Showing 234001 words to 237000 words out of 260321 words

Chapter 79 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42690

na gama qunsar takaicinka Bashir kuma ka qaddara cewa naka shafin baqin ciki da zubda hawayen yana dab da budewa a rayuwa” Ina gama fadar haka na wuce daki na barshi a tsaye yana bina da kallo, jiki a sanyaye kamar wanda aka zarewa laka ya juya ya fice daga gidan.

“Allah yasa da gaske kikeyi, dukda da ciwo amma idan kika daure kika mayar da komai ba komai ba Ma’u zakiga ribar hakan a gaba. Bance ki dena son Bashir ba amma Ki share daga zuciyarki, ki gayawa kanki koda Bashir ko babu shi zaki ci gaba da rayuwa ki kuma tsohuwar Asma’un ki wani koke koke duk ba naki bane abinda be faru ba shi ake tara wanda ya faru kuwa sedai a kiyaye maimaita irinsa.

Kina kallonsa yanda yake abubuwan sa tamkar babu abinda ya faru, gidan da kika fita ya dakko wata ya saka dan ya nuna miki dake din da babu ke babu abinda ze chanza masa kuma walwalarsa yakeyi amma ke yana takalarki da duk abinda yasan ze quntata miki kuma ki biye masa ina dalili?

Ai wallahi yanzu shi ya kamata ki nunawa yayi babban Rashin da baze taba maida irinsa ba, ki tattara hankalinki guri daya ki koma aikin ki, ki ci duniyarki da tsinke dama ce yanzu ubangiji ya baki ta ki samu duk abinda kika rasa a baya.

Kin auri Bashir saboda kina mugun son sa yanzu kingani ga damar ki ta se irin mijin da kike so zaki samu kin kuma san kura kuren da kika tafka a zaben baya yanzu zaki kiyaye su shine kuma zaki zauna kina baqin ciki da abinda Allah ne ya so ki ya qwato miki yan cin ki.

Koda ace gaba zaki koma gidan Bashir Ma’u ina so kafin lokacin yasan kima da darajar ki ta yanda koda Allah ya sake qaddara zama a tsakaninku zeyi miki ruqo na gaske da bare sake bari ki kufce masa ba, amma kin zauna abu kadan ya jangwaleki kiyita masifa yana jin dadi haka mana Ma’u ki farka daga wannan magagin da kikeyi” haka Anty ta cigaba da gaya mun maganganu har seda ni kaina na ji haushin kaina kafin ta barni ta koma gida.

BASHIR
Sosai yanayi da kalaman Ma’u suka dake shi, babu abinda yafi tayar masa da hankali irin hawayen daya gani suna zuba daga idonta, me yasa shi a koda yaushe yake zama silar kukanta ne? Wai takamaimai meye dalilin daya saka ya kasa bawa Ma’u irin kulawar data kamaceta tukuicin sadaukarwar ta a gare shi?.

A duk sanda ya kalli cikin idonta yana hango tarin so da qaunar sa a ciki irin wanda yake saka mutum aikata komai domin farin cikin wanda yake yiwa wannan soyayyar amma a yau sam bega hakan ba illah tarin tsanar sa da dana sanin kasancewa dashi daya hango a cikin idanunta da suke zubar da hawayen nadama.

Harga Allah yana son Ma’u, yana kuma tsoron kar wannan abun daya aikata ya saka ta tsane shi domin a duk sanda So ya koma qiyayya yana zamowa me zafin gaske, idan kuwa har ace tarin so da qaunar da Ma’u take yi masa suka rikide zuwa Qiyayya tabbas ya shiga gararin rayuwa dan kuwa babu wani ruwa a duniyar nan da ze ishe shi wanke kansa yayi hasken da zata kuma kallonsa harta maida masa da wannan so da qaunar daya rasa.

Abu daya ne idan ya tuna yake sakashi jin dama dama wato cikin jikinta, a qallah yana da watanni bakwai kwarara da ze taka duk irin rawar da yake so daga qarshe ko taqi ko taso ya mayar da ita dakinta a sannan kuma ko sama da qasa zata hade babu wanda ya isa ya saka shi ya qarashe sauran igiyar datayi musu saura a tsakanin su koda kuwa Ma’u zata ringa yankar naman jikinsa ne saboda qi sedai ya mutu sannan ta samu yanci amma badai ya sake sakinta ba wallahi.

Da wannan tunanin ya koma cikin gida, duk yanda yaso ya rarrashi yaran sunqi sauraren sa haka ya haqura ya qyale su, a cikinsu ma yafi tausayawa Faridah da take mace ita kadai, da Amnah tana nan bashida ko wacce damuwa yasan zata kula dasu tamkar Ma’u tana nan amma yanzu besan yanda zeyi da Faridah yasan bazata sakw da Amirah ba.

“Kodai na mayar da ita gurin Ma’u?” Ya raya a ransa,
“Kai amma ai in nayi hakan kuma na kwafsa na gama buyagin banza tun ba’aje ko ina ba kenan taga gazawata, haka zata haqura har ta sake da Amirah da sauqi ma tunda ba nisa Ma’u tayi ba kullum zasu ringa ganin ta a hankali ma zasu warware su saba da zaman kafin komai ya daidaita mu ci gaba da rayuwar mu cikin farin ciki” Alhaji Malam Bashir ya sakw ayyana hakan a ransa.

Da rana Amirah tayi iya yinta ta musu jalof din shinkafa taji busashshen kifi da nama, ganin Bashir na zaune data gama harda zuwa ta kirawo su suzo suci kai tsaye kuwa Aliyu yace bazasu ci ba.

“Yaya kaje kayiwa yaran nan magana su fito suci abinci mana ni naje sunce sun qoshi” ta fada tana zama a kusa dashi, seya miqe ya shiga dakin, suna nan jugul sun dena kukan dai amma kowa yayi tagumi.

“Oya muje muci abinci se mu fita yawo ko ina kuke so muje?” Ya fada yana tsugunnawa a gaban gadon da yan biyu suke zaune, su daman basu tsawwala ba dan ba wani fahimtar budurin da akeyi sukayi sosai ba kawai duk abinda Aliyu ya fada ne sauran se su mara masa baya shiyasa suka suke zaune a dakin amma tun dazu Ahmad yake zungurin tagwan nasa yana masa radar su fita shi ya gaji sa zama, daman yunwa suke ji dan haka suka miqe da saurin su ya kama hannu su suka nufi qofa.

“Baban Mami fa? Bazaka bi mu ba?” Ya sake fada yana kallon Abdallah daya rabe guri guda, se yaron ya maqe kafada yace

“Aa ni gurin Mami zanje”.
“Toh muje kaci abinci seka tafi Mamin ko?”

“Abbi nima haka” Farida ta fada kamar zatayi kuka. Se ya waiwaya yana mata murmushi yace
“Muje toh kuci abinci me son zuwa gurin Mami ya tafi wanda zamu je yawo mu fita toh” nan da nan suka hau murna suka bi bayansa banda Aliyu da Jafar da suke tsaye nan fuska kamar Hadari, shima be kula suba, ai su ba yara bane kamar sauran idan yunwar cikin su ta ishe su zasu fito su nemi abinci.

Haka suka ci abincinsu da yaran ya biye musu sunata labari, zuciyar Amirah kamar ta fashe tsabar baqin ciki, taso ace sunqi cin abincin in yaso ta huta da sake yi masa wani girkin da daddare seta ajiye abinta amma yanzu shine zasu wani fito suci gashi se wani biye musu yake suna surutu duk sun bata gurin ai kuwa bari su gana sedai su gyara ko kuma shi din yayi dan ta gaji wallahi.

Bashir kuwa suna gamawa yace suje gurin Mamin kafin ya shirya se su tafi, haka suka kwasa da gudu zuwa gidan be ko bi takan Amirah dake mitar an bata guri ba ya shige dakinsa ya shirya tana kallonsa ya ci kwalliya yace mata sun fita da yara kar tayi girkin dare zasu taho da abinci.

ASMA’U
Muna zaune shiru su Faridah suka shigo da gudu suna rige rigen fadawa jikina. Da murnata na tare su wata zuciyar tana cemun
“Badai ya haqura ya dawo mun dasu ba kai amma da kamar wuya”.

“Mami unguwa zamu je da Abbi yanzu Yah Amnah ki chanza mana kaya” Ahmad ya fada.

“Iye yan gatan Abbi to ai kayan naku suna can gidan kuma na jikin ku ma babu abinda sukayi zaku iya zuwa dasu” na fada ina duba rigunan jikinsu na cire musu rigar sanyin da na saka musu dazu saboda garin da dan sanyi sanyi yanzu kuma yanayin ya daidaita.

“Mami nima na bisu” Amna ta fada tana kallona, sena daga mata kai kawai alamar “Eh” da saurinta kuwa ta shiga daki ta hau shiri Faridah ma ta bita dan ita kayan ta ba dukka aka kwashe ba daman. Suna gama shiryawa muka jiyo horn dinsa daga waje sukayi mun sallama gaba daya suka fice.

Ajiyar zuciya na sauke me qarfi bayan fitarsu dan kaso saba’in cikin fargabar rabani da yarana da Bashir yayi ya kau dan a zatona ze rabani dasu ne kwata kwata ya hanamun ganin su amma indai har haka za’a cigaba komai ze zo da sauqi kenan.

Yan gyare gyarena na tashi na shigayi bayan na gama na hau kwaba musu cake na tafiya makaranta tunda basa zuwa da abinci acan suke basu harna rana shiyasa se nayi musu dan abin tabawa su tafi dashi bayan sun karya a gida shima Bashir na zuba masa to yanzu kuwa sedai Can Matar sa tayi masa indan zata iya su dai zan ci gaba da yi musu yanda na saba in zasu tafi na basu.

Ina cikin kwabin cake din Aliyu da Jafar suka shigo, ina kallonsu nace
“Aa ku ban da ku aka tafi yawon kenan?”

“Ban da mu, Mami akwai Abinci?” Jafar ya fada yana nufa yana bude tukunya, Aliyu kuwa kan deep frizzer ya hau ya zauna yana kumbura fuska,

“Ali mazan fama ya akayi ne ko kaima yunwarce ga abinci nan ku diba ku ci to”.

“Wallahi Mami watarana sena sumar da matar can idan ta sake shiga harkata” ya fada yana sake hura baki. Se na ajiye Mixer hannuna na juya dakyau ina kallonsa nace

“Wace mata zaka sumar kuma Aliyu?”
“Amirah mana” ya bani amsa kai tsaye.
“Kana jina ko Aliyu, karku kuskura kuce zaku saka abinda ya faru tsakanina da mahaifinku a rai har hakan ya shafi alaqarku dashi.

Rabuwar mu qaddarah ce daga ya rigada ya tsara iya lokacin da zamu zauna kunga babu abinda ze chanza hakan, sannan tsakanin ku da matarsa babu rashin kunya dan ba ita ta raba mu ba Allah ne ya kashe auran mu.

Koda wasa karna ji dayan ku yayi mata wani abunda ba daidai ba dan idan ma kunyi a maimakon ku ce kun rama abinda akayi mun qaramun laifi zakuyi aringa cewa ni na saka ku dan haka babu ku babu sabgarta. Duk abinda kuke nema a gidan baku samu ba kuzo nan shikenan”.

“Amma ki gaya mata wallahi Mami duk randa ta qara zagar mun uwa ko tace zata dakeni kafin ta fara ni zan doketa tam” Aliyun ya sake fada kafin ya sauka daga kan freezer ya fice daga Kitchen din gaba daya. A yanda yayi maganar hatta da muryarsa se najita kamar ta Bashir idan yana cikin fushi se kawai na bishi da kallo kafin nace
“Allah ya shirya ka ya rage maka wannan zafin zuciyar” se na juya kan Jafar dake kwasar abinci nace

“Meya hadasu da matar Babanku yake cewa ze daketa?”

GIDAN BASHIR BAYAN FITAR SA
Bayana Bashir ya fita seda Amirah ta tabbatar taji tashin motarsa alamar sun tafi ta sake leqawa taga basa nan kafin ta kulle qofar ta ciki ta yanda dole se an buga zata zo ta bude.

Dakin su Aliyu ta wuce kaitsaye, A zaune ta tatar dashi da Jafar suna magana sama sama tana shiga ta kama qugu daga bakin qofa cikin isa da taqama tace
“Ku tashi ku fito, kai Jafar kaje ka share abincin da qannenku suka zubar kai kuma Aliyu ga kwanukan can a Kitchen seka shiga ka wanke”.

A tsakanin su babu wanda ya tanka mata dan ko inuwarta basu kalla ba suka ci gaba da maganar su, wata Asharvta lailayo ta aika musu da ita kafin cikin Masifa tace

“Wato ga yar iska ina muku magana kunyi mun banza ba kuna zato zan zauna kamar jaka na dafa muku abinci ne a bata guri na gyara duk kuna zaune babu me tayani? Naga da uwar ku tana nan shara wanke wanke duk ku kukeyi mata dan haka yanzu ma lazim kuyi idan kuna so kuci abinci a gidan nan”.

“Seki bari wadanda suka bata suzo su gyara miki ai kuma aike ba uwar mu bace da zamuyi miki aiki, abinci kuma daman bamu ce ki dafa mana ba dan ko kin dafa bazamu ci ba. Kuma daga yau karki sake shigowa dakin nan idan ba haka ba se kin raina kanki Allah” Aliyu ya fada yana tsatstsareta da ido kamar wani Sa’anta aikuwa tayi kansa fuuu da niyyar kwasa masa mari ya goce hannunta ya bugi katakon gado.

Sosai taji zafi dan da qarfin ta ta kai mari ta riqe hannun tana girgizawa da cije baki Jafar ya kwashe mata da dariya kuwa nan da nan ta shiga zaginsu tana cewa

“Shegu yan iska marasa mutunchi wallahi se naci ubanku yau a gidan nan naga me kwatar ku” bata daddara ba ta sake yin kansu, seda taje daf da Jafar zata kai masa Duka ya matsa da sauri kusada Aliyu daya harde hannu a qirji yana ayyana abinda zeyi mata idan ta kuskura ta tabashi, a yanda yake jin haushin ta badan wani abu ba da wallahi rufeta zasuyi su mata shegen duka dan daga shi har Jafar din masu manyan gabbai ne girmansu ya zarta shekarunsu.

Yana cikin wannan tunanin ta kuma kawowa Jafar dake mata dariya duka tana aunawa Uwarsu ashar ai kuwa ya saka mata qafa ta baya ta tafi kamar zata fadi kafin tayi gaba ji kake Qum ta buga goshi a bango da qarfin gaske kafin kace me gurin ya tashi.

Ihu ta kwalla tana shafa gurin dan ta bugu ba qarya ji tayi kamar ma har idonta buguwar, tana kuka tana zaginsu suka tsallaketa suka fice daga gidan ma gaba daya.

Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku

BONONZA; BONONZA;BONONZA;

Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K


MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI
KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
08162859027🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 62

YUSUF

Baze iya misalta irin murna da farincikin daya tsinci kansa a ciki ba jin abinda Ma'u ta fada. A sukawane ya fice daga gidan yana shiga motarsa Driver yaja suka tafi,

Tun kafin su fita daga Get din Estate dinsu Ma'u ya rangadawa Alhaji Qarami waya baya so ya bata lokaci ballantana ta dawo ta chanja magana dan yasan koda Ace abinda tayi niyyar gaya masa kenan to Juma'ar data yanke harda tagomashin bacin ran Bashir ya saka.

Sanda ya gayawa Ahaji Qarami maganar se ya zamana tsakaninsa da Yusuf din har an rasa ma wanene yafi wani murna nan take yace masa ba matsala ya gayawa mutanensa idan sun shirya gobe suje yanzu ze kira Baffan su ya sanar masa.

lafewa yayi a cikin kujerar motar yana sakin murmushi ransa fes jinsa kawai yake kamar wanda akayiwa Bushara da Aljanna tabbas ya yarda mahaqurci mawadaci kuma Allah shine meyi a sanda yaso ba'a saka shi ba kuma a hana shi.

Hajiyar ya dannawa kira dan da ita ya kamata ya fara raba wannan abin Farin cikin ringin biyu ta daga ckin kamilalliyar muryarta ta dattijai ta yi masa sallama.

"Hajiya barka da dare, Albishirinki Hajiya" Ya fada a jere
"Barka dai Babangida wane abin farin ciki ne haka ya faru da har muryarka ta gaza boyewa ko taqaddamar tikitin takarar taku ce ta qare kayi nasara?" Ta fada a sake daga jinta irin mutanen nan ne masu sakewa sosai da yaransu

Wani murmushi ya saki kamar yanagabanta kafin yace
"Wannan ai ba komai bane akan wannan albishir din Hajiya ki canka da kanki wane abu ne kike zaton ze sakani farin ciki haka?"

Shiru tayi se can tace "Asma'u, nasan dai a yanzu idan ba zancen takara ba toh sedai ita din nasan dai wadannan sune manyan burikan ka a rayuwa"

"Kin canka Hajiya yau Ma'u ta amsa da kanta ta bani damar na tura magabata na a daura mana aure wannan Juma'ar me zuwa dan haka Hajiya ki gayawa su Baba Sale idan ze yuwu gobe idan Allah ya kaimu suje, zan tura miki da Lambar Babban Yayansu se ki bashi suyi magana suji ina ne zasuje neman auran".

"Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah, Babangida kaga abinda nake gayamaka ko? Ita rayuwa kabi ta a sannu. Duk yanda kaso da faruwar abu idan Allah be kawo shi ba haka zaka haqura. Yanzu kaga ribar haquri ko? Allah ya tabbatar da Alkahiri yasa yin na Allah ne, nayi murna nayi murna Babangida Allah yasa za'ayi damu bari na kira Kawun naka yanzu kuwa na sanar masa na tabbatar shima zeyi farin ciki da wannan Al'amari dan ko shekaran jiya dayazo seda yayi mun ciwon baki akan zancen auranka yace wasu da yawa ma basu yarda kana da aure ba ko wannan ze iya kawo maka tangarda a cikin tafiyar siyasarka" Hajiya ta fada cikin tsananin murna.

"Toh ai yanzu ciwon baki ya qare Hajiya in sha Allahu ki dai kirashi yanzun dan Allah kuyi magana a samu goben aje"

"Toh sarkin zumudi gobe ai yayi wuri ina lefinzuwa jibi haka?" Ta fada cikin tsokana, da sauri ya tare ta da cewa

"Haba Hajiya wane irin jibi kuma? Juma'a fa tace a daura aure kuma yau litinin nidai gara suje goben ayi komai. Mansur yana nan duk abinda ake da buqata a karba a hannunsa kafin na shigo"

"Toh Allah ya tabbatar mana da Alkahiri, bari na tura ayi mun magana da kawun naku nasan yanzu yana waje tunda ba'a dade da idar da sallah ba beci ace ya tafi gida ba" da haka sukayi sallama shi murna ita murna.

Ranar qaryar bacci duk iya satar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login