Showing 36001 words to 39000 words out of 175193 words

Chapter 13 - KUTSE COMPLETE HAUSA NOVEL

07 Feb 2026

552

yace saiya shigo, dan haka yasa duk bugun da samiran tayi bata bud'e ba, har zata bar wajen taji yadda wayarta tafara ruri, da sauri ta zaro wayar ta sakata silent kuma tayi cikin gidan abinta dan bazata bud'e ba.

*Nasir*

Ranshi babu dad'i yake kallon samira yace

"Wai wayar ma bata d'agaba?

Kai samira ta d'aga tace

"Bata d'aga ba wallahi, Amma bara nak'ara gwadawa, kuma gwada kiran tayi cikin sa'a sai Maryam d'in ta d'aga.

Samira batayi magana ba dan itama batasan Nasir d'in yasamu Maryam d'in cikin sauk'i, hakan yasa batace komai ba dan karma yayi tunanin ta d'aga.

Ita kuwa Maryam tana d'agawa tace

"Kinsan Allah samira, muddin mutumin nan yana gidan nan wallahi bazan bud'e gidan nan ba, dan haka sai dai kuyita zama a wajen kedashi, saboda haka kisan yadda zaki zille masa yabar wajen san nan na bud'e miki gidan.

*Samira*

Murmushi tayi a ranta tace "yauwa ta wajena, sai kuma tajuya ta kalli Nasir tace

"Kaga dai bata d'aga wayar ba.

Sai Nasir yad'an zaro ido yace

"Kina nufin duk dad'ewar da wayar nan tayi a kunnen ki ringing takeyi?

D'aga kai samira tayi tace

"Kwari kuwa, yanzu dai zan shiga mak'ota na zauna kafin ta bud'e, dan mijina ya kusa dawowa gida, kuma idan yadawo ya ganni a waje gaskiya ranshi zai b'aci, ya Nasir ka gaida gida.

Ba haka Nasir yaso ba, Amma dan babu yadda zaiyi sai yace

"To dan Allah bani number ta mana.

Kallon mamaki samira tayi masa tace

"Kana nufin baka da number matar taka?

Kai ya Nasir ya jijjiga yace

"Ina da ita mana, tayi blocking d'ina ne a wancen layin nata, idan kinada wani sai ki bani.

Cikin mamaki samira tace "blocking Kum? Gaskiya batada wani layin bayan nata, Amma Insha Allah zan fad'a mata ta bud'eka.

Jinjina kai Nasir yayi yace "tohm shikkenan, Amma kinga bani taki number mana, koda zan kira ban sameta ba saina kiraki.

Babu musu samira tabawa Nasir number kuma yakira ya tabbatar itace san nan ya shige motar yabar wajen ranshi duk babu dad'i.

Sai da samira ta tabbatar dayayi nisa san nan takira Maryam tace

"Bud'e min yatafi.

Dato Maryam ta amsa Amma a ranta tanajin babu dad'in tafiyar da yayi, zuwa tayi ta budewa samira tana yak'e tace.

"Keda Samira kawai sai kibari ya shigo wajena bayan kinsan Abinda ke tskannin na dashi?

Kai samira ta d'aga tace

" Iyi mana, mai zai hana na barshi ya shigo? Kinga muje na samu na bud'e kan nan wallahi har yanzu zafin kitson nan nakeji.

Murmushi Maryam tayi tace

"Ai sai danace kibari nayi miki kikace wai hannuna zafi ne dashi, ai gashi nan kinje inda hannunta yafi nawa zafin.

*Nasir*

Yana tafe yan tunanin Abinda maryam take nufi dashi da zatayi wan nan abin? Shifa komai ya wuce a wajensa, yakamata itama tayi hak'uri ta dawo gidanta ta zauna dan ya d'auki d'amarar yak'i da kowa a kanta domin bata hak'k'in ta a matsayin matarsa.

"A dalci fa? Wata zuciyar ta tambayeshi , gabansa ne yafad'i yana tunanin yin a dalci tsakanin ta Rashida? Zai iya kuwa? D'aga kai yayi kamar wani ke tambayar sa yace

"Tabbas zan kamanta, zan musu adalci da yardar Allah, zan daure na danne son danakewa Rashida na kamanta soyayyar Maryam d'in itama.

Da wan nan tunanin ya k'arasa gida dan sam sai yaji bayajin dad'in zuciyar sa shiyasa kawai yayi gida dan ya samu ya huta.

Tun daga harabar gidan yafara Jiyo wani sassan k'amshi, sosai k'amshin ya bigi hancinsa har sai daya lumshe idanu, bayajin dad'in zuciyar sa Amma sai ya tsinci kansa dayin murmushi da kumajin sanyin zuciyar a lokaci d'aya.

Sauri sauri yayi parking motar tasa ya nufi cikin gidan, yana shiga cikin falon wani k'amshin abinci ya daki hancinsa, nan da nan kuwa yaji cikinsa na motsawa Alamar yunwar daya yini da ita tana neman taso masa.

Mazewa kawai Nasir yayi yana satar kallon Rashida wacce taci ado kamar mai Shirin zuwa dinner, wani k'amshi ke tashi a cikin jikinta hakan yasa yakejin kamar yatashi ya rungume ta.

Bai k'ara shan mamakin Abinda Rashida takeba sai dayaga tataso tare dajan hannunsa alamar yataso, yana tsananin son Rashida shiyasa da wuya ya iya dogon fushi da ita, tana jan hannun nasa kuwa ya mik'e yafara binta abaya kamar wani k'aramin yaro.

Har band'akin d'akinta ta kaishi san nan ta taimaka masa wajen cire masa kayan, shi kansa wankan bata bari yayi da kansa ba sai data taimaka masa tare da cud'e masa jikinsa tas.

Nan ma bata barshi ba sai data taimaka masa wajen saka kaya itama ta canza nata domin duk sun jik'e san nan ta fito dashi wajen cin abinci.

Shidai Nasir kallon Rashida kawai yakeyi yana mamakin Abinda ya canzata har tadawo yimasa Abinda take masa ada, rabon da Rashida ta kula dashi irin haka tun kafin ya K'aro aure, ba k'aramin sanyi ya dungaji a ransa ba yana tunanin da Rashida zatayi hak'uri ta kwantar dakai ta karb'i Maryam a matsayin Abokiyar zama da zaman nasu yafi haka dad'i.

*Rashida*

Daurewa kawai takeyi take basa kulawar da daman ba sabon abune bane a wajenta, wan nan salon kulawar bawai yaune tafara masa ba daman can haka takeyi, Amma tana ganin tunda bai godewa Allah da irin Abinda take masaba har sai da idanunsa yagano waccen bak'ar yarinyar ya auro basai ta kyaleshi ba yajecen tacigaba dayi masa.

Har ga Allah tayi rantsuwar ta daina kulawa dashi, to zuwan da yaya karimatu tayine wajen ta tabata wan nan shawarar shiyasa tace bara ta gwada kozata iya daurewa tayi d'in, kuma gashi ta iya d'in.

Amma sab'anin nada d'in, nada tanayin sane cikin farin ciki da walwal, Amma na yanzu tayi sane cikin kunci da bak'in ciki, dan tana kulawa dashi d'in tana jin kamar ta nad'a masa mugun dukan da sai ya jikkata.

Amma babu komai indai hakan data dawoyi zai sa Nasir yamaida Maryam gidansu suci gaba da zamansu kamar yadda zaukeyi da zatayi, hakan yasa tacigaba da bashi abincin a baki yanaci.

Shi kuma nasir dayake gaulane sai kawai ya dunga washe baki yanayi mata fara'a kamar komai bai had'a suba.

*Nasir*

Kallon Rashidan yayi cikin jin dad'in abinda tayi masa yace

"Banga yaran ba suna ina?

Cikin jan aji Rashida tad'an kwab'e baki tace

"Sunyi barci.

Da wuri haka? Nasir yafad'a yana mik'ewa.

Itama Rashidan mik'ewa tayi tabi bayansa ganin yana Shirin shiga d'akin sa

Da sauri tayi kwana zata shige d'akin ta Nasir yayi saurin janyota, yana janyota ta juya tare da rungume shi ta saka kuka, shafa bayanta Nasir ya hauyi yana furta mata kalmar rarrashi, bai bar wajen da itaba har sai daya tabbatar ta samu sassauci, d'akin nata ya shige da ita tare da bata cikakkiyar kulawa, a wan nan daren ba Rashida ba har taya Nasir yasan yayi missing d'in Rashida ba kad'an ba.

A wan nan kwana biyun sosai Rashida ta d'aukewa Nasir damuwar sa, farin ciki take bashi duk dadai Abinda takeyi ba har zuciyar taba, daman tarko takeso ta d'ana masa kuma ya fad'a, dan taga alamun ma kamar ya manta da Maryam.

Amma a zuciyar Nasir ba haka bane, domin Maryam tana nan daram a cikin ransa, kullum sai ya kirata a waya Amma baya samunta, haka idan yakira samira wataran samiran ta d'aga wataran tabashi uzurin aiki take bataga kiran ba, kuma Abin dayake bashi takaici kullum ya kira sai samiran tace Maryam d'in tana band'aki ko tana salla ko kuma dai wani uzurin, sai yaji gaba d'aya mashi ya gaji da kiran, dan haka ya k'uduri niyar gobe zaije gidan ya sameta idan yaso suyi duk yadda zasuyi dan kafarta k'afarsa sai ya tawo da ita.

*Maryam*

"Ita kanta k'ok'ari takeyi take zaune gidan samira, badan samiran ta rageta da komai ba, hasalima samiran tana matuk'ar k'ok'ari akanta da kuma bata kulawa da sakata farin ciki, shikansa mijinta yana kyautata mata sosai kamar k'anwar sa, kullum sai ya tambeyeta ko akwai Abinda take buk'ata, Amma itama kullum magana d'aya take fad'a masa babu saboda ya wadata gidan sa da komai, san nan itama samira ta wadata ta, ita matsalar ta guda d'aya ce.

"Aurenta shine damuwar ta, ita bawai soyayyar Nasir ko zama dashi ne damuwar taba, kawai tanason tasan makomar aurenta ne a wajensa, sotake tasan akwai igiyar auren ko babu.

Duk Abinda samiran takeyiwa Nasir akanta ta sani, duk kiran wayar da Nasir zaiyi agaban Maryam d'in ne, kuma tanajin yadda Samira ke wana Nasir d'in a kanta, itafa ranta har ya fara b'aci kawai kawaici takeyiwa samiran, Amma gaskiyar lamari zata bud'e shi daga blocking d'in data masa koya kirata su fuskaci rayuwa

*****

Yauma kamar kullum suna zaune a falo suna hira sai ga kiran Nasir d'in, da sauri samira ta d'auko wayar tana dariya tace "kinga mijinki ke kira, wan nan miji naki a kwai naci, yanzun ma wallahi idan na d'aga ca zan masa barci kikeyi, domin kuwa har yanzu lokacin dazaki sauko akan Abinda yayi miki baiyi ba.

Binta da kallo kawai Maryam tana cewa "hnmmm.

Ai kuwa samira na d'aga wa tace "ina wuni ya Nasir?

Bai amsa ba sai cewa dayai ina Maryam?

D'an kallon Maryam tayi tace " sai dai Maryam d'in tana salla ne.

Da b'acin rai a muryar Nasir yace "kinga dakata Samira, karfa kiga ina biye miki kiyi tunanin d'aukar shashancin ku nakeyi.

Meyasa bazaki had'ani da itaba? Kullum yawo da hankali kikeyi min kamar Maryam ba matata bace ba, dan haka malama ki bata waya.

Kasa magana samira tayi, maimakon ta mik'awa Maryam wayar sai kawai ta kashe ta nemi waje ta zauna.

Ganin ran samira yab'aci yasa Maryam tace

"Meya faru ne Samira?

Ajiyar zuciya samira tayi tace "wan nan mijin naki mana.

Wai ni yake zazzagawa masifa saboda na hanaki karb'ar wayarsa.

Girgiza kai Maryam tayi cikin kawaici tace

"Uhnmm, ai kunfi kusa.

*Misalin k'arfe takwas na dare.*

Suna zaune suna cin abinci kawai sai jin nocking gida sukayi, tashi mijin samira yayi yana cewa.

"Towa muka samu kuma? Bai jira amsar da samira zata bashi ba sai kawai ya fice ya bud'e gidan, yasan Nasir dan shima d'an k'asan garin sune, cikin fara'a da mutunta juna suka gaisa, sai da suka gama gaisuwa san nan Nasir yace

"Ni mijin Maryam ne, nazo d'aukar ta mutafi ne.

Murmushi mijin samira yayi yace

"Masha Allah, to bara na sanar dasu, juyawa mijin samira yayi yace Nasir ne mijin Maryam, kuma yace yazo tafiya da ita ne.

Tashi tsaye samira tayi tace "lallai ma mutumin nan, gaskiya babu inda Maryam zataje ai da baisan mutuncin taba, saboda haka ka rabu dashi kawai har zuwa lokacin dazai san darajar ta sai yazo ya d'auketa.

Girgiza kai mijin samira yayi yace "baza'ayi haka ba samira, ki bari aji ta bakinsa tukunna sai musan Abinda yakamata muyi ko?

Bada san ran Samira ba suka yafa mayafai mijinta yaje ya shigo dashi.

*Maryam*

Gabanta ne yafad'i a dai-dai lokacin da Nasir ya bugo sallama, jitayi kamar ta zura da gudu dan ita wallahi kunyar ganin sa ma take, dan ji takeyi a ranta kamar idan ya kalli fuskarta zai gane tanason ganinshi ne, Amma duk da haka sai tayi saurin juyawa tafara tafiya zata wuce d'aki.

Da sauri Nasir ya dakatar da ita ta hanyar cewar

" Dan Allah Maryam kiyi hak'uri, karki tafi dan Allah ki tsaya muyi maganar da zamu fahimci juna.

Dakatawa da tafiyar Maryam tayi, Amma sai takasa juyowa ta kalleshi, dan haka sai kawai ta zauna a kujerar datake kusa da ita.

*Nasir*

Zama yayi yana kallon Maryam dacewar.

Dan Allah Maryam kiyi hak'uri da dukkan abubuwan da suka faru, wallahi sharrin shaid'an ne ya tunzurani Amma ina neman yafiyar ki dan Allah kiyi hak'uri ki bini mucigaba da zama, da yardar Allah babu wani Abin dazai kuma faruwa a tsakanin mu.

Kuka kawai Maryam ta fashe dashi tace

"Taya zan koma gidanka Alhalin bansan a inda za'a ajiyeni ba? Taya zan koma gidan bayan bansan matsayar da kukayi da matar kaba? Taya zan koma gidanka Alhalin bana zuciyar ka matarka ce a ciki? Taya zan koma gidan ka bayan matar ka bata amince dani ba?

Gaskiya bazan iya komawa gidan kaba muddin banida amsar tambayoyin danai maka.

*Nasir*

kuma muskutawa yayi yace. "kinada matsayi babba a wajena Maryam, domin kina raina da gaske kuma kema kin san haka, kuma zaki zauna agida nane a matsayin ki na matata wacce kike zab'i a wurina, kibar batun son danake wa Rashida, dan wallahi kema inason ki Maryam, dan haka dan Allah kizo mutafi.

Ajiyar zuciya Maryam tayi tace "bazan bika gidanka ba Nasir, badan komai ba kuwa sai dan inason samun tabbacin yadda matarka ta karb'eni, san nan inason a karo na biyu ka sanar da matarka cewa nima matarka kace , kuma zaka d'auko ni na dawo gidan dazama, dan babu yadda za'ayi ka d'aukeni a karo na biyu ka kaiwa matarka ni Alhalin bata da masaniya.

Kai Nasir ya sosa yace "wallahi babu ruwan Rashida dake Maryam, ai tasan wacecec ke a wajena, san nan kuma gida ai nawa ne, kuma kowa nakawo dole ta karb'a hannu bibbiyu, dan haka kona sanar da ita koban sanar da itaba zan iya d'aukar ki mutafi ai.

Sai a san nan mijin samira yayi gyaran murya yace

"Am... salamau alaikum, nima dai daman Abinda zance shine, bawai ina bin bayan magan ganun Maryam bane bisa son zuciya ta, ina bin bayan magan ganun Maryam ne saboda shine gaskiya, a gaskiyar magana yana dakyau kafara zuwa ka tuntub'i matarka akan dawowar maryam Nasir, dan itama tana da hak'k'i, kaga kenan ita tafi kowa cancanta da tasan da zuwan maryam tunda tare ne zasu zauna, kuma kaima zakafi farin ciki idan akace ka had'a matanka kuma suna zaune lafiya, dan haka maganar Maryam tanakan hanya.

*Samira*

Itama murmushi tayi tace "mufa ya Nasir kawai mu nason Rashida ta amshemu a matsayin abokanan zamane, insha Allah bazaka samu wani tsaiko ta wajen muba, wan nan shine kawai buk'atar mu.

Ajiyar zuciya Nasir yayi san nan ya mik'e yana kallon Maryam yace

"Shikkenan Maryam babu damuwa, Insha Allah zanyi Abinda kikace kuma Insha Allah Rashida zata baku mamaki, dan da yardar Allah da kanta zatazo tafiya dake.

Ba samira ba, hattaya Maryam da mijinta sai da suka saka dariya saboda Abin al-ajabin da Nasir yayi yanzu, ko kunya baiji ba yake cewa wai Rashida zatazo tatafi da Maryam, sai kace hakan abine kamar fitar tusa, dan haka shine abin yabasu dariya.

Haushi Nasir yaji akan dariyar dasu Maryam sukayi masa, sai yake ganin sun bala'in rainashi, wato suna nufin tsoron Rashida yakeji shiyasa bai isa yafad'a mata tajiba, dan haka sai kawai yaja kwafa tare da ficewa yana cewa

"Zaku gani, dan kuwa zan baku mamaki.



*KUTSE*

? ? *PAGE 17*

? ? ? ? ? *NA*

*MOM HANEEF*

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*Nasir*

Yau kimanin kwana biyu kenan rabon shi da gidan samira, zuciyar sa gaba Waya bata mishi daWi musamman idan ya tuno da yadda Maryam take masa magana cikin sanyi da tausasawa, yanason duka emotions Winta, shi sai yake ganin kamar ma ta rame, duk da a cikin hijabi ya ganta tabbas ta rame ba kamar yadda take daba.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da buga wani ta gumin a lokcin da Rashida tazo ta gifta ta gabansa ta wuce kichen, a ransa yake rayawa tabbas yasan ha??in Maryam bazai barshi ba, ha??inta na aure da kuma ha??in ban zatar da ita da yayi.

Kuma muskutawa yayi a karo na babu a dadi yana kallon Rashida wacce taci uban ado kamar zataje biki tanata shiga kichen da kuma fita tana jera musu kayan abinci a dining.

Tunanin yadda zaiyi wa Rashida magana yakeyi akan Maryam, kwana biyun nan suna cikin daWi kuma bayaso sam yayiwa Rashida maganar Maryam dan yasan ko siWe mata Wuwawu yakeyi saboda yadda yake riritata muddin yana mata maganar Maryam komai zai watse a tsakanin su, shiyasa tun ranar daya dawo daga gidan samira yaja bakinsa ya tsuke, amma yanajin a ranaa gaskiya dole ne yayiwa Rashida maganar Maryam koda zasu SaSe Win, yagaji da Waukar ha??in yarinyar nan da mahaifin ta yabashi a manarta kuma ya kasa saukewa.

Wata ajiyar zuciyar ya kuma saki lokacin da Rashida ta dafashi tana faWin lafiya yake? Menene matsalar?

Kallonta kawai yayi a ranshi yana cewa "kece matsalata Rashida, kuma kece damuwata, nikam ya zanyi dake ne?

Murmushi Rashida ta saka saboda ganin yadda Nasir ya kafeta da ido ko ?iftawa ba yayi, tasan sarai kwalliyar datai masa itace yake kallo har ya kasa Wauke idonsa daga kanta, a tunaninta kenan, da yake son zuciya da kuma son kai ya rufewa Rashida idanu sam data kalli Nasir batagama idanunsa sun cika da kwalla ba har sai dataga ta zubo.

Da sauri Rashida ta shiga goge masa tana cewa "wai meya faru?

Shima Nasir da sauri ya dawo nutsuwar sa ya sakar mata ya?e tare da cewa "kece.

Murmushi Rashida ta sakar masa tace "nasani ai, nice na damu zuciyar ka ko?

?aga kai Nasir yayi yace "sonki ne yayi min yawa Rashida, har inajin idan babu ke rayuwa ta dur ?ushasshiya ce.

Rungume kansa tayi ajikinta tana cewa "nasani Nasir, shiyasa nima a koda yaushe sonka da matsanancin kishinka yake rufe min idanuna.

?an Waga kansa tayi daga jikinta ta kalleshi, shima kallon nata yakeyi sai kawai ta kashe masa ido tace

"Ina sonka Nasir, kuma ina tsananin ?aunar ka, ina kishinka fiye da yadda kake tsammani, dan Allah karka ?ara kutso mana da wani abinda zai iya zama barazana a cikin rayuwarmu.

Zuciyar Nasir ce ta doka da ?arfi yanaji har lugude ne ketashi, da sauri ya rabu da jikinta ya tashi yana ya?e yace

"Yunwa nakeji my love, zo muje muci abinci, kin zubawa su Halima nasu?

Itama Rashida mi?ewa tayi batare da tayi magana ba tabi bayansa jikinta duk a mace.

*****

*Hajja*

Cikin Sacin rai take kallon autarta, sai faman kaWa kai takeyi da jijjiga ?afafu alamar duk furucin da autar tata takeyi bala'in ?ona mata rai yake.

Sai da auta tayi shiru da bayanin nata san nan hajja ta gyara zama tace.

"Kin tabbatar da Abinda kike gayamin? Kinsan banayin hukunci batare da bincike ba saboda gudun take ha??i, kuma kinsan muddin nayi bincike nagano Abinda kike faWa min ba gaskiya bane wallahi yayanku zan saka ya hukunta min ke.

Ido fal hawaye autar hajja tace. "Wallahi hajja da gaske nake a kunnena akayi, kawai dai nayi barcin ?arya ne saboda kar yaya tace idan na faWa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login