Showing 27001 words to 30000 words out of 236327 words
nufin, idan muka faɗa maka yadda komai yake zaka iya zana shi sak?."
"Insha Allah" ya faɗa.
"Zaka zama abokin na?" cewar Jafar ɗin.
Murmushi ZEEYAD yayi jin yadda yayi maganar nan ya girgiza masa kai.
Cike da jindaɗi ya rungume DEENAH yace "Yace zai zama aboki na daga yau."
Murmushi tayi tana kallon sa, ƙarar bugun bell ɗinda sukaji ne ya sanƴa su tashi da sauri nan Jafar yace "Gashi zan bar maka takarda ta ka zana ni ni kaɗai, kaji?" ya faɗa yana ajiyewa ZEEYAD takardar tasa.
DEENAH ma ajiye nata tayi tana murmushi tana kallon sa.
"Mungode sosai, Allah yayiwa rayuwar ka albarka" cewar Jafar kafin yaja hannun DEENAH sukayi gaba.
Juyowa tayi tana kallon sa hakan yasa shi sakar mata murmushi kafin kuma ta juyar da kanta suna cigaba da tafiya.
Takardar DEENAH ya ɗauka ya shiga ƙarewa zanen hoton ta da yayi a jiki kallo kaifin yayi murmushi ya juya zuwa ga next page ya shiga yin wani zanen kuma.
Bayan an tashe su da yamma suka biyo ta wurin ZEEYAD fuskar su ɗauke da murmushi suka zauna a gaban sa, nan Jafar yace "Alhamdulillah, Mun tashi ka gama yi mana zanen?."
Takardar ya ɗauko ya basa kafin ya shiga buɗe nasa cikin farin ciki "Wooww" ya faɗa yana buga tsalle kafin ya shiga nunawa DEENAH, "Kinga ni ya zana da irin hular larabawa akaina, kiga yadda nayi kyau."
Murmushi DEENAH tayi tace "Ina nawa fah?."
Nata takardar suka buɗe Jafar, da har farin cikin da yake ciki yayi masa yawa yace "Ki ganki, kyakkyawa dake kiga har flower ya zana miki akanki kamar head-band kina murmushi."
Dariya tayi tana kallon cikin takardar tace "Muje gida mu nunawa Umma."
Kallon ZEEYAD Jafar yayi yace "Ya Sunan ka?."
Idanu DEENAH ta zuba masa jin koh mai zai ce, sai dai kafin ya buɗi baki yayi magana suka jiyo murya ta bayan su.
"Kan bantar Uba, mai kukeyi anan bayan kowa ya watse ya tafi gida?, ƴaƴan marar mutunci tsinannu" ya ƙarashe yana ɗaukar ƙatuwar bulala ya nufo su.
ZEEYAD ya gane shi, shine mutumin da yasa masa ido ƴan kwanaki biyun nan.
Hannun DEENAH Jafar ya ruƙo suna shirin rugawa ne a tsawace yace "Idan kuka kuskura kuka motsa koh da ƴar yatsar ku ne toh wallahi sai na lahira ya fiku jindaɗi a garin nan yau."
Duk tsayawa sukayi suna kallon sa had ya ƙaraso gaban su, nan ya shiga nuna su da bulalar yana faɗin "Ku gaku ƴaƴan tsinanniya kuma gantalalliya koh?, ita uwarku ta fice yawon karuwancin da ta saba ku kuma kuna nan wurin baƙon da baku san daga inda ya fito ba yana kwakule ku ya baku wani abin koh?."
"Mu ai Ummar mu ba yawon karuwanci take zuwa ba, aiki take zuwa ta samar mana abinda zamu ci kuma ta kula damu..." bai ƙarasar ba yaji wani irin bugu a bakin sa nan kawun nasu yace "Idan ba yawon karuwanci take zuwa ba, ina take samun kuɗin da har take iya ɗaukar ɗawainiyar ku duka, kuma wurin aikin nata ba duk maza ne suka cika ba, Allah ne kaɗai yasan 6arnar dake faruwa achan, kai kuma nan har ƙanwar ka shegiya mai idanun mujiyar nan kake kawo wa wani ƙato yana tatta6a ta koh?" ya faɗa yana shirin fizgo DEENAH da ta 6uya bayan Jafar.
"Ka sake ta, ka sake ta idan zaka dake ta ni ka dake ni a maimakon ta" cewar Jafar yana riƙo ta tare da miƙawa kawun nasu hannun shi.
"Kai ni zaka yiwa rashin kunƴa koh?, toh bari ka gani" ya faɗa yana ɗaukar bulalar da niyyar zuga mata ne yaji an riƙe bulalar taƙi yin gaba taƙi yin baya.
Maido duban sa kan ZEEYAD dake tsaye hannun sa riƙe da bulalar yayi yace "Eh tabbas babu shakka, kaga zan dake ta nayi mata lahani ina zaka samu damar shafa jiki mai laushi, ai dole ka riƙemin bulala."
"What is he saying and who is he?" ya faɗa yana kallon Jafar.
"Kawun mu ne, yayan Baban mu ne shi."
"Yeah, naga alama" ya faɗa yana maida duban sa ga kawu dake sake da baki yana kallon su.
"Leave the Kid's alone, and don't you dare try to raise your hands on them again"ya faɗa yana fuzge bulalar hannun kawun.
"Bakomai, bakomai zamu gamu ne a gida, ai idan kun samu mai tare muku anan waje, ita uwarku ta gida bata isa ta hana ni dukan ku ba, shaiɗanun banza da wofi" ya faɗa cikin borin kunƴa yana yin gaba.
Duk da kallo suka bisa kafin Jafar yayi murmushi yana kallon ZEEYAD yace "You scared him away."
"Did i?" ya faɗa cikin ɗan waro idanu.
"Yeah, idanun ka suna cike da kwarjini ne, inaga shiyasa ya tsorata ya gudu" ya faɗa yana ɗan dariya.
Murmushi ZEEYAD yayi sannan yace "Yakamata ku tafi gida haka nan, sai gobe kuma."
Kai ya jinjina masa kafin yace "Toh sai gobe, DEENAH zo mu tafi" ya faɗa yana sanƴa hannun sa kan kafaɗun ta suka wuce.
Da Kallo ya bisu, wondering wane irin rayuwa sukeyi a cikin gidan su tare da wannan shaiɗanin mutumin...........
**************************
.........."Ke zo nan" ta faɗa dai-dai lokacin da su DEENAH suka shigo cikin gidan.
Cikin sanƴin jiki ta ƙarasa wurin ta, nan tace "shiga ciki ki gyara min ɗaki da falo banajin daɗin jiki na."
Kallon ta kawai DEENAH ta tsaya yi, hakan yasa ta daka mata uban tsawa tace "Dan Uwarki ba dake nake magana bane, kin wani sanƴa ni a gaba kina kallo haba ku kaɗai yara a cikin gidan nan amma sai kubi kuyi ta sawa mutum ciwon kai kuna sashi ihun da baiyi niyya ba, zaki wuce ne koh sai na ham6are ki?" ta faɗa cike da masifa da hargowa tana aikawa da DEENAH muguwar kallo.
Jafar ne yace "Yanzu fah dawowar mu daga islamiyya koh hutawa bamuyi munci abinci ba, kuma kice zaki sata aiki?."
"Toh ɗan masu iya yi, ai dah kawai duka ka kawomin nasan dagaske kake jin haushin abinda nakeyi wa ƙanwar taka, marar kunƴar banza da wofi kawai, tsabar baƙin halin ka da rashin kunƴa baka isa a sanƴa ka aiki a gidan nan kayi ba, kuma dan tsabar rashin mutunci yaushe rabon ku da ku ganni a cikin gidan nan amma koh sannu da zuwa baku iya yimin ba koh?, yayi kyau ba laifin ku bane."
A fusace ya juya ya buɗe 6angaren su ya shige.
Maida duban ta tayi kan DEENAH tace "Wai ba zaki wuce bane banza."
"Toh ai Anty kin tare ƙofar shigan" ta faɗa cikin sanƴi kamar zatayi kuka.
Tsaki taja tace "Wuce, kuma wallahi kika buge ni na haɗa kanki da bango" ta faɗa tana ɗan matsawa kaɗan.
Ƙafa DEENAH tasa tare da ƙoƙarin wucewa a rashin sa'a ta taka mata Hijabi.
Fizgo ta tayi waje tare da shimfiɗa mata mari a fuska ta zungure ta har kamar zata faɗi tace "Duk girman idanun nan naki baki gani ba sai da kika taka min Hijabi da wannan takalmin naki da kika ɗebo uban najasa da datti a waje?, toh jeki gama gyara ɗakin ki fito ki wanke min shi dan dashi zanyi sallah akanki kuma ba zan ciro wani sabon Hijabin ba, kuma ki cire takalmin nan yanzu anan wurin, ba zaki shigar min dashi ciki ba."
Da sauri ta cire takalmin nata tana shigewa haɗi da matsar kwalla.
Koh da ta shiga kaca-kaca falon yake, ga kuma wani uban datti kamar bola kwanukan da akaci abinci dasu wanda da alama sun daɗe a wurin sakamakon abincin da duk ya bubbushe a jiki duk ta tattara su wuri ɗaya ta fito dasu baranda ta ajiye.
Tsintsiya ta shiga nema bata gani ba, hakan yasa ta faɗin "Anty ina tsintsiyar sharan?."
"Banidashi, jeki ɗauko na uwarki,kiyi amfani dashi" ta faɗa cikin yatsina fuska.
Wucewa tazo tayi taje part ɗinsu ta ɗauko tsintsiyar shara da mopper da abubuwan gyaran ɗaki duka ta fito.
Da kallo ta bita nan tace "Duk wadannan abubuwan na Ummar ku ce koh arowa tayi?."
"Na Ummar mu ce" ta bata amsa.
Baki ta ta6e tace "Wuce."
Wucewa tayi ta shiga kafin kuma ta hau gyaran cikin falon, kafin ta gama kuwa har an kira Magrib, gashi koh rabin gyaran bata yi ba.
Sosai ta fara sauri dan kuwa yau tasan ta shiga uku a hannun Rabi'atu ga kuma ɗaku na uku ne a cikin part ɗin nasu wanda duk sai tabi ta gyara su, gashi tunda ta dawo bataji muryar Ummar su ba, da alama dai bata dawo daga wurin aiki ba yau ɗin dawuri.
"Kutumar kan Uban chan" ta faɗa tsaye daga bakin ƙofar falon.
"Dan Allah Anty kiyi haƙuri, ƴunwa nakeji shiyasa banyi sauri a aikin ba" ta faɗa kamar zatayi kuka.
"Au bakici abinci ba koh?, zakiga bakici abinci ba dan Ubanki" ta faɗa tana bata mari a fuska sannan ta ɗaura da faɗin "Na baki minti goma ki gama tattara min cikin falon nan kiyi mopping ɗinsa mai kyau,kije ki ɗauko turaren uwarki ki sanƴa min."
"Toh" kawai ta faɗa tana cigaba da aikin nata da sauri.
Zama Rabi'atu tayi akan cushion tana aika mata da mugun kallo.
Itace bata gama aikin ba dawuri har sai da bakwai ɗin dare ya gifta kaɗan duk ta haɗa gumi sai kuka take sakamakon gajiya da kuma ƴunwa da takeji.
"Maida abubuwan ki ɗauko turaren wutar ki sanƴa min, gobe tunda bakuda makarantar safe kizo ki ƙarasar min da aikin."
"Muna da makarantar Boko fah gobe da safe."
"An biya muku kuɗin makarantar ne?."
Kai kawai ta jinjina mata hakan yasa ta daka mata tsawa tace "Da kai nayi miki magana?."
"Eh, an biya mana."
"Wuce dalla ki bani wuri."
Da sauri ta tattara kayan aikin ta fice daga part ɗin.
A komai part ɗin su Rabi'atu yafi nasu DEENAH kyau da tsaruwa dama kuma girma wanda shine ya kasance nasu DEENAH ɗin tun lokacin da Mahaifin su yake raye, amma tunda kawu ya auro amaryar sa Rabi'atu yasa ta a ciki Part ɗin ta daina samun isashhiyar gyara, ga kuma shegen ƙazanta a cikin ta, Rabi'atu irin matan nan ne da basu damu da gyara ba, ga kuma shegen hassada da baƙin ciki dama kuma sa ido a cikin ta, duk irin kayan da ta gani a jikin Ummar su DEENAH sai ta tada jaraba an siya mata irin sa idan kuwa ba haka ba tayi ta tada masifa da jarabawar tsiya kenan a cikin gidan, sosai ta ɗauki Ummar su DEENAH a matsayin kishiyar ta, dan kuwa ba ƙaramin kishi take da cigaban ta ba dukda mijin ta baya raye,amma bata zauna ba kasancewar tayi karatu sosai kuma har kwalin degree ne da ita, gashi kuma a yanzu tana shirin samun aikin Lawyer kasancewar abinda ta karanta kenan sai dai Rabi'atu batasan da hakan ba, da irin baƙin ciki da hassadar da zatayi mata ba kaɗan ba.
Fitar ta daga part ɗin ta hango Ummar su a tana girki akan Gas, da sauri ta ƙarasa tace "Ummah dama kin dawo?."
Kallon ta tayi tace "Na dawo, sai dai ban daɗe da shigowa ba, kinga yanzu ma na ɗaura girki."
"Amma Umma maiyasa baki dawo dawuri ba yau ɗin, kuma baki neme ni ba?."
"Aiki ne yayimin yawa a office shiyasa ban samu na kammala dawuri ba, ga kuma na wuce kasuwa yi mana siyayya, ban samu abin hawa dawuri ba, kuma ai na hango takalmin ki a bakin ƙofar Rabi'atu shiyasa ban damu da na neme ki ba, tunda yayanki yace min kina chan kina yi mata aiki, ashe ta dawo?."
"Toh Umma sannu da dawowa."
"Yauwa ƴar albarka jeki ajiye abubuwan hannun naki kizo kinji."
Da "Toh" ta amsa kafin ta shige ciki.
Ajiye abubuwan tayi a mazaunin su sannan ta shiga ɗaki ta ɗauko kaskon wuta da turaren wuta ta fito.
"Ina zaki dasu?."
"Anty ce tace na kawo mata nasa mata a ɗaki."
Shiru Ummar su tayi bata ce komai ba, hakan yasa ta wucewa.
Da sallama ta shiga nan ta sameta gaban TV tana kallo koh amsa sallamar ta batayi ba.
"Anty gashi nan."
"Ina wutar da za'a sanƴa turaren a ciki?."
Tsuru-tsuru tayi da idanu kafin tace "Babu wutar."
"Kamarya babu wutar?, ba yanzun nan naji muryar Ummar ku ba, bata hura wuta bane?."
"Eh, ba na mukubur ta hura ba yau ɗin."
"Tohh, a miye ta hura?."
"A Gas ne?."
Ta6e baki tayi tace "Manƴa, jeki anso min kaskon wutar ta na electric ɗinnan kizo ki samun a shi."
"Ai ya 6aci" ta faɗa tana kallon ta.
"Ya 6aci, kamarya ya 6aci, wa ya 6ata?."
"Tun rannan ne da kika ce na kawo miki, har ya faɗi a hannun ki ne bai sake kawo wuta ba."
Ta6e baki tayi tace "Bani turaren."
Miƙa mata tayi nan ta buɗe tare da kaiwa hancin ta, sosai yake da ƙamshi maimakon ta yaba sai tace "Ina wannan ɗinnan da nakejin ƙamshin sa har nan idan tasa ɗinnan?."
"Shi ɗin ya ƙare kuma bata sayi sabo ba."
"Mttssww, jeki kar6o min jafaran ki samin shi a haka nayi maneji" ta faɗa cikin yatsina tana ajiye turaren a gefen ta.
Ficewa tayi dan kuwa tasan shikenan kuma turaren ba zai sake dawowa wurin su ba.
Jafaran ta ɗauko ta kunna mata a falon harda cikin ɗaku nan part ɗin duka, inda duk datti ya cika su babu gyara tayi ficewar ta.
Koh da ta koma ta samu Ummar ta tasa mata ruwan wanka a kettle nan tayi wankar ta shirya cikin riga da wandon baccin ta, tayi sallahn Magrib ɗin da batayi ba, sannan ta zauna akan sallayar tana jiran a ƙira Isha'i tayi.
Bayan duk sunyi sallahr Isha ne kuma duk suna zaune a falon nasu suna kallo kasancewar girkin daren bai ƙarasa bane Jafar yace "Umma bari kiga wani abin mamaki" ya faɗa yana zuwa ya ɗauko jakar Islamiyyar sa.
Da kallo ta bisa nan DEENAH tace "Yaya, ka tsaya nima bari na ɗauko nawa" ta faɗa tana fita da gudu taje ɗaki ta ɗauko ta dawo fuskar ta ɗauke da murmushi.
"Umma kinsan mene?."
"Ina zan sani, ku faɗamiki meke saku farin ciki haka nima na tayaku."
"Zamu nuna miki amma sai kin rufe idanun ki."
"Tohh" ta faɗa cikin ɗan zaro idanu.
"Umma ki rufe" cewar DEENAH tana zagayawa ta bayan ta ta rufe mata fuska.
Dariya tayi tace "Toh na rufe, ku nuna min."
Ciro takardar da ZEEYAD yayi zanen su a jiki yayi ya buɗe page ɗin tsakiya inda Zanen hoton Ummar su yake ya buɗe yace "Umma kada ki buɗe sai na ƙirga uku."
Nan ya gyara takardar yana nuna wa a saitin ta kafin ya shiga ƙirga "One, Two, There....Surprise" ya faɗa da ƙarfi lokacin da DEENAH ta buɗe mata idanun nata.
Baki ta buɗe kawai cike da ɗumbin mamaki tana ƙarewa hoton kallo, hannu tasa ta amsa tana cigaba da kallo cike da mamakin da take ciki tace "Who drew this, did you?" ta faɗa cike da farin ciki tana kallon sa.
"Noo" duk suka haɗa baki wurin faɗa kafin yace "Abokin mu ne yayi."
"What really?, he is so very talented, wannan ne hobby ɗinshi, ya sanni ne?" ta
tambaya.
"Bamu saniba, kawai ya zana ne, bayan munyi masa kwatancen kamannin ki, bari kiga nawa da na DEENAH" ya faɗa tare da buɗe page ɗin baya take hoton sa ya bayyana.
"Wowww" ta faɗa.
"Umma kiga nawa, har biyu ya zana ni" ta faɗa tana kawowa kamar zata shigar da takardar fuskar Ummar ta.
Amsa tayi cikin farin ciki ta shiga ƙarewa DEENAH dake manne a jikin takardar kallo.
"Wowww, look at my cute gorgeous daughter" ta faɗa cikin murmushi tana kallon DEENAH.
"Umma kinga wanda ya zana mu, mu biyu nida DEENAH."
Amsa tayi ta shiga dubawa tace "Masha Allah, abokin ku yaro ne ya zana wannan abin i can't believe my eyes, lallai wannan yaron nada baiwa ta musamman, toh kuma nawa kuka bashi?" ta faɗa cikin murmushi tana kallon su.
"Bamu basa koh biyar ba?."
Baki ta buɗe tana kallon su kafin tace "Lala baku kyauta ba ƴaƴan nan, mutum yayi muku zanen nan kuma baku basa komai ba, lallai yanada kirki sosai."
"Umma ana bada kuɗi ne idan anyi?."
"Ehmana, kuɗi sosai ma kuwa, ki ganki fah ke sak ya zana babu bambamci, kuma kice baki basa komai ba."
"Kenan Umma kina nufin zai iya yin na kuɗi, idan yayi zanen mutane su basa kuɗi?."
"Yeah it's a good ambition ai, just take a Look masu baiwa ta musamman ne zasu iyayin wannan zanen, sannan kuma su iya neman kuɗi dashi, da akwai wadanda aikin su kenan kuma ba ƙaramin kuɗi suke samu ba, musamman ma ace a ƙasashen turai yake, suma girmama irin masu wannan baiwar sosai da sosai and with this he can make alot of billions idan Allah yasa masa albarka a ciki."
Kallon juna shida DEENAH sukayi suna waro idanu cike da mamaki kafin kuma su tsinkayo muryar Ummar su na faɗin "Wanene abokin naka, sannan a wane gida yake?."
Kallon juna sukayi yayin da fara'ar fuskar su ke ɗaukewa..............
*Dan Allah ku dinga yimin sharing mana saboda Allah👏🏽😩*
*MHIZZ JIDDHERR...........✍🏽*
[8/30, 9:32 AM] Mhizz Jiddherr❤️: *Z E E Y A D*
```[The Abandoned Prince]```
*NA*
*JIDDAH BINT MUHAMMAD*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION*
_Kada wacce tayimin Kuka a page ɗinnan😩_
*011...*
_*Banida lafiya ku sani a addu'oin ku, banyi editing ba*_
...............Da kallo suke bin juna wondering wane irin amsa yakamata su bawa Mahaifiyar tasu, Jafar ne yace "Umma ai basuda gida, shi kaɗai ne yake rayuwa."
"Um!, bangane ba, kamarya shi kaɗai yake rayuwa?."
"Umma Balarabe ne fah, ba ɗan nan ƙasar bane, kuma bashida wurin kwana da zama sai gindin ƙatuwar bishiyar dake hanƴar islamiyyar mu."
"Balarabe, then toh a'ina ya san ku har kuka zama abokai dashi?."
"Shine wanda DEENAH take kaiwa abinci kullum."
"Shine yayi wannan zanen?."
"Eh Umma kuma fah bayajin hausa ma, sai turanci kaɗai" cewar DEENAH tana kallon ta.
Tunani Ummar tasu ta shiga yi kafin ta rufe takardun tace "Ku maida cikin jakan ku, bari na dubo mana girkin" ta faɗa tana tashi ta fice zuwa waje.
Da kallo suka bita kafin Jafar ya kalli DEENAH yace "Ya naga fuskar Umma ya canza?."
"Koh ka sani zata ce kada mu sake kula shi tunda bamu sanshi ba" ta faɗa kamar zatayi kuka.
"Umma tana da kirki ba zata raba mu dashi ba."
Takardar ta sake ɗauka tana sake kallon hoton dake jiki fuskar ta na fitar da murmushi...........
******************
...........Washe gari bayan gari yayi haske tuni sunyi shirin makarantar su kowa ya sanƴa uniform ɗinsa inda Ummar su ma tayi shirin fita aiki.
Kallon Umma dake ta sauri tayi tace "Umma baki fah zuba min abincin ba."
"Wane abinci kuma DEENAH?" ta faɗa tana kallon ta.
"Abincin da zan kaiwa abokin Yaya."
"Ina shi yayan