Showing 15001 words to 18000 words out of 188741 words
da ya dace
Nemanta yake yi hankalinsa tashe har bangaren HAJIA, inda ta ja tsaki rai bace ta ce" Ni kam yau na hadu da balakin wannan mata, to yarinya karama ce da zaka wani daga hankali dan baka ganta ba? Allah ya sa Allah ne ya rabaka da kaya!"
Jiki a sanyaye ya fito daga ɓangaren hajiar ya nufi motarsa ya tayar yana tambayar masu tsaron fadar a zuciyarsa yana tunanin ina ta nufa duba da yar tafiya tsakanin fadar da cikin baban gari Damagaran, inda gidanta yake, gashi dare ya yi kuma Yusuf ya jima da tafia
Sosai kirjinsa ke dokawa, hankalinsa gaba daya ba a jikinsa ba har ya samu ya karasa gidansa
Tun daga bakin kofa masu gadi suka sanar da shi HAJIA ta dawo hakan ya saka shi sauke wata irin ajiyar zuciya sannan ya karasa wajen ajiyar motoci ya parker watsetsiyar motar da YUSUF ne ya cenza masa ita cikin sababin da suka shigo ne sai da mahaifinsa ya fara murzarta kafin ya sake su kasuwa
A sukwane ya karasa baban falonta yana ambaton sunnanta
Shirun da ya ji ya tabbatar masa bata nan dan haka ya nufi karamin falonta na cen cikin dakinta
Zaune ya sameta saman kujera waya a kunnenta tana magana a hankali, wanda ya tabbata da Yusuf take maganar dan idan ka ga ta maida hankali tana magana cikin nutsuwa da tausasawa sosai da yaronta take magana shi kuwa yana zuba mata rigima
A tausashe ta ce" Ka tabbata ka daina fushin? Idan baka daina ba nima fushi zan yi fa?"
Yusuf ya saki dan murmushi yana jin nutsuwa na shiga dukan gaban jikinsa, shin yaya suke tunanin zai iya gannin darajar duk wani mai son wulakanta masa ita? Idan ya rasata a duniya shi ya san ya gama lalacewa, ko a yanzu ya san cewa adu'arta ke tafe da shi ba komai ba
A Nutse ya ce" Na hakura Anna, ina gidana yanzu haka"
"Allah ya maka albarka ya tashemu lafiya"
Da kula da tarin kauna ya amsa ya katse kiran har yana sauke ajiyar zuciya ya lumshe idannuwansa yana jin ciwon irin yadda ake saka masa uwa a gaba a wulakanta saboda shi
A hankali mahaifinsa ya karaso inda take zaune ya zauna ya mika hannu ya riko lalausan hannunta yana kallonta ya ce" Me yasa kika tafi kika bar ni? Wa ya kawo ki? Kin san irin yadda hankalina ya tashi kuwa?"
A hankali ta janye hannunta daga cikin nasa tana kallonsa ido cikin ido a tausashe ba da rigimar komai ba ta ce" Aban Yusuf, me yasa tsanarka a kan yaron nan ke hauhawa a kulun ne?"
Dan tsai ya yi yana kallonta , a hankali ya koma ya gyara zamansa cikin kujerar still yana kallonta gannin amsarsa take jira
Da kula sosai ya ce" Ban tsane shi ba, ke kin san shi din shine mafi soyuwa a zuciyata a cikin yayana, ina yi masa haka ne dan ya ji haushi ya daina abinda yake yi, me amfanin kana aikata laifi kuma kana yi a idon kowa? Ai ko Allah ya Hanna ka ringa tonawa kanka asiri, gashi baya son danginsa, ban san me suka yi masa ba baya son su, ace du irin yadda HAJIA take da shakuwa da shi ba zai iya sonta ba? A kansa kadai HAJIA ke yin kuka a duniya ama fir ya kasa ganewa ya rabeta ko dan tsufanta?"
Kai HAJIA AMEERAh ta cire daga duban gefe ta maido kansa tana dubansa, a Nutse ta saki dan murmushi a tausashenta ta ce" Ka yi hakuri ka ringa duba furucinka a kansa, saboda mahaifi kake a wajensa , ko me yake aikatawa fatan shiriya shine ya dace ya fito daga harshenka, ka yi hakuri ka fi karfin zuciyarka domin baka sani ba abin ya fara fin karfin son ka ga ya dawo hanya ya koma abin birgewa wa zuciyarka yin daidaya da zuciyarsa"
A hankali ta ajiye maganar kafin ta dago ta saka idannuwanta tar cikin nasa ta ce" Me kake jira daga wajensa ? Ina ganin shi yana sara da duban bakin Gatari , da ace irin halayan da ake masa zai yi da an shiga uku, shin wani d'a za'a zagi mamansa yana tsaye bai dauki mataki ba? Fin karfin sa na yi shi yasa shi kuwa ya kaurace dan kar ya aikata aikin da za'a Dube shi da shi, me yasa bakwa masa adalci ne? Me yasa bakwa dora abinda yake iya ji a zuciyarsa kamar yadda kuke iya ji? , me yasa kuke gagawar yanke masa hukunci idan ya wulga koda bai yi tari ba?" Wannan karronma a hankalin ta ajiye maganarta sai dai dubanta na iya fasara daf take da tsinkewa
A Nutse ta dora da fadi " Yau da gobe nake guje maku, dan ba zan ware kowa ba, idan Ni na zamo takalmin takawarku shi a abu mafi daraja yake kallona, in ma me na aikatawa ahalinku wanda kai ake iya yafe maka Ni ake kallona a matsayin *AZAL* din da ta afko ahalinku da cikin da na ba kaina wace ba za'a iya hakuri a Dube Ni ba, shi yana dubana a mutun mafi daraja a duniyarsa, shin yaya kuke so yaron da kuke kiran uwarsa masifa shi ya zamo maku mai biyayya a gabansa? To ai koda ace shine shegen da muka yi Ni da kai ba zai taba fa......."
"AMEERAH!" Hon Bello Muctar Gali ya fada yana dagowa daga jinginar da ya yi hankalinsa na neman tashi zuciyarsa na bugawa, domin tunda suke da ita du irin abinda yake faruwa bata taɓa dubansa ta nuna bacin ranta ba, kai komai bata fadi bale har ta tado abinda shi ya birne yake kuma zaune da matarsa da zuciya daya da so da kauna Duda ita ya san ba lallai in ta iya manta baban abin da ya shiga tsakaninsu a zamanin samartaka ba, sai dai ga dukkan alamu abin na ranta har yau kunnayensa ke jiyo masa maganar dake daf da dauke nutsuwarsa
A hankali ta zuba masa ido kafin ta tari numfashinsa tana dan Bude lumsasun idannuwan da yaronta ya yi gado a wajenta tana kallonsa ido cikin ido a kausashe sosai ta ce " BELLO, idan maye ya manta uwar d'a ba zai yiwu ta manta ba, yayana da aka ciro a dakin tiyata aka nunan sun mutu ba zasu taba guguwa a zuciyata ba, ba zan taba mantawa ba!"
Sai kuma ta sasauta muryarta tana jingunuwa da jikin kujerar nan a hankali ta ce" Ina daukan zamana a ahali irin naku matsayin jarabawata ina kuma rokon Allah ya zamo silar yafewar laifin da na aikata, sai dai ka sani ina guje masu yau da gobe a kan D'ANA!, i love my love fiye da raina, ku kun san biyayar aure da shi ke rikeni ba dan bani da yadda zan yi ba!, Ni ce AMEERAH (GIMBIYA) ta DAMAGARAM, banbancin mai nisa ne!"
Daga nan ta yi shiru tana jin kanta na neman yi mata ciwo
Hon Bello kuwa sai ya rasa shin mamakinta yake ciki ko firgicin halin da take ciki? Lalle a yau an kaita bango, ashe itama tana iya nuna bacin rai a kan abinda ake yiwa Yusuf har haka?
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya mike dan ya dauko mata maganinta da ya zamo kulun sai ta sha take kwonciya
Sai da ya je ya dauko ya kawo ama fir tace ba zata sha ba, wannan shi ya karra daga masa hankali domin idan ta yi fashin sha da wahala in bata KWONTA rashin lafiya ba, a hankali ya so sake fahimtar da ita ba zai taba iya kin gudan jinninsu ba, ama akace ka guji fushin wanda baya gagawar fushi, cikin wani bacin ran kafin ta mike ta nufi dakinta ta ce" Ka shiga tsakanina da A'isha!, ta fita a hanyata, abinda na hadiye na shekarun baya ba zan iya hadiyewa yanzu ba, kanwa take a wajenka , koda yaya ce ina iya dakatar da ita bale kanwa, ta guji budar bakina dan idan ta kirayi YUSUF mazinaci mashayi bata san me zan kirayi nata ya'yan ba wa'inda ba hasashe nake yi ba ko Kazafi, tana yawan kirana *AZAL!* idan aka bibiyi tarihi kalmar AZAL ta yiwa ahalinta kadan , a kan YUSUF babu abinda ba zan yi ba ciki harda rabuwa da UBANSA!"
Daga nan ta yi dakinta ta rufo ta saka ky ta murza da karfi sannan ta karasa wajen gadonta tana rike kanta ta KWONTA jiri na neman summar da ita daga kwoncenma
A falo kuwa da kyar Mahaifin Yusuf ya iya samun waje ya zauna yana dafe kansa da hannayensa bibiyu
A hankali ya bude idannuwansa sakamakon tuno ranar da yayansa ya fito da wani zannin gado a hannunsa rungume da jajirai biyu farare sal masu kama da shi tak tak Duda jajirtakarsu kamar ya yi kaki ya tofar kamanin har sun bace ko dan Allah ya nuna masu cewar ba gardama abinda suke gudu nasu ne? Yan jarirai sun yi fari fat na alamun ba rai a tare da su ya nuna masa, bai ko bashi damar runguma ba ya fice da su yana fadin abinda aka tsara za'a sanarwa duniya cewar ba kumburin cikin haihuwa bane ta yi dawainiya da shi, kumburi ne na kari dake girma tamkar cikin haihuwa yana ji yana gani bai san inda aka birne masa yayansa ba, haka uwarsu ko ganninsu bata yi ba aka yi rufa rufa ga zafin haihuwa na cs ga radadin rashin ƴaƴanta aka dawo gida aka daura masu aure a ranar tare da wasu matan biyu, wa'inda HAJIA ta zaba masa yana ji yana gani bashi da ikon furta ko kalma daya kuma aka nuna aurenta shine karshen daurawa kai fin karfi dai aka nuna ba zata tare a gidanta ba a kalla ta kusan shekarewa a tare da HAJIA , galazawa babu irin wace bata gani da Hajiar da kanwarsa A'isha, yayansa kuwa dama basa ko ga maciji da ita, shi dai bai nuna mata tsana ba ama kuma bai nuna mata kauna ba, a wajen su HAJIA kuwa nan ta ringa tsintar sababin sunnaye masu girgiza zuciya, gashi a lokacin ba damar ta je wajen Tata mahaifiyar saboda ta yi fushi da ita sosai, sai a rasuwar mahaifinta suka amsheta suka yafe mata har suka janyota jikinsu, ama Duda haka babu ruwansu da damuwar dake damunta na dakin mijin da a ganninsu ba gidan aurenta bane, gida ne mai hatsarin gaske , gida ne da jita jitar da ake yadawa a kansa ya sa da yawa ke masa wata irin fasara, su tasu sarautar mai hatsarin da baki ba zai iya misaltashi bane, wani abin ne a bine a ahalinsu ya sa haka ko Allah ne ya kadarto masu haka a rayuwarsu? Allah shine masani, ama yannayin matarsa na yau ya girgiza shi fiye da tunanin bawa
Menene bata gani ba? Bata taba nuna masa ba
Idan yana fada ma Yusuf takan kauda kai ta yi murmushi ne ta ce" Sai addu'a Aban Yusuf"
Ama a yau ta fadi abinda yake gannin shi dai bata yi masa adalci ba
Shin yaya take tunanin zata haifo masa d'a tsatsonsa ya tsana? Yau ko ba nasa bane in dai daga jikinta ya fito ba zai taba tsanarsa ba, bale nasa ya Allah yaya zai iya tankwasa zuciyar wace bata cika fushi ba?.......
🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔
Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*SAJIDA NIJAR*
*PAID BOOK*
_Bismillahir rahamanir-rahim._
*7*
*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*
*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
KARKU BARI A BAKU LABARI🥳
Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*
A gidan su RAUDA
Tun karfe shida na safe hayaniya ta kaure a tsakar gidan, wace ta hannata mikewa bale ta je ta samu ta dauro alwallah ta gabatar da sallar asubahi, rikici ne wanda yake tashi sama sama, fada ne irin na matar mashayi da mashayi, fadan da farkonsa aka sani ba'a san karshensa ba, fadan da du tsiya da zarar ya nuna zai rabu da ita take komawa ta yi mikis kamar ba ita ba, du gorin da take yi, du masifar da take yi cewar an hadata da balaki an aurota ba'a ciyar da ita, ba'a shayar da ita, an kawo mata rikon ya'ya an zuba mata irin tsiya gayar tsiya ba zata iya ba fatanta Allah ya rabata da masifa da BALAKI, domin auren Umar masifa ne da BALAKI ba komi na, ba karuwa sai raguwa , babu farin ciki sai bakin cikin rayuwa, na kulun hauhawa yake yi ba raguwa ba, da zarar ya nuna wai su saki hannun junna mana sai ta shige daki ya labe ba zaka kuma jinta ba sai ya fita ta fito ta wulakanci su RAUDA da dan uwanta wanda tsoron maman nasu ya saka ko muryarta ya ji sai jikinsa ya kama rawa ya shiga neman wajen buya
Ido Rauda ta rintse sakamakon wata ashariya da Mama ta kyatsa tana fadin" WALAHI baka isa ba, baka isa ba Umaru, kudin da nake binka ai sun fi haka, a kan me zaka ce zaka siyawa RAUDA kayan makaranta da kudina? Kar ta yi karatun mana, karatun nata da ba anfanar uban kowa zai yi ba, yawon banzan da take fita ne kake kira karatu ko me kake so ka daukeni? Yau da ace wannan yarinyar ba y'ar zumunka bace har na yi maka wata fasarar, ama Duda haka zan zuba ido sosai dan WALAHI karya ne ba'a yi y'ar da zan gogi arzunzumi ta goga ba.... ba z........."
Wani irin karan duka da ya shiga kunnayensu ya saka su duka biyun rintse idannuwa, hawayen da RAUDA ke rikewa suka samu damar fita da gurbin idannuwanta shar masu zafi da radadi, shi kuwa kannin nata ya rarafa ya boye a jikinta jikinsa na rawa kirjinsa na dokawa kamar zai summa
Ihun kukan Mama da y'arta ke tashi sama sama tana fadin " Allah ya isa tsakanina da kai, dan na fadi gaskiya zaka dakeni? Menene ba'a yi a duniya yanzu? Ni dai da RAUDA da iyayenta sai Allah ya mana hisabi, tunda suka fadi suka mutu ka zama mashayi ka kawo min ƙatuwar budurwa ka saka min ga wani dama da nake riko, ba zan yafe masu ba kuma kaima ba zan yafe maka ba dukana da ka yi, kuma na fada sai na saka ido a kanku dan ban yarda da mashayi ba, in kuka sha kun san abinda kuke yi ne? Ba zan kyaleka ka wulakantani ba Umaru!"
Shi din da kansa a tsayen da yake yana haki zuciyarsa tamkar zata balo kirjinsa ta fito hawayen ke wanke masa fuskarsa
Gannin idan ya zauna yana iya kasheta ya saka kansa a uku ya saka ya juya kansa na sarawa ya nufi hanyar fita
A lokacin da ya fito waje idannuwansa suka sauka a kan makocinsa da kuma limamin anguwarsu sunna tsaye daga nesa da gidan kadan ama ga dukkan alamun gidan hankalinsu yake
Yana yin ido hudu da su kunya da tsananin takaicin kansa suka rufe shi, a hankali ya dakata ya so juyawa sai dai makocinsa ya ki bashi wannan damar ya karaso inda yake tsaye ya mika masa hannu yana masa Salama
Hannun nasa ya kalla, sai ya ringa jin dari darin bashi nasa dan na makocin nasa a wanke tasss ga tabjinsa a hannunsa yana ja har wani kanshi yake, shi kuwa nasa harta miyar da ya ci jiya da dare bai wanke ba, sai kunya ta saka shi kallon nasa hannun ya nemi nokewa
Karasowar liman ya riko hannun nasa suka yi musabahar dole yana kallonsa shima a tausashe ya ce" Shin ka yi sallar asubahi?"
Wata kunyar ce ta sake kama shi, to rabonsa da yin Sallar asubah a