Showing 30001 words to 33000 words out of 236327 words
naki?."
"Yana waje."
"Kira shi yazo ya kai masa dawuri, kinga dai zanyi latti koh?."
Da sauri ta fice taje ta kira Jafar da har ya fice waje ta dawo.
Abincin Umma ta miƙa masa tace ya kaiwa abokin sa ya dawo da wuri su wuce.
Amsa yayi cike da farin ciki yace "DEENAH zo muje."
"A'a ba zata ba, kai kaje" cewar Ummar tasu hakan yasa farin cikin dake ɗauke kan fuskar DEENAH gushewa.
Ficewa yayi nan Ummar tasu ta kalli DEENAH da kanta ke ƙasa alamun tayi fushi kafin kuma tace "Kinason ganin sa kullum?."
Da sauri ta ɗago tana kallon Mahaifiyar tata jin abinda ta faɗa.
"Kinason ganin sa kullum?" ta sake tambayar ta.
Da sauri ta jinjina mata kai alamun eh, nan ta sake cewa "Daɗi kikeji a ranki idan kin ganshi?."
Shiru tayi tana kallon fuskar mahaifiyar tata kafin kuma tace "Umma idan yaƙi cin abincin da na kai masa ne nakejin babu daɗi."
"Maiyasa baya cin abincin da kike kai masa?."
"Nima ban sani ba, amma idan naje har korata yakeyi yace na daina zuwa kusada shi, kullum baya cin abincin da nake kai masa sai dai na baiwa almajirai a hanƴa."
"Bashida kowa, bashida wurin kwana kuma bayacin abincin da kika kai masa, strange" ta faɗa cikin ɗan nazarin abin kafin kuma ta numfasa tace "Okay muje."
Fitowa sukayi bakin ƙofar gidan suna jiran dawowar Jafar.
Suna tsaye suna jiran dawowar Jafar kawu ya fito daga cikin gidan, kallo ya ƙare musu sama da ƙasa kafin yace "Toh za'a fita harkar karuwancin da aka saba kenan?."
Ɗauke kai Umma tayi bata kulasa ba sai ma danne-dannen wayar da takeyi fuskar nan nata a murtuƙe.
Nan ya sake cewa "Ke, ki koma ba zaki makarantar ba, Rabi'atu bata jin daɗin jikin ta dan haka ki tsaya ki taya ta da ayyukan ta tukun."
"A wane dalilin?" cewar Umma dake kallon sa cikin mamaki tunda ya fara magana.
"A dalilin matata batada lafiya sannan kuma a matsayi na Na wan Mahaifin ta."
"Toh gaskiya kayi haƙuri, yanzu makaranta zata kuma ta riga da ta shirya, idan yaso idan ta dawo sai tayi mata aikin, amma yanzu kam gaskiya makaranta zata."
"Ni nace ba zata makarantar ba, Koh so kike dama ita Rabi'atu ɗin ta mutu koh, ke baki taimaka mata ba, ke kuma baki bar ƴar ki ta taimaka mata ba, kinayin haka ne duk dan kinsan batada ƴan uwa anan babu mai zuwa mata kullum taya ta aiki shiyasa kike haka, yanzu idan nayi magana nace ke kike 6ata ƴaƴanki da kanki sai ki hau ni da rashin kunƴa kina cewa ƴaƴan ki masu tarbiyya ne, ina tarbiyyar take bayan kina yi musu da hani da taimakon mutane."
Ummar su DEENAH sam batason surutu da hayaniya irin na Kawu gashi kuma akan hanƴa suke kowa na wucewa yana kallon su, ga kuma kawun baya magana a hankali, bai ƙi ya tara mata mutane ba yanzu sannan ya aibanta ta a gaban su tare da yi mata sharri, wannan ba damuwar sa bace, dan kuwa bashida mutunci koh kaɗan, hakan yasa Umma buɗe jakar ta ta ciro makullin part ɗin nasu ta bawa DEENAH tace "Yi haƙuri MADEENAT ƴar albarka, ki haƙura da makarantar yau ɗin ki taya antyn ki aiki,kinga batada lafiya koh?."
DEENAH da idanun ta suka tara hawaye ne tasa hannu ta kar6i makullin tace "Toh Umma bakomai zanyi mata aikin ai na kwana ɗaya ne kawai."
"Yauwa yarinƴa ta Allah yayi miki albarka" ta faɗa tana shafa kanta.
Tsaki kawu yaja sannan yace "Ni za'a nunawa tijaranci da munafurci?, ke kanki kinsan a matsayin ƴaƴa na suke sannan kuma ina da kowane irin iko akan su ke baki isa ki hana ni yin abinda nayi niyya game dasu ba, shima wannan jan ƙosan kwanan nan zan fara maganin ka kaima" ya faɗa yana nuna Jafar dake ƙarasowa wurin nasu yana aikawa da kawu da mugun kallo.
"Jeki kinji" ta faɗa tana share maganar Kawu ɗin.
"Umma ina kuma zata je?, sati uku fah bata je makaranta ba duk dan sabida Kawu da ya ɗauke ta ya kaita ƙauye ta sha wahala ta dawo dakyar kika samo kuɗin amso ta, shine kuma yanzu zai ce ba zata je makarantar boko ba, shi yake biya mana kuɗin makarantar ne?" ya faɗa cike da muguwar haushin kawun nasu dake cinsa.
"Kin gani koh, kina dai ganin irin maganganun da yaron nan ke faɗamin a gaban ki amma kin kasa hana sa, sabida kina jin daɗin yadda yake min magana kamar wanda shine na sama dani, toh koh mahaifin ka da yake raye baya yimin magana gatsai haka balle kai ɗan da ya haifa jiya-jiya, jeka makarantar ka dawo zaka dawo ne ka same ni anan gidan, ɗan iskan banza ɗan iskan wofi."
Hannun Jafar kawai Umma taja sukayi gaba ba tare da tabi kan maganar kawu ɗin ba.
Da kallo DEENAH ta bisu tana matsar kwalla, dan kuwa tasan ba ƙaramar baƙar wahala zata sha a hannun su ba yau.
Tsaki yaja sannan ya juyo ga DEENAH tare da daka mata tsawa yace "Zaki shiga ciki ne kokuwa sai nayi kwallo dake, shegen kanta yawa yawa tayan tifa."
Tusa ta gaba yayi har part ɗinsu sannan ya hau ƙwala kiran "Rabiya"
A ƙufule ta fito idanun nan duk a kumbure kwantsa ya cika da alama ma tashin ta kenan daga bacci nan tace "Haba dan Allah Mai-gida, wannan wace iriyar wulaƙanci ce?, ina cikin bacci na kayi ta kwala min kira haka sai kace wanda za'a tashi ƙiyama mtssww" ta faɗa tana tufar da ƴawu.
Haƙora ya washe yace "Allah ya huci zuciyar ki gimbiya ta, jeki kawai kiyi kwanciyar ki ga nan mai aiki na samo miki, ita zata yi miki dukkanin ayyukan cikin gidan nan, ni yanzu bari na fita naje nayo cefanen kayan miyar da za'a yi, ai kince kaza kike so koh?."
Yatsina fuska tayi tace "Eh kaza nakeso, sannan kuma ka haɗomin da gasasshiyar ta da 5Alive, na samu naci sabida ƴunwa nakeji yanzun."
Dariya yayi yace "Kada ki damu bari naje ni yanzun nan na dawo, ke kuma ki tabbatar da kin kammala dukkanin ayyukan ki kafin na dawo cikin gidan nan idan ba haka ba yau sai jikin ki yayi tsami a gidan nan, kinji koh bakiji ba?."
"Naji" ta faɗa kanta a ƙasa.
Maida duban sa yayi ga Rabi'atu yace "Shalele ta bari naje ni yanzun nan na dawo."
"Toh" kawai tace koh ladar samun addu'ar dawowa lafiya bai samu ba haka nan ya fice kamar ya tashi sama dan sauri.
Kallon DEENAH dake tsaye tayi tace "Ke dan gaki isashhiya jiya ban ce miki akwai aikin da zaki ƙarasar min ba, amma dan munafurci shine kika shirya kika kama hanƴa da niyar ficewa zuwa makaranta?."
"Kiyi haƙuri mantawa nayi."
Rankwashi ta zuba mata a tsakiyar kai tace "Mantawa kikayi, ni zakiyi wa ƙarya toh dan Ubanki ki wuce kije ki ƙarasar min da aikin jiya."
Hannun ta dafe da kanta tayi hanƴar part ɗinsu tana matsar kwalla.
"Ina kuma zaki?."
"Canzo kaya na zanyi."
"Zo nan" ta faɗa.
Zuwa DEENAH tayi ta tsaya a gaban ta nan ta miƙa mata hannu tace "Bani makullin."
Makullin DEENAH ta bata nan kuma ta sake cewa "Ina abincin makarantar ki?."
"Yana cikin jaka na."
"Ciro shi" ta faɗa cikin tsuke fuska.
Sauƙe jakar makarantar tayi ta ciro lunch box ɗinta a ciki da ledar bredi ta miƙawa Rabi'atu.
Amsa tayi tare da buɗe kular nan ƙamshi ya bugo mata hanci harda su lumshe idanu, Farfesun Cow- tail ne sai shining yakeyi mata a idanu nan ta haɗiyi ƴawu tace "Cha6 ana bura uba a cikin gidan nan, wato ku nan har farfesu akeyi muku ku kai makaranta lallai daɗi yayi muku yawa, yanzu da ban tambaya ba haka nan zakije ki ajiye shi tsabar baƙar zuciya da mugunta irin taki bayan kinsan banida lafiya ga kuma ƴunwa dake nuƙurƙusar ƴan hanjin ciki na, lallai ƴar gata" ta faɗa tana tsamo nama ɗaya ta jefa a bakin ta tana tauna harda su lumshe idanu.
Suɗe hannu tayi tace "Wuce kije ki fara yi min aikin" ta faɗa tana amsar jakar makarantar ta.
Shigewa DEENAH tayi zuwa falon nan ta gansa kaca-kaca kamar ba jiya ta gyara sa ba, tattare ledojin da ta gani anci abu a ciki tayi ta fito ta sasu a dustbin kafin kuma ta kalli part ɗinsu da yake a buɗe da alamu Rabi'atu na ciki nan taje ta dan ɗauko tsintsiya.
Inda suke ajiye kayan shara ta nufa ta ɗauko, motsin da taji a ɗakin Ummar ta ne yasa ta zuwa ta leƙa, daidai lokacin kuma Rabi'atu ke ƙulle abu a bakin zanin ta.
Jin kamar tsayuwar mutum ne yasa ta juyowa a firgice tana kallon DEENAH dake tsaye tana kallon ta, Wata iriyar azababbiyar ashariya ta dumulmulo tare da sauƙe shi akan DEENAH tace "Dan bahun ubanki mai kikeyi anan, ba cewa nayi kije kiyi min aiki na ba?."
"Kayan shara nazo ɗauka fah."
"Kayan shara kika zo ɗauka shine zaki sanƴa ni gaba kina kallo da wadannan mayun idanun naki, shegiya mai suffar kafiran aljanu, algunguma kuma wallahi kika kuskura kika buɗi baki kika cewa Ummar ki na ɗau mata abu a ɗaki wallahi sai kin gane kurenki a gidan nan kin dai san hali na koh?, zaki ficemin ne koh sai nazo nayi wurgi dake anan shegiya mai kama da farar mayu."
Da sauri DEENAH ta fice ta juya ta bar ɗakin, nan kuma Rabi'atu ta cigaba da binciken ta har dasu sauƙe akwati tana cicciro abubuwan dake ciki, duk wanda taga yayi mata kuwa sai ta ɗauke shi tana faɗin ai itace yakamata ace tana sanƴa irin su.
A haka ta gama ɗaukar wadanda sukayi mata kafin ta fito zuwa part ɗinta.
Anan ta tadda DEENAH har ta gama gyara mata falon ta koma gyara ɗaki.
Ɗakin ta shigo anan ta dire abubuwan da ta ɗebo nan ta shiga gwadawa, kama daga kan su kaya, ɗan kunnaye da sarƙa dasu awarwaro da ma kuma dayawa na ado.
Idanun DEENAH ne suka sauƙa kan wani sarƙa da ɗan kunnen GOLD na Ummar ta nan taje ta ɗauke shi tana faɗin "Anty wannan shine kyauta na ƙarshe da Abban mu yayi wa Ummar mu kafin ya rasu baikamata ki ɗauke shi ba."
Hannu tasa ta fuzge tare da tsinka mata mari tace "Na ɗauke ɗin munafuka, idan Ummar taki ta dawo kice mata ni Rabi'atu ce ta ɗebe mata kaya, wadannan tsadaddun kayan ni yakamata na dinga sanƴa su ba Ummar ku ba, dalla wuce ki bani wuri koh na ham6are ki yanzun nan."
Ficewa tayi daga cikin ɗakin idanun ta na tara hawaye.
Sosai ta gyara mata koh ina sai tada ƙamshi yake, bayan ta gama yi mata gyaran ne kuma ta sake loda mata uban wanke-wanke da wankin kayan ta da basu wuci kala huɗu ba ta wanke.
Sosai DEENAH ta gaji wanda har tana yin aikin tana kuka, sosai jikin ta keyi mata ciwo.
Tana cikin yin wanke-wanken Kawu ya dawo da cefanen da yaje iyowa.
Sai a sannan ne Rabi'atu ta ta6uka abu wurin yin aikin gidan nata, sai dai dukda haka bata bar DEENAH da ɗaukomin wancan ɗaukomin wannan ba.
A haka ta gama girkin ta sai dai koh ta6i bata baiwa DEENAH ba dukda kuwa uban aiki da gajiyar da tayi, ga kuma ƴunwa da takeji.
Part ɗinsu ta koma tayi wanka ta shirya cikin atamfa ɗinkin riga da skirt kafin ta samu wuri ta kwanta.
Cikin bacci taji ana shafa ta, kafin taji an fara ɗaga mata skirt ɗin dake jikin ta.
A razane ta buɗe idanun ta tana sauƙe su cikin na Kawu dake shirin zare igiyar wandon sa.
Ihu tasa nan yayi saurin rufe mata baki yana zare mata jajayen idanun sa yace "Idan kika kuskura kika yi ihu, sai na ɗauke ki na maida ki ƙauye, sannan kuma duk wani aiki na Rabi'atu ke zaki dinga yinsa, kuma makarantar boko da ta islamiyya babu ke babu zuwa har abada."
Sosai jikin DEENAH ya kama rawa kuka kuwa harda majina, nan fah kawu ya fara kiciniyar ware mata ƙafafu inda ita kuma take matse wa.
Wani uban rankwashi ya zuba mata a tsakiyar kai yace "Ba zakiyi shiru ba sai kin tona min asiri?."
"Dan Allah Kawu kayi haƙuri, mai kake son yi min dan Allah kayi haƙuri wallahi banyi maka laifin komai ba, kada ka dake ni."
Sosai Kawu ya haɗa uban gumi fuskar nan tasa yawa an naushi fura, idanun sa wuri-wuri yake lashe baki yace "Ba dukan ki zanyi ba, ƙafafun ki kawai zaki buɗe min, wani abu mai daɗi zanyi miki, sannan kuma kada ki faɗa wa kowa kinji" ya faɗa yana ciro naira ashirin a cikin aljihun sa yace "Sannan kuma idan kika yarda nayi miki ,zan baki wannan kuɗin ki sayi minti, ai kinaso koh?."
"Dan Allah Kawu ka sake ni, ai Umma tana saya mana mintin da yafi na ishirin ma, dan Allah Kawu kayi haƙuri."
"Ke kinga ki barni nayi abinda nazo yi cikin kwanciyar hankali, kinga babu kowa a cikin gidan nan, daga ni sai ke dan kuwa Rabi'atu ma ta fice ungwa, kuma kinga koh sha biyun rana batayi ba balle a taso su yayan ki daga makaranta, babu mai kwatar ki dan koh kinyi ihu ba wanda zai jiyo ki" ya faɗa yana kai hannun sa cikin skirt ɗinsa.
A razane tasa ihu tare da gantsara masa cizo a kunne kafin ta fito a guje.
A razane ya tashi cike da firgice wa ya ɗau hular sa ya bi bayan ta, sai haɗa uban zufa yake.
DEENAH kuwa tuni ta fice a gidan sai falfala gudu take da dagaggen skirt a hanƴa tana ihu da kuka, sai dai kamar haɗin baki babu kowa anan hanƴan kasnacewar ungwa ce da kowa na cikin gidan sa musamman ma da yau ranar aiki dayawa sun fice zuwa wurin aiki da makaranta.
Tuntu6e taci ta faɗa kan wani tsohon langa-langa inda ya yanke ta a ƙafar ta sosai take kuma jini ya 6alle ya fara zuba.
Hango Kawu da tayi a bayan ta ne yasa ta tashi ta ƙara ƙaimin gudun ta.
Tundaga inda yake zaune jugum dashi ya hango ta da gudu tana kuka.
Miƙewa tsaye yayi yana taro ta cike da tashin hankali ganin yadda take ta zuba kuka.
"Hey, mai ya sameki, mai yasa kike kuka, waye ya dake ki?" ya faɗa cikin jero mata tambayar.
Turus Kawu yayi yana kallon su cike da tashin hankali ganin DEENAH na nuna shi da hannu.
"That Monster, mai yayi miki?."
"Shine yace wai na buɗe masa skirt ɗina" ta faɗa cikin kuka sosai.
Jin ta ambaci skirt ne yasa shi maida duban sa kan skirt ɗin, nan yaga jini na biyo mata ƙafa ya 6ata mata skirt ɗin.
Sosai zuciyar sa ta hau bugu, gashi bata bar kuka da maimaita "Shine yace wai na buɗe masa skirt ɗina."
ZEEYAD da bai fahimci mai take cewa bane yasa shi nufar Kawu tare da cakumo wuyar rigar sa yace "Mai kayi mata?."
Cike da hargowa Kawu ya fara ihun "Jama'a a kawo ɗauki zai yiwa yarinƴar mutane faɗe, zumu zumu na kama sa yana shirin ƙetawa ƴata haddi, jama'a a kawo ɗauki" yadda Kawu yake ihu ne kuma yasa mutane suka fara taruwa, da kuma wadanda suke kan hanƴar wucewa duka, kan kace miye kuma wurin ya cika da jama'a gashi har yanzu Kawu bai bar faɗin cewa "ZEEYAD zaiyi wa DEENAH fyaɗe ba."
Wani dattijo ne yace "Haba malam Sale ka dawo nutsuwar ka mana haka nan kayi mana bayanin abin dake faruwa."
"Ya kake nayi, tayaya za'ayi na dawo cikin nutsuwa ta yana shirin lalata rayuwar marainiyar Allah, bamu san shi ba, bamu san daga wace nahiyar ya faɗo ba, yau rana tsaka na kama sa da wannan mummunar laifi."
"Mai kake son faɗa ne haka?."
"Gashi nan, wannan balaraben shi na kama yana shirin yiwa yarinƴa ta fyaɗe yau."
"Inalillahi wa inna ilaihi raji'un" duka ƴan wurin suka faɗa kafin kuma duk su rirriƙe ZEEYAD da baisan mai ke faruwa ba, bai kuma san abinda suke faɗa ba.
"Kai ku tsaya, ku tsaya, bari muji komai daga bakin ita yarinƴar tukun" faɗin dattijon nan kafin su nufi wurin DEENAH dake tsaye har yanzu tana kuka da alama bata cikin hayyacin ta sabida tsorata da tayi, ga kuma cinƴar ta da ta matse guri guda tana cigaba da kuka.
Wannan dattijon ne ya nufi wurin ta yace "Ke yarinƴa kinsan wannan?" ya faɗa yana nuna mata ZEEYAD.
Abinda take nanatawa ta sake faɗa "Shine yace wai na buɗe masa skirt ɗina."
"Inalillahi wa inna ilaihi raji'un" duk ƴan wurin suka hau nanatawa.
"Kun gani koh ai na faɗa muku, wannan dama daga ganin sa ba shida aiki sai lalata yaran mutane, na daɗe da fara zargin sa, toh wallahi ba zan yarda ba, dole ne a kirawo hukuma suyi gaba dashi, dole ne a samarwa ƴata ƴancin ta wallahi, dan kuwa ba zaiyiwu ya lalata mata rayuwa bane ba kuma na kyale shi."
Kan kace miye kuma har an kirawo ƴan sanda, ZEEYAD da sai yanzu ya fahimci abinda ke faruwa ne yace "Babu abinda nayi mata, mai zai sa nayi mata haka, itace tazo wuri na wannan mutumin na biye da ita" ya faɗa yana nuna Kawu.
Ɗaya daga cikin mutanen ne yace "Ƙarya kake yaro, na daɗe da sanin irin ku, yau Allah ya toni asirin ka, kanaso kayi wa yarinƴa fyaɗe sai kuma Allah ya kama ka, dole ne ƴan sanda su zo su tafi da kai wallahi" cewar wannan mutumin cikin muryar turanci, sai a sannan ZEEYAD ya fahimci Kawu sharrin yiwa DEENAH fyaɗe ya ɗaura masa.
"What, fyaɗe?, bani bane i would never do such thing, shine yayi mata fyaɗe, and she came running to me for help, you can asked her again bani bane nayi mata fyaɗe."
"Karya kake ita ma ai yarinƴar an tambaye ta kuma tace kai ne kayi mata fyaɗen, yanzu dai an ƙira Uwar Yarinƴa da ƴan sanda suna kan hanƴar zuwa dole ne kayi bayani wallahi" nan suka sake ƙanƙame sa yayin da wasu kuwa har sun fara kai masa duka.
Kawu kuwa babu abinda yake cewa sai "yauwa ku ƙara masa, shine, shine wallahi sai hukuma sun hukunta ka, macucin banza da wofi" ya faɗa yana yin wurin DEENAH tare da kamo ta, kafin ya sunkuya ta saitin kunnen ta ganin hankalin mutane ya koma ga ZEEYAD ya raɗa mata "Kina jina wallahi kika kuskura kika ce nina nayi miki abinnan sai na kashe Mamar ki da Yayan ki, sannan