Showing 75001 words to 78000 words out of 188741 words

Chapter 26 - AZAL HAUSA NOVEL

sajida   

12 Jan 2025

9835

abin fitsari da abin miya gaja gaja ta rungume shi a jikinta a birkice murya a rarrabe tana fadin"
Azl 26
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*

Bismillahi rahamanin rahim

Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿ•บ๐Ÿ˜ .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*

๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu ๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ๐Ÿ’ƒ๐Ÿผmusamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)

Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ (magnifique)

Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account ๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ (da wa kika ja Madame?)

Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜ sai kun zo



Tana fadin " Abdul, Abdul, Abdul Nine, auntynka ne, kalleni Nine fa"

Tunda ta rungume shi, ya shiga maganganu hadi da kuka, magangannu irin wa'inda mutun kan tarawa idan wani wanda ke hanawa a wulakantashi baya nan aka wulakanta shi idan ya dawo dan ya sanar masa
Ido a rufe hawaye a fuskarsa yake fadin" Auntyna, auntyna ko? Sai ta zane ku, ku dukan ku, idan ta zo sai na fada mata Salaha ta zane Ni, ta hanna min tuwo, ta hanna Ni zuwa makaranta, dan ta ce na mata wanki nace ban iya ba ta saka na yi ta zane Ni, ta saka na yi shara, Abdul bai iya komai ba ama tace sai na yi sai na yi wanke wanke, har na kone hannuna da mama tace sai na hura wuta, sun ce Abdul maye ne sai kallon mutane, bayan auntyna tace Ni ba maye bane, sun ce wai sai sun yankani idan baki zo ba, kin gansu sun doke Ni, sun rufe daki sun barni na kwana a waje , ina tsoro ina tsoro ina tsoro......"
Sai kawai RAUDA ta fashe da kuka, a rikice ta dago tana kallon Mama wace ta karaso tana son kwalkwatar Abdul dan ba zata taba bari ta tafi da shi ba, domin idan ta tafi da shi ta san shikenan kuma labarin mijinta ba zata kuma ji ba, ita kuma walahi wannan abin sai ya haukatata, rashin Umar tuni yana daf da zautar da ita,

A rikice ido a kausashe Rauda ta yi mata nuni da yar yatsarta ta ce" idan kika kuskura kika taba hannunsa , yau sai na yi kason ki!"

Ido Mama ta kwalalo tana ja baya tana kallonta, dan tunda suke, tunda Allah ya hada zamansu bata taba yi mata magana ido cikin ido da tabbacin furucinsta irin na yau ba, duk irin yadda kirjinta je hayaki a kan maganar mijinta sai ta kasa kwatar yaron da take gannin shi kadai ne hanyar da zata rika ta rike wuyan RAUDA sai yadda ta yi da ita ba

RAUDA ta dago fuskarsa tana kallonsa ta ce" In zane su? Kana so in zane su?"

Abdul ya ringa gyada kansa yana kuka yace " Aunty? Ke ce ko? Aunty ki zane Salaha, kin ji? Tace Ni ne wai mai kama da aljannu, kuma tace min mahaukaci......"

Ai bai gama rufe bakinsa ba ta maida shi bayanta a guje ta ridi Salaha

Kafin Salaha ta samu ta gudu daki Rauda ta yi mata rikon da ta fi jin tsoro, ta rike mata wuya daf ta watsota waje

Salima ta zarro ido abin na neman fin karfin ta tana neman kiran sunnan RAUDA wace ta shake wuyan Salaha sosai ta sake zarro ido gannin Mama ta dauko katon ludayin miya irin tafkeken nan ta daga ta makawa RAUDA shi a bayan kanta

Ihu Salima ta saka, da gudu ta nufo Mama tana neman rike ludayin ama sai da Mama ta sake makawa RAUDA shi tana fadin" Na maki alkawarin nice ajalinki, sai na kashe ki!, ba kin samu gidan sarauta kin labe ba? Dole zaki dawo inda nake ki nemo mana abinci ko ciyar da mu , dole zaki fito ki nemo min mijina , munafuka algunguma shegiya mai tafe da *AZAL* a duk inda kika shiga, iyayenki dan sun haife ko masifa kala kala sai da suka shige rami gaba dayansu koka huta, Ni da aka kawowa ke gashinan kulun cikin balaki nake karshe wanda ya dauko kin zaki jawa a rasa inda yake?, karya kike yi mai kama da kulba sai dai na kashe ki na kashe banza!"

A rikice Salima ta yi waje, dan abin ya fi karfin ta, kuma abinda ya bata tsoro du irin ihun da suke yi makota babu wanda ya leko ko wa'inda ke waje babu wanda ya shigo

Da gudu ta karasa wajen direba jikinta ma rawa ta shiga nuna masa tana haki tana fada masa lokaci daya kuma tana fadin" Ta kashe RAUDA, ta kashe ta, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, ka kira police, ka sanarwa mai martaba kar Mah ta ji, kar ka sanarwa Mah!"

Magana take yi hankali tashe tana son juyawa gidan da sauri direban YUSUF ya fito daga motar ikon sauri ya ce" Hajia, ki dan tsaya kar k8 shiga bari na je"

Kana gannin yadda yake magana ka san irin mutanan nan ne da basa tsoron a mutu, direbansa ne wanda ke kai Mah anguwa idan baya nan, mutumensa ne da dalili ya haษ—a har ya dauke shi aiki

Yana fada ya nufi gidan da sauri yana kautar da mutanen dake tsaitsaye, ita kuma tana biye da shi a guje dan gaba daya anguwar ta shiga bata tsoro

Salaha ya fara ganni rigar dake jikinta ta yage sosai, ama ba ta kirjinta dake fili take ba, sai kakari take ta cuje rufar da ta yiwa kanta, gashin kan a tsaitsaye sai kwalalo ido take tana cenza waje, sket din jikinta kuwa harda jika kamar wace ta zabga fitsarin kwonce

"Ina Hajiar?" Ya fada murya a kausashe yana kallon Mama, wace ke haki sai yade yaden magana take yi kan ta ga ubanda zai fitar da RAUDA domin bayan ta sumar da Raudar kama kaffafuwanta ta yi ta ja ta da kyar ta kaita falo, sannan ta hankada keyar Abdul ya je ya rukunkumeta yana ihun kuka , a nan ne Salaha ta mike kamar zata mutu ta sace wayarta dake yashe a nan ta boye a jikinta sannan ta ci gaba da murzar jikinta dan walahi ta shaku iya shakuwa

"Wace Hajia?" Mama ta fada tana kame kame dan daga yannayin tsayuwarsa ta san yana iya yi mata aikin gajanci la'ada waje

Tsaki ya ja gannin matar fa kamar wata cika ce Walahi, sai kawai ya shigo da kyau ya nemi zagayeta dan shiga dakin lokaci daya yana neman layin YUSUF

Har zai shiga ya dan juyo gannin ta dauko ludayin nata ya dan zuba mata ido sannan ya kalli Salaha da Salima da suka yi zuru zuru sunna kallonsa

Alamu ya masu na su dan dakata , daga tsayen da yake ya risinar da kansa, ya jimke hannunsa da girmamawa sosai ya furta" Barka da warhaka Uban mai uba, marar ubanma kaine ubansa, Barka da warhaka ja gaba ikon Allah, Barka da warhaka dashen Allah, rubutace kake babu wanda zai goge, Allah ne ya nadaka uban gidana ba wani dan Adam ba, dama ina kira ne dan ya kama dole na yi kiran"

YUSUF ya girgiza kansa, ya fara gane abubuwan nan da da wahala a bashi lafiya da su, wato kirari kirarin nan sai kawai ya share shi , a hankali ya furta" Lafiya?"

"Dama su Hajia da na kawo ne aka samu matsala, dan inaga a summe take sosai, matar da muka zo gidanta ne ta shinfida mata koshiyar girki!" Ya fada da irin Muryar nan ta daba, yana sake gyara yannayinsa tamkar a gaban YUSUF din yake

YUSUF ya yi shiru yana tunanin ikon Allahn nan, kai jama'a summe kuma?, ga Mah a cikin zuciyarsa wace tashi daya ya yi tunanin idan har ta ji ai itama tana iya sumewar

A kame ya furta" ka dawo da ita yanzu yanzu, a shigar da ita ciki kafin su Mah su dawo likita zata yi jiran ku"

Daga haka YUSUF ya katse kiran nan ya shiga kiran layin likitarsu ta familly

A dayan bangaren kuwa ana katsewa ya mayar da wayar aljihun rigarsa ya juya da nufin shigar, sai ya ga still Mama na son yi masa ganganci

Juyowa ya sake yi yana murmushin da ya kashe zuciyar Salaha dukda halin da take ciki ta yi mutuwar tsaye tana kallonsa
Yana kallonta ya ce" Hajia yawa ne walahi, idan kika gwada ba zai haifar maki da d'a mai ido ba, dan tsaf zan moda maki shi a Keya numfashi ya dauke a kamani, ki dan bari mana na gama aikin oga dan har ga Allah mu yan a mutunsa ne, oya bani hanya dan dole na dauko Hajia!"
Yana gama fadi ya shige ciki , ya tarda Abdul zuwa yanzu muryarsa ta gama disashewa ta yi kwonce jikin RAUDA yana ta kuka mai fitar da hawaye ama babu amo

Dan zuba masa ido yayi yana mamakin meye ya haษ—a matar nan da mutanen nan masu salihan fuskoki?, yaron nan ya bashi tausayi ainun, hakan ya sa da ya talaba RAUDA Abdul ya riketa tam yana kukan kar a tafi da ita ya fara tiso shi gaba suka fito da ฦ™afarsa ya nemi hangaje Mama da ta so riko Abdul din , da idannuwansa kuwa ya mata alamun yana iya daka mata kafa , hakan ya sa Mama kwasar kururuwa tana fadin yan anguwa su taimaketa kwarton RAUDA ne ya zo ya dauki harda Abdul marayan Allah zai tafi da su duka su kwato mata su, ama yan anguwa suka ki bin shi har Salima ta bude masa bayan mota ya saka RAUDA Abdul ya shige yana sake riko hannunta na dama dake yarfe, shi kuwa ya shige gaba Salima ta shige bayan itama ya tada motar ya figeta ya fice a anguwar

Sosai mama ke ihun kuka, kukan da take yi na yanzu mai shiga zuciyarta ne yana tarwatsa duk wani tunanin gannin mijinta da ta yi a kwana kusa, dan gani take idan har aka tafi da RAUDA da kuma Abdul shikenan babu mai nemo mata Umaru , hakan na nufin ya mutu bata ga gawarsa ba, hakan na nufin zawarci ya kamata da ciyar da kai da biyan haya, hakan na nufin rikon Yar nan cilo ya dawo hannunta gaba da baya, hakan na nufin ko a koma saide saiden abinci a bakin titi ko kuma a koma kauye in dai ana so a rayu? Ina , ba zai taba yiwuwa ba, walahi har garin nan da Rauda take sai ta bi ta dan itace kadai zata iya nemo mata mijinta a garin nan!

Tana komawa ta tarda Salaha zaune ta tafka tagumi da hannayenta bibiyu tana kallon kofar da Maman nata ta fita

Mama ta karaso inda take da tausayinta tana share hawaye ta ce" Salaha, kema kin fara shiga tunanin mahaifin naki yanzu ko? Ko ta jiyatar da ke ne? Tashi ki yi wanka ki je chemis ga yan cenjina nan a baki magani kar aje ta maki mugun rauni kin ji?"

Salaha ta cire tagumin da ta yi ta zubawa mahaifiyarta ido tana tunanin yaya zata yi da matar nan dake son saka mata hawan jini kiri kiri?
Da wata murya ta rashin kunya, wace du dan arziki ba zai yiwa koda yayansa ne magana a haka ba bale mahaifiya, mutun mai daraja a duniyar bawa, Salaha ta budi baki tana kallonta ta ce" Yanzu ke mama a duniyar nan du abinda ya nufo Ni na rufin asiri sai kin saka kafa kin shure? Da idannuwana nake miki alamun ki barshi ya dauketa su tafi, ki barshi mama ama kika ware murya kika tatare zani kike ihu kan wani mijinki da ya tsufa ya gama bugawa? Haba dan Allah to wai Ni ya ake so na yi da raina ne? Daga kin ga na gilma ki isheni in yi wanka, in wanke kafa in wanke pant in wanke baki in wanke kai, bayan fatar nan in aka cika yi mata iya yi tsaf zata tsofe ta bar kai ba komai? Hana dan Allah wankan nan duka duka yau kwana uku rabona da in yi, kuma na fada maki ki bani lafiya in na gama al'adata nake son haษ—awa harda wankin kan na yi ko? Ama kiri kiri mama kike ce min in yi wanka? Yanzu wannan din da kika yiwa haka Ni ai ina ganninsa na ji na kamu da son sa, yanzu in na nemo shi na fada masa yace ba zai iya yi ba saboda uwata me kike so nace maki? Gaskiya a ringa yi ana tuna in fa na rasa miji lalacewa zan yi, dan walahi ba zai yiwu in zo in koma zikau ba, ina.....!"
Ta karashe tana kade kafarta ta nufi ciki ta yi dakin Rauda dan nemo hijabi mai kyan gani ta fita, domin a yanzu yanzu zata batar da wayar nan ta dan samu kudin da zata fara nemo wannan gayen, kwal uba sak irin gayen da take so take burin aura a rayuwa kennan fa, ita fa in yace Mamanta ce bata masa ba sai ta sayi iyayen karya ya samu ya aureta daga baya ta ringa zuwa wajen mama koda a boye ne!

Kumnayen mama suka saurari kalaman yarta ta cikinta, ama zuciyarta ta kasa gaskata mata gaskiyar lamarin
A tsugunnen da take, ta kasa mikewa bale har ta iya tarda Salaha dan su yi magana ta gane ko kanta ta buga ta samu tabuwar hankali ne? Har sai da salahar ta fito ta fice a gidan sannan ta iya dagowa tana jin jirri na kwasarta
Da kyar take kiran sunnan salahar, ama firrr yarinyar nan ta yi kamar bata ji ta ba ta yi ficewarta gashi kiraye kirayen magariba ake yi yanzun , wasu masallatan har sun shige sallah, gashi anguwar ta ki lafiya yanzu a yi wannan a yi wancen, kar dai Salaha ta haukace ta shiga uku?
Wannan tunanin ya saka Mama daukan hijab ta fito tana janyo kofar su ko rufewa da kyau bata yi ba ta shiga bin layi tana haskawa da yar hannu tana neman Salaha, a lokacin da ta fice ne kuma wasu yan samari irin mararsa jin anguwa suka yi wuf suka shige gidan suka shiga yan tatare tataren abubuwan anfani da gagawa suka tattara abinda zasu iya fita da shi suka ficewarsu hankali kwonce!


Tafiyar gagawa ya yi domin cikin abinda bai fi minti arba'in ba suka karasa fada kuma ya samu shigewa har cikin fadar har bangaren su YUSUF da motar domin umarnin da ya sake bashi kennan a lokacin da ya yi kiransa ya shaida masa a summe take fa, har yanzu bata dawo hayacinta ba, kuma ta zubar da jinni sosai daga keyarta shi kam abin ya fara bashi tsoro, shine ya saka shi shigowa direct har cikin gidan da motar sannan ya saka shi bi ta baya ya zo har kofar bangarensu ya ja ya tsaya dan dogarai ba zasu barshi shiga get din ba daga nan, domin yanzun tsaron ya ninka na da sosai, yanzu bayan dogarai harda polisawa ke ba fadar tsaro kuma an fi ba wannan wajen tsaron fiye da ko'ina

Kasancewar a lokacin yana masalaci sai da suka gama sallar Isha sannan ya fito tare da mutanen dake biye da bayansa suka nufo hanyar gidansu, har sai da suka kusa isowa ya salame su yana shaida masu zai shiga da wuri yau

Sai da suka gama kirarinsu yana kallon su suka juya sannan ya shiga takowa a nutse idannuwansa a kan polisan da suke take masa baya wasu daga gabansa, ya girgiza kai a ransa ya furta' Sai kace wa'inda in Allah ya yi wani dan iya shegen zai kashe Ni sun isa su hanna, kawai salon a hanna mutun wali a cikin gida a hanna mutun motsin kirki!'

Yana karasowa wajen motar direban ya fito ya duka har kasa hannunsa jimke yana masa kirari mai haษ—e da yi masa Barka da karasowa

Cikin gundura da magangannun nasa ya ce"
Azl 27
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*

Bismillahi rahamanin rahim

Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

๐Ÿ’ƒ๐Ÿผ Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching๐Ÿƒ๐Ÿปโ€โ™€๏ธ๐Ÿ•บ๐Ÿ˜ .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login