Showing 141001 words to 144000 words out of 188741 words
me yarona? ban san yaya zan yi ba yanzu, dan daga Ni sai Allahna na daukarwa kaina alkawarin daidaita mu'amalata da AMEERAH, inada damar daga hankalin kowa a gobe gobe a daurawa yarinyar cen aure, sai dai wani abu nace min kar na yi haka, ya dace in bata damar ta itama, dan ta nuna tana son a yi adalci kuma ta nuna ba za'a hanna mana yarinyar ba ko?"
Murmushi ya yi yana duban Hajia, dama shi ya san akoy ranar da irin maganar nan zata fito daga bakinta a kan Mah, lokuta da dama idan suka samu matsala ita da YUSUF a kan Mah yakan ce masa ya koyi kawar da kai a cikin lamarinsu, ya ringa tausasa Mah, in sha Allah duk wani abinda ke rikita masu lissafi zai daidaita, Mah zata ji dadi fiye da tunani dan a yi hakuri a bari Allah ya daidaita abinsa ya fi ace za'a yi garaje
A tausashe ya furta" Ki yi hakuri, ki yi addu'a, ki kuma kamanta tayawa, daga wannan idan har wani ya kuma fito mata ba shi ba ki yi hakuri cen dama ba shine mijinta ba!"
Hajia ta hadiye yawun dake wuyanta tana tunanin zata iya kuwa? jiki ba karfi ta yi masa rakiya, sunna tatauna maganar har wajen get na farko sannan ta juyo tana ta sake shawara da komawa kan shawararta ta farko, bata san in har ita zata iya hakuri tana ji tana ganni a yi haka ba, sai dai Shaheed ya fada mata ko me za'a yi ba za'a tsallake hukuncin ubangiji a kan lamarin ba, ya kuma fada mata adu'ar itace ta fi fiye da tada zaune tsayen...., da wannan ta karasa ta shige bayi saboda kiraye kirayen sallar magariba da aka fara.
Kwonci tashi asarar mai rai
Yau RAUDA ta wayi gari cikin wata sabuwar rayuwar da ta sake sakata a halin tunanin yau da gobe kafin ta dangana ta ajiye gefe saboda mutanen dake zagaye da ita tamkar ana yin wata sabgar ne
Tunda safe Atu ta sauka a gidan, Salima kuwa duk kin da ta yi sai da ta kunsa mata kunshi dan Hausa harda yan yatsunta sannan ta amso dinkunnan da aka yi mata tace a gobe sai ta saka, ko da safiya ta yi da ta yi wanka a dole ta sa ta saka suturar ta yafa mayafi ta zauna tare da bakinta da yan gidan
sun mike a fira, Bah ya yi kira cewar ta zo su yi salama da Uncle dinta, dan a yau yau zai daga zuwa kasar waje dan neman lafiyarsa kamar yadda MALEEK ya sanar masu, kuma kiran da aka yi mata bangaren MALEEK din ne zasu je dan su Bah din sunna cen tare da uncle Umar da likitan da zai yi masa jagora har zuwa ƙasar wajen, kasancewar yau Asabar bai fita ba , sai suka same shi a cen din gaba dayansu
Hijab ta so daukowa, sai Mah ta nuna mata mayafinta bashi da wani laifi, sannan ta nuna ATU da Salima su yi mata rakiya
Har zata fita a dakin Mah, Mah din ta yi kiranta, ta mike ta dauko turare ta karaso ta shiga fesa mata fuskar nan tamau a hade danma kar tace a'a, sai da ta yi mata wanka da shi sannan ta umarce ta kan ta je, ta juya ta fita tana waiwayan Mah din, domin tun jiya da dare ta ga yannayinta wani iri, kuma ta yi ta tambayarta amsar daya ce lafiya kalau , ba komai.
A nutse suke takawa, tana bin gine ginen nan da kallo, dan rabonta da ta karewa wajen kallo tun kaurowarsu da gabanin aurenta, tunda ta shiga takaba kuwa bata tako ta nan baban filin gidan ba, ta dai fita ta cen baya zuwa bangaren Hajia, sai yau da suka fito ta ringa gannin gidan sai karra kyau yake sanadiyar shuke shuken da aka zuba ta ko'ina, flawowi ne da shuke shuken fruits kala kala, du sun fara tasawa gidan ya fara daukan Color na shuka masha ALLAH
tafia suke yi a nutse, a jikinta dinki ne na lesh fari kal mai dan digo digon somon sai dan kyalkyalin da ba za'a rasa ba, an yi mata ɗinkin sket da riga budadiya ama bakin tsayin rigar gwuiwarta dan sam bata sauka kasa ba, hannayen ne a bude sosai sai wuyan da aka yi irin baban wuyan nan da baya yiwa ramamu kyau
ta yi daurin dan kwalin da ya fitar da gashinta sosai ta baya, sai mayafin da ta yafa a saman kanta, mayafin kuwa shara shara ne sosai, hannayenta ba komai dan ko wayarta ta baro a dakinta,, sai takalmin da ta saka plat mai tsadar gaske
Sunna daf da shiga get na farko bayan sun gaisa da sojawan dake kofar baban sojan dake ja gabar masu tsaron wajen ya zuba mata ido da kallon da har sai da su Atu suka ankara da shi,, ama ita ta yi tamkar bata ganshi ba, dan ta riga ta tsarawa kanta soyaya kuma ba dai kwana kusa ba gaskiya, shi yasa ta dauke kai a lokacin da Atu ta ce"
Shi yasa ta dauke kai a lokacin da Atu ta ce" Ama gayen cen ya iya kallon kurula, ji min mutun, ta yiwu kowa idan ya zo sai ya kure shi da kallo haka"
Salima ta sake waigawa da sauri ta dauke kanta dan ita tsoronsa take ji tun ranar da suka zo rakiyar Amnah kiri kiri ya hanna masu busa shiga, kuma yan rakiyarma sai dai da daidaya aka ringa shiga ana fitowa, irin yadda ya tsare gida a ranar harta manyan sai da suka tsorata, yau kuma shine da kallo irin wannan?
"Uhum, wancen? barshi inda kika ganshi, walahi mugun miskili ne, kuma baba ne a harkar soja, kin san shi ke jagorar sojawan gidan nan kaf, Ni tsoro yake bani, Allah ya sa kallon da yake yi din ba na ya koramu bane!"
Jin haka ya sa RAUDA jan birki, itama ta juyo ta dube shi kamar yadda ya dan mike daga tsayuwar da yake gannin ta tsaya kuma har ta dube shi
har ga Allah ya san a aikinsa akoy kiyaye irin abubuwan nan, bale a wajen da yake shi ke hanna yarensa shagalta da komai da gindaya masu sharudan ba su ba bibiyar yan matan gidan koda barori ne bale ya'yan gidan, sai gashi yana ji yana gani kaffafuwansa na sake matso shi har ya samu kansa da tsayawa dan nesa kadan da ita yana sake yi mata kallon da ya wuce ka'ida yana gannin yadda Salima ta sake tabatar masu ta tabata kora su zai yi, ya kasa ce mata ba kora su zai yi ba, karra kallon wannan halita dake gabansa zai yi koda kuwa ya san hakan na iya jaza masa yin nesa da aikin nan mai tarin ni'ima
Murmushi ya yi ya ce" Yan matah....., bakuwa ce ke ko a nan kike?"
RAUDA ta lumshe idannuwanta tana jin tamkar ta yi wani mulmulalen ashar, dan har ga Allah sai ta ga ana neman wulakantata ne a wulakanta takabarta, duka duka yau fa ta gama ko? shine har za'a samu wani dan balaja'un da zai tsayar da ita?
Takaici ya sa ta juya bata tare da tace da shi ci kanka ba ta nufi ciki
Da dan sauri ya dubi Salima da mamakinsa ya gama kasheta yana fadin" Kanwata, dan Allah ke ki saurare ni"
Salima ta yi murmushi tana kallon sa
Shima sai ya rasa me zai ce, ta inda zai fara, abu daya ne ya sani yana kallonta ya ji ta gama yi masa dari bisa dari, dan kuwa ya ga halitta gannin idannuwansa
Ajiyar zuciya ya sauke yana hangen ta kama babbar kofar falon ta bude ta shige a raunane ya furta" Ina son ta!"
Salima ta dan zaro ido, ba dan komai ba sai jin muryarsa ta cenza daga yannayin karfi da umarnin jiya, zuwa laushi a yau
Murmushi ta yi, ita kuma hankali kwonce ta ce" Ka tabata da gaske kake?"
Ya yi murmushin shima yana kallonta ya ce" Ta fi karfina ko?"
Salima ta dan baza hannayenta tana sake kallonsa ta ce" Ya danganta, da wani irin mutun ne kai, idan har kai din namiji ne da ya iya son mace , da kuma da mace, to tabas zan iya baka y'ar uwata, ama kafin nan ka fara neman izini wajen Bah baba idan ya baka an gama "
Tana gama fadi ta juya tana murmushi ta yi ciki, shi kuwa ya rasa fargaban maganar ya tambayi uban gidansa maganar nan zai yi ko kwarin gwuiwar tunkarar uban gidan nasa saboda ta cencenta? abinda ya sani daya ne yarinyar nan ta isa a cikin isasu tunda har ta iya dukan zuciyarsa a gannin farko, ashe y'ar gidan ce? ya rab ka sa abin ya zo min da sauki
A lokacin da Salima ta karaso, ATU na tsaye bata shiga ba, hakan ya sa ta kalli hanyar da ta tabata a irin yadda RAUDA ta yi gaba da zafin rai yaci ace ta shige tuni
Idannuwanta suka sauka a kan RAUDAR a tsaye, hannunta rike da fari kal din labulen falon, idannuwanta kuwa a risine tamkar wace ke kallon wani abu ko ke gudun kallon wani abin
Kasa kasa ta ce" Menene? lafiya?"
ATU ta sauke ajiyar zuciya tana jin tamkar ta gudu, sai dai ta san ba damar guduwa
A cikin falon kuwa, tunda Rauda ta bude dakin nan da yannayin garaje a zuwanta na bakuwar wajen wace bata taɓa ziyarta ba, ko a yau din ta bude din ne dan Salima ta tabatar mata cen din shine baban kofar falon baba na bangaren gaba daya, sai ta ji duk irin sanyin wajen yana neman zame mata zafi sakamakon gannin wata rigar alfarma sakale da jikin alfarma daga barin hagu mai dan tazara an dan bude labulen wajen ana tsaye ana kallon baban filin get din na biyu na dogarai, wanda ke tabatar mata duka kaf abinda ya wakana yanzu an gani, hakan ya sa ta kasa karasawa cikin falon take tsaye da burin jin an maidata baya dan ta riga ta sanyo kanta cikin, sai dai aka yi kamar ba'a san da ita a wajen ba, aka yi kamar ba'a gane ta shigo wajen ba aka ci gaba da kallon abinda bata san ko menene ba, har sai da Salimar ta karaso kasancewar bata dauki lokaci mai tsayi ba ta gaza tsayawar kawai ta kama hannun Atu tana fadin" Mu je mana aminiyar mu"
Suka shigo su dinma, sai dai su sunna shigowa Salima ta nemi zubewa saboda wanda RAUDA ke tsaye tana kallo su dinma sun ganshi
A nutse ya juyo da jajayen idannuwansa ya sauke a kan fuskarta
Tun daga sama har kasa ya sake bin suturar jikinta da kallo da mayafin dake jikinta
Kansa ya dauke ya nufi falon da su Bah ke shan fira shi da abokinsa wato uncle Umar, dan alakarsu a yanzu tana da karfin gaske
A hankali ta ringa fitar da numfashi daga hancinta, kasa kasa ta ringa kallon su SALIMA
Idannuwanta ta lumshe ta masu alamun su je
SOSAI Salima ta so juyawa, ama ta kasa saboda rikowar da Atu ta mata ta nuna mata tare fa zasu je din walahi sai dai kowace wace
sunna karasawa Bah ya tarbe su da fara'a yana masu sannu yana kama sunnan daya bayan daya, haka uncle Umar
Zama suka yi a saman kafet su dukansu, a lokacin ne kuma Amnah ta sake zuwa dauke da wani plate din kayan baki ta sake ajiyewa, Bah na yi mata adu'a ta juya, ama idannuwanta sun sauka a kan wace take hako da burin samun yancin da take bukata dan birkita duniyarta!, hakan ya sa ta kasa komawa sai kawai ta labe a kusa dan jin komai a kan wannan karamar y'ar barikin
Tun da suka zauna din ake yi masu nasihar baki dayansu , kowace an yi mata nasihar dai-dai da abinda ya dace a yi mata har Bah ya zo kan RAUDA
A tausashe, bayan ya tuna maganar da suka yi da Hajia ya sauke ajiyar zuciya kuma ya dan kalli YUSUF din ya ce" Y'ata, ba zan gaji da baki hakurin rashin miji ba, ki yi hakuri kin ji? idan mace ta rasa miji ta yi baban rashi a rayuwarta mai matukar wahala, sai dai idan kika yi hakuri kika yi ta addu'a Allah zai fido maki wani, dan a cikin goma dayama baki dauka ba, kuma na san babu wanda zai ga y'ata ya kita, shi yasa zan karra maki nasihar ki kula da tarbiyar ki da darajar ki ta y'a mace, har Allah ya fitar maki da wani mijin na sake bashi amana, a yi ta hakuri da rayuwa kin ji?"
RAUDA ta sake sada kanta tana sauke ajiyar zuciya, a hankali ta gyada kanta dan ba zata iya budar bakinta a irin wannan adu'ar mai girma ba, ko ba komai iyayenta ne, akoy nauyi sosai tsakaninta da su, shi yasa Salima ce kawai da Atu ke amsawa, su dinma ba wai da wani karfi da iya yi ba, a hankali cike da kunya
Uncle Umar na murmushi shima ya dora tasa nasihar, ya idashe da fadin" Kin ga lokacin tafiyarmu ya yi, ki ci gaba da yiwa iyayenki adu'a na san ko na mutu yau hankalina a kwonce yake a kanku ke da d'an uwanki, dan Allah tunda kin samu kin fita a takabar ki je ki dauko shi wajen mahaifiyarsa,, na fi jin nutsuwa idan yana tare da ke, dukkan wata nasiha ta kirki kina samu RAUDANA, fatana ki ci gaba da dauka har karshen rayuwarki, Allah ya maki albarka"
da amen suka amsa, banda shi dake zaune da tanfatsetsiyar samsung dinsa yana dubawa
A nutse ya daga waya, ya dan yi shiru kafin ya ce" Ok docter gasunnan, A sauka lafiya "
Daga haka ya dubi wajen Bah, wanda ya mike yana fadin" Malan Umar mu je, likita har ya isa aeroport ko?"
Kai ya gyada yana kallon su, sun mike su duka da kuma gagawa suka fice, hakan ya sa mikewar da yan matan suka yi basu kai ga fita ba ya rufe kofar ta hanyar aiki da abin rufewar dake ajiye saman karamin teburin wajen sannan ya sake dagowa yana duban Salima wace ta dawo ta duka dan ta fahimci magana yake son yi
Kasa kasa sosai ya furta" Me yasa kuka fito ta nan bayan ga hanya nan ta baya?"
Salima ta yi saurin kallon RAUDA, wace ke tsaye nesa kadan da su, ta sada kanta ta ce" Yau RAUDA ta fita, shine muka fito ta nan dan ta dan rawata kafarta "
"A part din Mamanta babu abinda babu na rawata kafa, ta rike kaffafuwanta iya cen, i'm i clear?"
Salima ta yi saurin gyada kanta tana tunanin me kennan?, sannan ta nemi izinin tashi daga tsugunnen ?
Sai dai me, bata kai ga tashi ba, wani gigitacen shedani ya turo RAUDA, RAUDA dai tasu mai sasaukan hali da biyayya ce ta karaso saman kafet din nan, kaffafuwanta masu ɗauke da Safa ruwan ash mai kwaliya ta ringa lotsawa a saman kafet din har ta karaso dan daf da kujerar da yake zaune
yannayinta idan ka kalla zaka gane tana dauke da magana irin ta bacin ran nan, ama kuma ta danne
A tausashe tana kallon sa kamar yadda ya zubawa fuskarta ido yana kallo ta dan risina dubanta kadan a hankali sosai ta furta " Da tace na fita, tana nufin na gama takaba....hakan na nufin Dole zan fita ko dan Allah ya bani wanda zai kuma daukewa duk wani wanda na zamo jidali a idannuwansa Ni, Allah ya huci zuciyarka Bah karami...... Ni RAUDA ba akuyar dauri bace!"
Daga haka ta mika hannu a inda abin rufewar yake, tana jin ranta na tafarfasa da tabbacin ko waye shi walahi walahi ba zata taba yarda ya rikita mata lissafi wannan karron ba, wancen sojan kuma zata je ne da kanta yanzu ta amshi numbarsa, idan soyaya ya zo da ita zasu yi sai me, tace sai me?!
Sai dai a lokacin da ta dora hannunta a kai, a lokacin Salima ta baje a kasa tamkar an watsa mata mari, Atu kuwa ta dora hannayenta saman kai ta je ta liku da kofar fitar tamkar kadangaren dake neman ruwa , a lokacin ne bata yi zato ko tsamani ba, bata taɓa kawowa kanta ba, batama gane ta yaya duk girman jikinta da kamewarta ba, ta jita tamkar an daga yar farar leda ba karfi an kuma zaunar da ita saman kujerar da babanta ya tashi, lokaci daya an cire rawanin dake dan sakawa ana dan yin nesa da idannuwan nasa, da kuma yannayin fuskarsa, lokaci daya tak aka tunatar da ita karfi ba dayya, ba,, kuma karfin murya ba daya ba, a lokacin da ya kama fuskarta ya dago da karfin da ya sa ta bude idannuwanta ta zuba cikin nasa, a lokacin ne kuma matarsa ta fito da gudu ta dora dubanta a kan haka, a kuma lokacin ne ya budi bakinsa Rai bace, ido cikin ido yana dubanta a kausashe ya ce"
😭😭😭😭😭, Ni wollah ko, to wai ma to wai kam..
a dai ringa amsar BONANZA 😂😍😍😍
Azl 51
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE
💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....
*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da