Tata uwar ta kwonta dama, bata taba tunanin bayan gawarwakin da aka barta ta hanga daga nesa zata kuma jin ana yi mata fada dan ta gyara ba, dan a da ta yarda cewa tunda aka birne iyayenta shikenan an birne mai sakata kuma bai hannata, ashe a duniya akoy wa'inda ke daukan dan wani tamkar nasu har su yi masa fadan rayuwa? zata ci gaba da godewa Allah dan shine ya yasare mata har ta samu wannan daukaka
tana aikinta da bege ne a zuciyarta har ta juyo dan daukar abin goge kofunnan nan na kwalba dan ya rataye su a jikin karfen da ake rataye su idannuwanta suka sarku cikin nasa,
da sauri ta rintse idannuwanta kasa kasa ta dafe kirjinta da ya buga mata da mugun karfi ta furta" A'uzubilahi minna shaidani rajim"
kofar frij din dake hannunsa ya mayar a hankali ya rufe , yana rike da kwalbar lemun da ya dauko ya karasa saman kujerar dake kicin din mai dauke da dan table, domin irinsu sun kai hudu a kicin din ya zauna yana ajiye kwalbar sannan ya sake dago dubansa ya kuma zuba duban da ya yi mata a dazu wanda ya gama raya mata sak yana mata kallon wata fasika subahanallah
idannuwanta ta dauke, dan bata iya irin kallon nan ba, da wahala ta iya jurewa, ama kuma ta kasa jure kawar da kan nata da kuma kasa hakura da abinda ranta ke ayana mata har ta sake juyowa ta kalle shi zuciyarta na dokawa tana jin tamkar ta je inda yake zaunen nan ta fada masa walahi abinda ya gani ba abinda yake tunani bane a kanta, ama ta kasa dan haba daya yakan cike mata idannuwa da tunani ne har ta ji ta gaza katabus idan yana wajen
idannuwansa ya cire a kanta, yana jin dacin da ya rike masa makogwaro har yanzu bai fada ba, shi yasa ya fito daukan jus dan baya bukatar surutu da kowa sai gashi ya samu yar nan a kicin din tana aiki , shi dai bai san me ya zaunar da shi ba, ya dai zauna ne ya kasa tafiya
karasawa ta yi ta dauki abin bude juss din, sannan ta dauki kofin da ta wanke jiki a mace ta karaso wajen table din ta ajiye kofin hannunta na dan so ya mata rawa dan har sai da ta dan jimke shi kafin ta kama kwalbar da abin budewar nan ta bude sannan ta dan dago a hankali idannuwanta suka sake shiga cikin nasa
daburcewa ta yi , a sanyaye ta ce " walahi ba abinda kake tunani bane a kaina, Ni ba yar iska bace, kuma shima hakanan, barkwonci ne da tsokana take saka shi yin wasu ab....."
sai kuma ta yi shiru tana haki tamkar an biyota da gudu
kaifafun idannuwansa kawai ke kanta, ci kanki bai furta mata ba ya dauki jus din ya fice, inda ta ji wani shayinsa da tsoron yannayinsa a ranta, wanda bata taɓa ji ba, tunda Allah ya haliceta, bata firgita a kan laifin da ta san ta aikata bale wanda bata aikata ba , a birkice ta zauna saman kujerar tana yamutsa gashin kanta, tana jin tausayin kanta, kai abinda ta sani daya ne kar ya fadawa Mah wata maganar da Mah din zata ji haushinta, dan bata san me yake iya fasarata ba, dukda ya san da wahala ya wani kula da abinda ya gani, ama kuma idan da bashi da wani nauyi a kansa, yanzun yana da shi, dole ire iren abubuwan nan ya taka masu birki a masarautarsa
yana komawa dakin ya nemi waje ya zauna yana kama sunnansa a cikin zuciyarsa lokaci guda yana fadawa kansa magangannun da suka yi tasiri sosai wajen nesanta shi da AZAL!, ya fada tun kafin ya gane kansa, bayan ya gane kansa kuwa ya fada babu AZAL din da ta wuce ya *SOYAYA!* , kuma in sha Allah shine da kansa zai yi yaki da kankin kansa ɗan gannin bata shafe shi ba, ba zai taba yarda da wannan *AZAL* din ba, komai rikicinta kuwa zai ture ne, dan haka ya kafa kai ya shanye jus din ya dauko wayarsa ya fara shiga sakwannin da aka ajiye masa na karin binciken da yake yi da irin tsarin da *TASA SALON SARAUTARSA* yake so ta kasance
wannan suka dan dauke masa hankali daga abinda yake tunanin ba'a kyauta masa ba, har ya dawo ya ringa basarwa tamkar babu wani abinda ke iya Dada shi da kasssssss a wannan fannin, dan binciken da TAJ ya masa a kan matar nan da Mah ke fushi da ita ya sake dauke masa hankali, wai ya je ya samu an yi mata sata, kuma bata san inda y'arta ta shiga ba, hakan ya sa tana neman susucewa domin zancecekun da take yi sai ya dauki fansa, ko a kan wa take nufi bai gane ba shi dai, ama kuma baban abinda ya fi ganewa shine babu abinda ke girgizata irin maganar mijinta da ta y'arta,da wannan ya rufe bincike bincikensa bayan ya ji jikin Uncle Umar ya warware sosai likitan na saka ran sakinsa nan da yan kwanaki idan ya sake murmujewa ciwukansa suka yi sauki sosai.
"Ashe baki da wayo? ashe shashasha ce ke?, uban me kike yiwa rawar jikin da zai sa kulun kina gindinsu? kin kawo su dakinki sai wahala kike ɗorawa kanki? Tun ina kauda kai har kin sa na magantu ke baki da hankali ne? Salima bari ki ji Salima A ruwa akan dade ba a wuta ba, kuma duk abinda kike tsinta a wajensu na soke ba ke ba YUSUF bale tarkacen dake tare da duniyarsa!" mahaifiyar Salima ke yi mata fada tunda ta shigo ta duka a gabanta
rai bace ta dora da fadin" kina kallo, tunda suka zo uwarsa ta kange komai, da gidanmu ama Hajia ta zo ta shinshinfida mana dokoki dan an dora dan so a mulki, a yi mu gani in tusa zata hura wuta, in dai mashayin yake kuma mazinaci? Sai ya aikata a cikin gari ta yadda zamu fito mu jefe shi!, ke dai ina hanna ki shiga harkar su, ina maki hannunka mai sanda har kin saka na yi maki magana, ki guji ranar da raina zai bace walahi sai kin kasa gane Ni, dan ba zan taba sasauta Maki ba!"
Kan Salima na kasa ne, hawaye na bin fuskarta, a zuwanta dakin mari biyu ta sha kafin wannan tashin hankalin ya biyo baya....., ba marin ne ya fi daga mata hankali ba irin furucin bakin mahaifiyarta
shin me ya yi zafi ne? me yasa ake son kai abinda yake danko da danko gaban wuta dan a raba? jinni daya fa akace, a jinni dayanma uba ne shi, ya kyautatawa kowa da kowa ba wai iya su da suke kannensa ba
a raunane sosai ta ce" Mama dan Allah ki yi hakuri"
Mahaifiyarta ta dauke kanta tana tuna sharar shanyen da kishiyarta ta yi mata dazu , cikin dariya wai tace su Salima dai kiri kiri an zama boyi, a yi girki a yi gyaran gida , koda yake ta yi abinta ita ta san abinda ake bata,
maganar ya mata zafi sosai, kuma ta kasa magana dan gaskiya ta fada, Salimar ta zama kamar waya boyin gidan, komai ita ke ja da sauran yan matan, itama abin nan na yi mata ciwo, ama ba komai ai zai dawo gidan shi Hon din, idan ya dawo a san abinda ake ciki, ita ta dukufa ne addu'a take yi yana dawowa ya amshi mulkin nan a ga ta tsiya, sun ga ta isa da takama daga Hajiar har ANDIYAR , dukda Honorable dinma nasun ne ama ba su kadai ba harda suma da ake yiwa gani ganin!
"ki tashi ki je ki yi abinda zai gyara ki, fitowarki a babar likita shine tsirarki a kulun ina fada maki, mace kike in baki jajircewa kanki ba haka zaki yi rayuwa a bayan wasu!"
jiki ba karfi, zuciya a mace murus da zafafan kalaman dake fitowa daga bakin wace ya dace ace ta fi kowa taushi da sanyayawa, koda zafi ya kora ya dace ace an ji sanyi a karkashin ta sai gashi yauma da ta samu damar fakewa da wani fushin ta dandankara magangannun da bata sani ba sun jima da yin miki a zuciyar y'arta, sun matukar nisanta ta da yarinyarta , domin da tana da kula da ta gane babu wani abu dake shiga tsakaninta da yar da ta haifa da ya danganci na rayuwarta, sai wanda ya zamo dole ta sani...., ta rasa babar damar da ya dace ace itace ke rike da ita ba kowa ba a hannunta
fitowa ta yi tana share hawayenta, sai dai kirjinta ya riga ya rike mata, da dan sauri ta nufi baban falon dan ta san yanzu kam ba kowa a cen tana coshe bakinta
tana shiga ta barke da kuka da take tarewa da sauri ta nufi kujera zata haye ta darji kukanta ta ga RAUDA a dukunkunne tana nata kukan harda shasheka
da sauri suke goge hawaye, RAUDA na kallonta, itama tana kallonta
da kyar ta ja numfashi ta ce" Ke kuwa ke da wa kike kuka kuma?"
Salima ta dan sake zuba mata ido ta ce" Ke zan tambaya ke da na bari lafiya kalau?"
zaunawa Salima ta yi tana sauke ajiyar zuciya suka shiga fira, fira ta rayuwa, sama sama, firar kame kame dan su kawar da damuwarsu, har suka cika dare sannan suka wuce daki, da fatan samun barci, domin ita damuwa a riketa a rai ta fi haifar da ila da karancin barci.
......................................................
*washe gari*
tunda duku duku suka wuce asibiti wajen Bah
sun same shi zaune saman salaya yana jan carbi, a yau har ya samu ya yi sallah da kansa a tsaye kuma, sannan ko fuskarsa ka kalla zaka gane cewar sauki fa ya samu sai godiyar Ubangiji, hakan ya sa suka zauna Mah sai labari take masa shi kuwa yana biye mata yana ta faman dariyar na dariya, labaran da ba zasu wuce na Hajia, na YUSUF, na RAUDA, Salima, Abdul, da dai duk wani dake tare da su
MAH na murmushin gannin Bah na fadin shi dai yanzu tare zasu juya, YUSUF yace ba inda zai tafi sai ya warke sumul shi kuwa yana faman fadin ya warke me ya yi saura kuma, ama YUSUF ya yi shiru yana girgiza kafa ta ce" Aban YUSUF , gwara ka yi hakuri, dan nima na fi so ace komai normal sai mu je gida, abinda ka samu lafiya, ka ga zuwa lokacin jikin baban RAUDA shima ya warware sai kawai a sha bikinta dan ka ga jiya mun zauna da mai neman auren nata, kuma har ga Allah bashi da laifi, Aban Yusuf ka fa san mutumen nan, ina balaraben nan dake yawan sakawa ka cema Yusuf ya saida masa mota?"
YUSUF ya dago idannuwansa a hankali ya sauke saman Mah, shi dai bai san cewa baki na furucin abinda ba'a saka shi ba sai yau, domin yana ji yana gani sai ji ya yi ya ce" Dama maganar har ta yi karfin da za'a aura mata shi?"
Mah dake diban abinci a spoon tana yin bakin Bah da shi, shi kuwa yana wani karbewa kamar wanda baya iya ci da kansa ta kalle shi ta ce"
Azl 33
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE
💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*
💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)
Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique)
Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?)
Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo
ta kalle shi ta ce" Eh fa, ya yi, kuma tana son shi, Ni dama abinda ya dameni kennan, yanzu abu daya ne nake so dan Allah a maida hankali a kai, a yi bincike, dan ko dan gari ne ba zan bashi y'ata ba bincike ba, bale bako"
Bah ya yi murmushi yana rike hannunta da ta nufi shi da abincin ya ce" In dai Abdallah Balarabe kike nufi kar ki damu Hajia, dama na san shi dan har tushensa na je, ama zan binciko me ya zama yanzu dan dan adam akoy cenza hali, ki ce bana akoy sabga a gabana zan aurar da y'a "
y'ar dariya Mah ta yi, tana kallon YUSUF ya fice a dakin ta ce" ba karamin aiki ba Bah, domin ko kayan daki Bama son na gida na waje muke so!"
A lokacin da Mah ke fira da mijinta YUSUF ya fito coridor din dakin da Bah ke ciki ya yi tsaye ya saka hannayensa cikin aljihun rigar dake jikinsa ta jalabiya ya yi tsaye yana dan hangen mutane daidaikun da wani dalili ke fitar da su mai karfi daga dakunnansu domin tunda ya shigo aka dakatar da kowa aka fada masu na dan lokaci ne yanzu zai fita , hakan ya sa polisan dake tare da motarsa shi da Mah suka dan bazu sunna kai kawo