Showing 129001 words to 132000 words out of 188741 words

Chapter 44 - AZAL HAUSA NOVEL

sajida   

12 Jan 2025

9839

din maganin Mah ta mike kasa kasan itama ta furta" A'a Mah, i'm fine, sai kin zo"

Daga nan ta juya ta fice a falon , zuciyarta a cinkushe, tana jan carbinta ta karasa bangaren Mah lokaci daya ta je wajen kujeru ta zauna tana dan yatsina fuskarta, hakan ya ba dimple din kusan idannuwanta damar lotsawa

Da dan takaici ta fitar da numfashi kadan daga bakinta a hankali ta furta" Aikin banza marar tarbiyya, ki shigo ki tardo manyan mutane ki kasa gaishe da kowa, ana magana kina kada kafa a gaban iyayenmu, kuma ki ce zaki tafi baki gaishe su ba? Ni bana son rashin da'a waye sa'anta a nan? Sai wani firirita take yi da takamar an san ita Wacece? wace ke banda shara ajebo?, abu daya ya tsallake fuskarki daga hanuna Mah ce!, in ba dan wannan ba da na gwada maki Ni din wace da kika zagar min uba, wace ke kuwa banda mace marar aji, wai gidan aure ne aka kawo ki kina azarbabi haka? shirme wata nawa da auren kina nan kina shirme?, mtssssss auren naku da babu wanda ya dama?...."

(Mu dai ya dame mu☹️)

Sosai take fada a zaune har ta cinye lokacin da ita da ganta bata ankara ba sai da ta dago dan ganin time ta mike da sauri ta nufi kicin din tana tunanin abinda zata dafa, domin haka kawai take jin ita kanta ya shafe ma bata san me zata dafa bama!


A cen inda ta baro su Mah,Hajia ta jima tana yiwa Amnah nasiha da nuna mata ya dace ko me ta nado a turminta ta gyara dakanta dan uwar mijinta uwa ce a gare ta kuma bata da wata wace ta fi ta

Mah na zaune ne tana bin su da kallo, ama a ranta tunani ne kala kusan hudu ya hadu ya rarraba mata yannayi

A lokacin da akace ta bi shi, da farko ya so dakatar da hakan, domin a yannayin da ya yiwa fuskarsa ta gane ya so ya hanna hakan, sai dai idannuwanta sun nuna mata wani abu, domin a lokacin ne ta ga ya kuma kallon Baby, bayan kallon da ya mata fiye a irga tunda ta zauna, kallon da ya bambanta da wanda yake yiwa SALIMA, kallon da ta fadawa Bah tun cen baya ya nuna mata ba komai bane kar su ce wani abin ne, tana hankalce da shi a lokacin da ya ga ta dago da sauri sai da ya yi murmushi sannan ya nuna su je!.....Hakan ya matukar daure mata kai

Sai abu na biyu, abinda Baby ta yi!
a zamanta da baby, zata iya cewa yarinya ce mai hankaltuwa da abu komai kankantarsa ko girmansa, ta kasance mai kwontar da hankalinta a kan komai, abu komai kankantarsa baya shige mata, ta yaya Baby zata dube su tace wai bata gane ana nufin Amnah ce matar YUSUF ba? me yake faruwa da Baby ne?, a irin abinda ta ga yau ta yi, zata iya rantsewa bata taɓa gannin ta yiwa ko bawan gidan nan ba, wani yannayi mai tafe da rigima da neman fitina da wani yannayi mai zafin da kuma alamun son fashewa da kuka?......Kar dai duk irin yadda ta ringa bin su da tambayar nan cewar kin amince da auren wane? ka amince da auren wance dan kawai su yi kokarin kwatanta mata da wani abu komai kankantarsa suka yi mursisi dan su raina mata wayo ne?
....
Sai abu na uku, yannayin Hajia!
Hajia uwa ce a wajenta
hakan da ta sakawa ranta ya sa take zaune da ita duk rintsi
a rayuwa ta sha wulakancin Hajia wanda kare ba zai dauka ba
a yanzu yannayin nan da ta samu sabo yana so ya saka ta fito fili ta tambayeta sanyi take son yi a kanta dan ta sakankance ta yarda cewar itama mutun ce sai ta sake da ita ta sake masheta baiwar da bata da ubangida?, da ace Hajia zata dubeta a matsayin y'a da ta dora kanta a saman cinyarta ta yi mata kukan dake kirjinta na tsayin shekaru ko komai ya wuce a ranta, sai dai zuciyarta na cike da matsanancin tsoron kar baya ta dawo gaba a sakata yin faduwar tasar da ba zata iya gyaruwa ba!

dayan abin kuwa yarinyar nan ce dake gabanta zaune
Tun daga kan yarinyar har zuwa dan yatsar kafarta ta gama gane cewar yaronta ya samu daidai da zamaninsa kuma Allah ya hada shi da irin classs dinsa....., haka kawai take cike da kukan zuci, wanda zuciyarta ta fi bata amsa daya tak *ME KIKE TUNANI ANDIYA? KALAR ZAREN KALAR KAYAN, AI DAMA DA WAHALA ALLAH YA HADA ABINDA BA DAIDAI DA JUNNA BA, TA YIWU ITA DIN RAINONSA CE!* , walahi wannan kalamai su ke gigita mata duniya, kuma ta fada ta karra da babar murya domin ba zata iya yin mugun son kai fiye da kima ta yadda zata take abinda ke gabanta ba,
Amnah, tana bata tsoro
yannayin Amnah na firgita tunanin ta, bata san me yasa ba, ta dai san cewa ba bada kama ne ke gabanta ba, zahiri ne!

Sunne abubuwan da suka hadu suka yi mata kwawanya a kwonyarta

"AMEERAH, ki je bangaren ki da ita, dan bata da wani wajen da ya wuce cen, zan sa a kawo mata suturarta da ta dace da kaurarta, zan sa a je a kimtsa mata bangarenta yadda ya dace, idan aka yi sallar isha'i zan saka datijawan mu na arziki da kannen ta su hadu su raka ta, ki yi hakuri da abinda aka yi maki da farko, ina mai tabbatar maki na za'a maimaita ba, " Hajia ta ajiye maganar a nutse, sannan ta sake kallon Amnah dake zaune, kanta a sade, domin duk yadda ta so yi masu kiririta da bin su da ido cikin ido ya gagareta, kai abinda ke kai kawo a cikin zuciyarta ya fi komai yawa, dan haka sai kawai ta sada kanta tana tunanin abinda ke iya fitar da ita

Da kuma Hajia ta ce" Kamar yadda na fada maki, in dai zaman lafiya kike so da mijinki, ki girmama mahaifiyarsa, duk d'an halak ai inaga zai girmama baba koda ba shi ya kawo shi duniya ba ko AMNAH?, ki girmama ta, zaki ji dadin ta fiye da kowa a gidan nan, dan kuwa Ni sheda ce , ki tashi ki bi ta"
Hajia ta idashe zancen tana mata nuni

A hankali Mah ta dago dubanta ta sauke a fuskar Hajia,zata iya cewa ta jima tana yin sharar shanyen nan, domin lokuta da dama koda bata so bakinta ya fada ba idan tana yin fada da bada misali zata yi misali da ita ne a matsayin a yi koyi da halayarta....., abinda ke kanta a yanzu yanzu shine Hajia ta kasa yafe mata abinda suka aikata ita da d'anta ne,
da ace ta yafe mata, da ta dubeta tuni, da kuwa ta ji dadin rayuwa tare da ita

A hankali ta mike saboda zaman da ta jima tana yi, ta dan rage tsayinta a tausashe ta furta" Allah ya saka da alkhairi Hajia, mun tafi"

Hajia ta dubi Mah, zuciyarta na tsintsinkewa da lamarin sirikar Tata, lokuta da dama sai ta yi yunkurin yin wani gagarumin abin da zai shirya tsakaninsu sai ta rasa ta yaya? ta ina zata fara? bale a yanzu da YUSUF ke kan matsayin nan, takan yi tunanin idan har ta nuna wani abu daga ita din har sauran jama'ar zasu yi tunanin ɗan Yusuf ya zama sarki ne take neman sulhu da Mahaifiyarsa, ba zasu taba yi mata uzuri ba, a matsayinta Na uwar da tashin hankali ya sama rana tsaka a cikin kishiyoyi da miji da tarin makiya kan d'an da ya fi kowani yaro kokari da zafin nema a cikin y'ayanta, d'an da ita da kanta ta gama sakawa ranta cewar da izinin mai sama shine jagaban garinta, ya zo mata da gigitacen labarin da ya hargitsa tunaninta, ya kuma ja ya tsaya, ta ja ya ja , ta yi ta yi kan ya hakura da ita ya nuna gwara ya mutu da haka, duk irin tsatsauran matakin da ta dauka a kansa ya ki yin hakuri, karshema ya kamu da zazafan ciwon zuciyar da a yanzu haka emotion na dadi ko na wuya ke rikita masa lissafi har ya fita a hayacinsa ba? ba zata yi mata uzuri ta auna a kanta ba, ta tabata ko MAH sai ta fasarata , shi yasa take ta kai tubanta wajen Allah, dukda ta san cewar Allah baya yafe laifin da bawansa ya yiwa bawansa, sai idan bawan ya yafe, tana rokan sa ya bata hanyar da zata daidaita tsakaninta da *SARAKUWAR TA* ne.


A tausashe Hajia na duban Mah ta ce"


(RAUDA kin bar wajen gatanan tafe☹️)


morning alll......,

Azl 46
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*

Bismillahi rahamanin rahim

Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*

💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)

Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique)

Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?)

Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo




A tausashe Hajia na duban Mah ta ce" Allah ya hutar da Gajia Anmi MALIK"

Kunya ta ji ta kama ta, ta sake sada kai ta yi murmushi sannan ta mike ta yi gaba a nutse tana dan daidaita tafiyarta dan bata so ta bar AMNAH nesa sosai da ita

AMNAH kuwa, tana biye da ita ne idannuwanta na sake bushewa da tunanin dake cikin ranta, burinta daya ne kwal ya samu kanta ita kadai dan ta yi abinda zai bata damar Sannin Wacece yarinyar nan, domin ta daukarwa kanta alkawarin koda ace y'ar uwarsa ce jinni daya sai ta shayar da ita mamaki ta hanyar nuna mata kofa bata auri ƴaƴanta ba ita ba sa'ar yinta bace, bale ace tana auren MALIK!
Tana tunanin nan suka karaso Mah ta bude ta shiga tana salama Amnah na biye da ita

A lokacin Salima na falon Mah tana aiki da computarta, dan ta tarda RAUDA kicin ne su yi aikin tare sai ta same ta yau bata son magana, domin tana aikin ne ba tare da tana kula firar da take mata ba, shi yasa ta taho ta yi zaune abinta ta barta da yan kurumcinta

Da kula Mah ke amsa gaisuwar da Salima ke yi mata, ta dan ja tana tunanin inda ya dace ta kai AMNAH, a cikin dakunnan wajen

Ta so kaita dakin RAUDA, sai ta nufi dakin kusan na RAUDAR da ita a nutse ta saka ky din da Salima ta dauko mata a dakinta ta bude tana fadin" Bismillah, bari mu gani ko sai an sake gyara shi? na san dai ko jiya an yi gyare gyaren dakunnan dake rufe"

Salima ta fara shiga, ita kuwa Amnah ta yi tsaye a waje, dan ba zata shiga ba sai an tabatar mata wajen clean ne dan gaskiya ba zata iya shaƙar kayan mura ba

"Bismillah aunty Amnah" Salima ta fada bisa umarnin Mah

shigowa ta yi tana bin dakin da kallo sannan ya sauke dubanta a kan Mah, kamar yadda ta saba kallon mahaifiyarta tsai cikin ido ba wani risinawa haka ta dubi Mah din,dan bata san ita hakan Bama wani abu ne dake iya sakawa a ga rashin tarbiyarka ba kallon baba cikin ido

Da kula Mah ta ce" Ki zauna a nan , dukkan abin bukata za'a kawo maki, idan akoy wani abin da kike so ki sanarwa kannenki, ko ki sanar min, kina da bukatar kitso ko kunshi ne?......" Mah ta karashe tana sake duban kaffafuwan Amnah, dan da ace sun yi wani sabon da ya dace ta yi mata katsamandan a al'amuran ta, da tace da ita ki yanke faratunan nan ki tsaftace kanki ko dan sallar ki, sai dai a yanzu wannan yarinya mata take a wajen d'anta, matarma bakuwa, mai cike da abubuwan da suke boyayu a duniyarta

Itama kunshin dake hannunta ta bi da kallo, wanda bai jima da aka yi mata shi ba, domin mahaifiyarta bata barinta neman komai ta rasa a gidan nan, duk wani abin da zata bukata za'a turo mata ne kai tsaye, Mamanta ta fada mata kar ta yarda a ga kazantarta komai kankantarta dan a haka za'a nemi a rainata

kai ta girgiza tana sake duban Mah sannan ta nufi wajen bed din dakin ta zauna hankali kwonce, hakan ya sa Salima dan zarro ido tana kallonta , ita kuwa ba wani damuwa ta ce" A'a, bana son kunshi, ina dai son gyaran kai da mak'up"

Mah ta yi dan murmushi sannan ta juya ta fice

Tana fita Salima da ta gaza motsawa ta nufo ta da dan mamaki ta ce" Aunty Amnah, yaya zaki zo ki zauna tun Mah na nan tsaye a saman gado? har yanzu fa bakuwarta ce ke kuma hausawa sukan ce in dai da kunya y'ar halal har ta mutu tana jin kunyar sarakuwarta!"

Itama da mamakin tana kallon Salima, dan zata iya cewa a duniyarta tana mamakin Salima ainun, tunda ta san y'ar kishiyar Mah din ce, kuma a gaskiya sukan dan yi fira idan ta kama bale ba laifi tana girmamata sosai, shi yasa itama take yinta, da kula ta ce" Kunya? to meye a ciki dan na zauna?"

Salima ta dan dafe habarta, a nutse tana kallonta ta ce" Aunty Amnah, kar ki ce meye a ciki dan kin zauna, kin san ana girmama mahaifiyar miji, bale wannan din koda bata haifi mijinki ba ko a gari kika ganta zaki sada kai idan zaki yi mata magana Dan matar sarkin garinki ce fa, a irin yadda muke da girmama sarakuna tana da kima sosai a idannuwan duk wani mai mutunci fa"

"Ya Allah, Salima wai meye na yi na rashin girmamata? zama? to ai Ni Ko ubana ke tsaye ina iya zaunawa normal ne bale wace bata haifeni ba, Ni walahi mamaki kike bani Salima, matar nan kamar ba kishiyar mamanki ba, kina kallo yadda ta maida maki uwa baya a cikin gida ama ke itace abar ki raba? in dan kudin d'anta ne kema ai yayanki ne ina gannin kina iya takama da kudinsa ko? walahi ki farka tun wuri, kishiyar uwa ba zata taba sonki ba!" Amnah ta fada tana hangen wace ke neman izinin shigowa

Salima da ta yi mutuwar tsaye ce ta iya juyawa ta bada damar a shigo

shigowa ta yi ta duka har kasa tana miko jakar Amnah sannan ta juya kanta a kasa, dan a yanzu a gidan nan idan akace an aikeka wajen gimbiya ka kama adu'ar Allah ya raba ka lafiya da ita kennan , dan abu kadan zaka yi ta saka ka a uku, ta janyo maka tashin hankalin da zai sa ka tsani kanka ka tsani zama a masarautar

Jiki ba karfi Salima ta kawo mata jakar ta ajiye mata, tana dubanta a tausashe ta ce" Eh lalle ba ita ta haifeni ba, kuma matar mahaifina ce , sai dai Ni tunda nake da ita alkhairinta na sani ba sharinta ba, rayuwa na juyawa kala kala, na yi wayo tun daga yarinta, zan iya ce maki ban taba haduwa da abinda zai sa na ji ta daukeni kamar wadda bata haifa ba, kin san menene aunty Amnah? ita rayuwar kanta idan ya zamo ka sakawa ranka kowa na iya cutar maka shikenan, ka shiga uku, domin babu wanda zaka yarda da shi ko ka yi mu'amala da shi da zuciya daya, bale idan kai dai a rayuwa tunaninka za'a yi maka asiri ko an yi maka ne? to in sha Allah ka ginawa kanka mugun ramin da zai hannaka kwonciyar hankali........, Bana tare da Mah dan arzikin dake tare da ita, idan arzikin ne kamar yadda kika fada iya wanda ya zuba min a matsayina na kanwarsa ya isheni rayuwa, bale ban cika saka buri a raina ba, sai dai jinina ne shi, mahaifiyarsa kuma yawa ce Amnah....ki huta lafiya"

Daga nan ta ajiye mata jakarta ta fice, tana jin gaba daya matar yayan nata na fice mata a rai, dan walahi tunda ta zo take son gane wace ita? ta gane wasu halayar ama bata gane wasu ba , a yanzu kam tana kukan wannan jigo da aka yiwa gidansu, dan bata tunanin in har ya isa a kirayeshi bango , ko kuwa uwa mabada mama!


Tana fita itama ta ja dan siririn tsaki, kasa kasa ta furta" Dama yaya zaki yi ya kasa isarki? daga ke har uwarki abinda ke iya isarku abin siyan jakata ne, kuma fa ban ga laifin ki ba, kawai dai mamaki kike bani , ama kuma kina da wayo daidai misali tunda kika iya bin inda zaki ji zuma ziryan ba mai haɗe da shuga ba, sai dai dukanku zaku yi bayani ne,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login