Showing 126001 words to 129000 words out of 260321 words

Chapter 43 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42672

yana ta daga mana hannu.

Mun sauka qasar madina lafiya, sosai na kama ibadah ta dan ko kusa ban bari hidimar yara ta hanani ribatar goman qarshe da muka shiga ba. Kwanan mu biyar muka tafi Makka muka dauki Haramin umarar mu, bayan mun sauke nan ma a kullum ina Masallaci ina ibaduna, kwanan mu biyu aka sallace banyi sanya ba na duqufa sosai ina ta kaiwa Allah kokena. Adduata duk akan Iyayena, Yarana da Mijina tareda sauran Al'umar musulmi baki daya.

Ranar Juma'a data kama Lahadi zamu dawo Nigeria da yamma mun fita kasuwa da yara wayata dake cikin jaka ta ringa qara, seda muka shiga shagon nacewa Amna zu zagaya su dauki abubuwan da suke so kafin na dakko wayar na duba,

Rahma ce Amaryar Amiru da mamaki nake kallon tarin missed calls dinta gida shida se na fara qoqarin kiran ta dan tabbas nasan ba lafiya ba irin wannan kiran nayi sa'a kuwa ringing biyu ta amsa wayar.

"Maman Aliyu wane labari naji dan Allah kice mun ba gaskiya bane" ta fada ba tareda ta bari ko gaisawa munyi ba. Se naji gaba na ya fadi, daman dauriya nakeyi, a kwanakin kullum cikin faduwar gaba nake da quncin zuciya na rasa me yake damuna shiyasa ko da yaushe ina cikin Harami ina sallah ko karatun qur'ani su kadai suke sanyayamun zuciya na kuma fawwalawa Allah ya iya mun koma menene yake tun karo ni dan a duk sanda naji irin wannan yanayin to tabbas wani mummunan abu ne yake shirin samuna.

"Maman Aliyu bakya jina ne kin yi shiru k baki samu labarin abinda yake faruwa bane" Rahma ta sake fada abinda ya fito dani daga duniyar tunanin dana luluqa.
"Wani abun ne ya faru Rahma ban sani ba wallahi Allah dai yasa lafiya" na fada a sanyaye, se tayi shiru kafin cikin wani yanayi tace

"Tunda baki sani ba bazakiji a bakina ba Maman Aliyu amma ki kira Yaya Bashir yanzu base anjimaba kiji komai" kafin nace wani abu ta yanke wayar.

Seda na kira Bashir sau uku amma be daga ba, ganin magriba ta kusa sena haqura muka qarasa siyayyar mu muka koma masauki akan zuwa bayan Isha se na sake kiransa idan na dawo daga masallaci amma sam na kasa samun nutsuwar zuciya.

Kira na ringa doka masa abinda ya bani mamaki ko ince ya fara bani tsoro ganin na kira yafi sau Ashirin wayar tana qara amma ba'a daga ba sena mayar da akalar kiran nawa kan Amiru dan na sake kiran Rahman itama bata amsa ba.

Kira biyu ana ukun Amiru ya daga. Cikin sanyinsa muka gaisa se mukayi shiru gaba daya ni ina jira naji yace wani abu ne ya samu Bashir shima yana jiran jin dalilin kiran, ni na katse shirun da cewa

"Baba Amiru Bashir kunyi waya da Bashir kuwa yau"

"Eh mun yi waya bamu dade da rabuwa bama na barshi a gida yanzu na fita"

"Oh yana Gombe ashe, nayita kiran wayarsa ne amma ban samu ba shine nace bari na kiraka naji ko kunyi magana yau shikenan se an jima" na kashe wayar. Daga yanayin sa sam banji cewa wani abu ya faru ba to me yasa Rahma zata kira ta daga mun hankali??

Qoqari nayi na yakice tunanin daga zuciyata muka shirya muka tafi masallaci, ina cikin yin shafa'i da wutri wayata da sam na manta ban saka ta a Silet ba ta dauki qara lokaci daya gaba ya yanke ya fadi da har seda na dafe qirji na shiga nanata Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un a zuciyata.

Ina sallamewa na jawo wayar na duba, Alawiyya ce ta kirani, sena miqe kawai ina shirin bin bayanta wani kiran ya shigo sena yi saurin daga wa na saka wayar a kunnena.

"Ma'u bansan daga ke har mijinki yan kutumar uba bane se yau, anya ba asirce ki yayi ba kike zaune dashi ya kulle miki baki? yanzu ace za'ayi miki kishiya duk duniya ki kasa gayawa kowa sema ki tsallake kibar qasar wai kin tafi Umara sedai kawai muji a gari, shikenan ai Bashir ko gaki gashi nan tun ba'aje ko ina ba kin fara karbar saka makon ki a hannunsa".

A duk maganganun Alawiyya babu abinda na tsinta banda kalmar kishiya data fada, seda na da dage piller masallaci jin jiri yana neman kadani.

"Lallai wato ga mahaukaciya tana magana kin yi mun shiru ko Ma'u, shikenan amma ki tabbata kin nemi wata yar uwar da zaki raba baqin cikin Bashir da ita dan wallahi bazaki dora mun hawan jini da takaicin mijinki ba, mtsw" taja tsaki.

Seda nayi da gaske na iya bude baki nace
"Alawa ni duk ban gane abinda kike nifi bane waya gaya miki Bashir yayi aure?"

"Kina nufin baki sani ba to maza shiga whatsapp yanzu na tura  miki hotuna kigani se ki tabbatar wa idon ki" tafada kafin ta kashe wayar.

Wata wawuyar Ajiyar zuciya na sauke lokacin da naga hotunan da Alawiyya ta tura mun. Hotunan Bashir ne da Amirah tareda sauran yan uwan su wanda na tabbatar na daurin auran Amiran ne amma ai na zata se gobe Asabar aka saka a katin data tura mun kuwa.

Da daddaya na ringa binsu da kallo Bashir yaci uwar Babbar riga fara gasu Addah nan baki ya gonar Auduga an washe shi ina shirin bude na qarshe da naga kamar kati ne kiranta ya sake shigowa.

"Yanzu kin yarda ko kuwa dai kina tantama" ta fada".

"Haba Alawa haka kawai kin saka hawan jinin dare daya ya nemi kamani a marrar nan kike mun zancen kishiya. Amirah cefa kin manta da bikinta akeyi hotunan daurin auren nefa duk kika bi kika kidima kanki".

"Allah ya yafe miki Asma'u ya nuna miki hanyar daidai, shikenan tunda ni na kidima kaina ba lefi idan kika dawo hayyacin ki se muyi magana dan naga alamar kwakwalwarki ta juye Ma'u kina buqatar saiti amma ki nutsu ki sake kallon hotunan dakyau ga wasu can ma na qara tura miki" Alawiyya ta fada sannan ta yanke waya.

Hotunan na sake bi da sababbin Videos din data turo mun na Amirah data sha kwalliya tayi kyau suna ta shaqiyanci, akan katin dazu na sake tsayawa na bude shi na fara karanta abinda aka rubuta.

"DAURIN AURAN ENGINEER BASHIR AHMAD DA AMIRAH MURTALA" Abinda na gani an rubuta kenan, daga Bashir din har Amirah ko daga bacci na farka naga sunansu na san sune ballantana wannan ga gurin daura auran nan masallacin dake layin gidan Addah ne hakan ya sake tabbatar mun da gaske dai Nawa Bashir din ake nufi bawai wani na daban ba.

Wayar hannuna ce ta dauki qara, ban san ya akayi na daga kiran ba nidai naji muryar Anty Halima tana cewa

"Asma'u dagaske ne ko wasa yanzu a duniya Bashir ya rasa irin cin Amanar da ze yi miki se ya tura ki wata qasa sannan ya daura da yarinyar da kika riqe?"

Iya abinda naji kenan lokaci daya tsikar jina suka zuba  kaina yayi mun dum kamar wadda aka kwadawa guduma daga nan ban sake sanin inda nake ba se farkawa nayi na ganni a gadon Asibiti.

Waya ta da nagani a gefena na jawo na sake budo hutunan dazu dan in tabbatar gaskiya ne ko qarya. Ina kunna Data kuwa kamar ana jira messages rututu suka fara shigo mun alamar dai magana ta baza gari ga status din yan gidan su   Se a sannan ma naga status din Jama'a ashe an yi posting hotunan sosai hankali na nae bekai kai ba.

Tun yaushe aka shirya hakan? Daman Bahsir da Amirah suna soyayya ina zaune dasu ban taba ganin wata alama ba?

Wai ma me nayi wa Bashir a rayuwa dana cancanci irin wannan sakayyar bayan tarin dumbin sadaukarwa da Alkhairan da ni da yan uwana muka yi masa.

Wane irin mugun hali ne dani da har ya kasa gayamun zeyi aure sedai naji a duniya bayan daya rigada ya daura me nayi masa dan Allah?

Sannan Ace duk matan duniya manya da yara farare da baqar fata Bashir ya rasa wadda ze aura se Amirah yarinyar dana gama bautawa tun tana qanqanuwarta har girma yanzu ace da ita zanyi zaman kishi yarinyar data  san sirrina, na bude mata duk wasu sirrika da nake taqama dasu saboda yanda na dauketa tamkar qanwata na gyarata saboda ta samu daraja a gurin mijin da zata aura yanzu ashe duk mijina nayiwa wannan tanadin? Ni za'a yaqa dasu?

"Yah ubangiji kaika halicceni, kai ka tsara mun rayuwata tun kafin wanzuwa ta a doron duniya Allah kasan zan iya shi yasa ka dora mun na roqeka nayi tawassali da sunayen ka tsarkaka nayi tawassali da Annabin ka Muhammad SAW Allah in har sunyi dan su cutar dani na roqeka karka basu ikon ganin gazawa ta, ka sanya min juriya da dakiyar tun karar duk wani qalubale da zan fuskanta a rayuwa. Ubangiji ka sauqaqa mun dau wani ka bani zuciyar da zan iya dauka" na fada a fili ina fashewa da wani irin kukan baqin ciki.

Wallahi ko kadan banji haushin auran da Bashir yayi ba, da ace wata ce daban zan shanye na danne bazan taba nuna masa komai ba har in ga iya gudun ruwan sa amma Amirah fa Amiran Addah me yasa se Ita? Da ace Ummi qanwarta ya aura nasan bazan ji baqin ciki irin wanda nake ji yanzu akan auran Amirah da yayi ba.

"Amirah zata dawo gidan nan kuma a sannan baki isa ki koreta ba" kalaman Addah suka dawo mun a kwakwalwa ranar da na kori Amirah daga gidana a Gombe. Ashe abinda suka shirya yi mun kenan daga ita har Dadan suka dakko kishiyata suka kawo mun da nufin na gyarata su kuwa wasu irin mutane masu saka Alkahiri da sharri ta ina na kuskure musu a rayuwa da suka zabi hukunta ni ta irin wannan hanyar?

Kuka na ringayi wanda tun likitocin da suka dubani suna bani haquri har suka haqura sukayi shiru, bana buqatar sauran bata lokaci a qasar tunda daman ba dan Allah ya turani ba dan ya aiwatar da nufin sa ne to yaci galaba amma nima dole na koma Nigeria muyi wacce zamuyi da Bashir dan bazan taba hada miji da Amirah ba.

Yana da damar ya auro mun mata uku mu zauna amma ba Amirah yarinyar da nakewa Kallon Yata ita ce ze hadani kishi da ita baze sabu ba.

Sanda na koma Hotel din da muke na tarar da yara zuru zuru dan da aka kaini Asibiti can suka koma saboda a qa'idar su ba'a barin dan jinya.

"Ku hada kayan ku yau zamu tafi" na fada ina hargitso duk abinda hannuna ya kai kansa ina sakawa a jaka. Seda na gama sannan na tuna da ai Passport dinmu ma baya hannunmu yana gurin Agent din da Bashir ya hadamu dashi, wayata na dauka na shiga kiran nayi sa'a tana shiga ya daga.

"Malam Isah kayi mana booking jirgi idan da akwai Yau ka, ka fada mun kudin ko nawane zan biya wani abu ya taso mun bazan iya jira har se gobe ba" na fada ba tareda na amsa gaisuwar daya fara mun ba.

"Amma Hajia me ya faru haka, bayan haka kuma ai Ticket din ku bana komawa Nigeria bane Dubai zaku wuce daga nan na zata ai Engineer ya gaya miki ma"

"Isah dakai da Dubai din da Engineer kunci abu ta kazan ubanku" na lailayo wata Ashar me maiqo da ni kaina bansan na iya ta ba na kora masa kafin na ci gaba da cewa

"Ka kawo mun passport din mu nan da Awa daya idan ba haka ba wallahi se nayi qarar ka nace safarar mu kayi, kasan ina da duk wasu bayanai naka da zan bayar ka kuskure lokacin baka zoba ka gani".

"Kiyi haquri hajia ku shirya yanzu zan turo mota da zata kaiku Jiddah ni ina can yanzu haka akwai jirgin da ze tashi yau da daddare bari na bincika idan da akwai guri se a siya" Isah ya fada jin abin yafi qarfinsa.

A dakin muka bar kusan rabin kayan mu dan bana buqatar abinda ze bata mun lokaci bate har aje ana maganar wani awon kaya ko wani abu muka hau mota se Jiddah gaba daya ma gani nayi motar bata sauri, ina ma ace zan iya rufe ido na ganni a Nigeria, ina buqatar naje naga da wadanne idanu Bashir da danginsa zasu kalleni.

Mun samu jirgi amma se munyi jiran Awa goma sha biyu kafin tashinsa, haka Isah ya nema mana hotel gaba daya ya rasa meya faru haka gashi kiran duniya Bashir yaqi dagawa daga qarshe ma ya kashe wayar gaba daya Asma'u kuwa bega fuskar da ze mata tambayar abinda yake faruwa ba ma dan haka yaja Aliyu yana tambayarsa ko mutuwa akayi

"Nima ban sani ba, kawai daga Masallaci aka kaita Asibiti kuma data dawo mun kasa tambayarta abinda ya faru idan mukaje gida koma menene se mu gani" Aliyun ya bashi amsa.

Haka muka hawo jirgi se Nigeria ya sauke mu a Kano,Asuba ranar lahadi muka sauka tun a AirPort na samu shatar mota ta kwashe mu kafin Goman safe mun sauka a Gombe muka ci burki a qofar gidan su Bashir cikin Sa'a nayi kyakykyawan gamo da Ango Bashir da tun daren Alhamis rabon da ya sake daga wayata.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 39

A qofar gidan motar mu ta tsaya, idona akan Bashir da suke tsaye tareda wasu mutum biyu da ban gabe su waye ba.

“Ku jirani karku fito” na fadawa yaran, seda na yi kokawa da duk wani rauni da karayar zuciyar daya taso mun kafin na bude motar na fito ina gyara mayafin kaina gaba daya mutanen gurin suka bini da kallo banda Bashir da tunda muka hada ido ya maida kansa qasa kaman wanda aka kama yayi qarya.

Kai tsaye cikin gidan na shiga, nayi sallama ina jiyo hayaniyar su daga cikin dakin Dada amma ba’a Amsa ba dan haka na nufi can din, har na kai bakin qofar naji an kira sunana, sena waiwaya.

Alhajin su Bashir ne yana tsaye daga qofar dakinsa ya yafito ni da hannu sena juya na koma gurinsa.

Ina durqushe a gabansa kusan minti biyu kafin yaja numfashi yace dani

“Asma’u kiyi haquri nasan an cutar dake amma zan roqeki Arziqi kar kice musu komai yanzu, ki barsu akwai ranar da su da kansu zasu maidawa junan su martanin abinda sukayi miki.

Na sani Qarin aure ba haramun bane amma ta yanda aka shirya naki sam be kamata ba. Ya zama zamba cikin aminci. Ki sani Ita Amana daya ce kuma wanda yacita baya taba zama lafiya, idan har Bashir da uwarsa sun qulla wannan aure dan su ci mutunchin ki Asma’u in Allah ya yarda muna raye ko mun mutu se sunga sakayyar cin Amanar da sukayi miki.

Ina qara roqonki da kiyi haquri, ki qara akan wanda kike yi in sha Allahu bazaki tabe ba, duk me neman gazawarki akan idonsa zakiyita ci gaba da yardar Allah”.

Kuka nakeyi dagaske a raina ina hasaso irin tarin qaunar da na nunawa Bashir da Ahalinsa, a tsahon zamana dashi kusan shekara goma sha uku yanzu bazan iya cewa taka maimai ga wani abun laifi daya taba hadani da wata daga cikin su ba, a kullum cikin kyautata musu nake iya qarfina kuma duk albarkacin so da qaunar da nakeyi wa Bashir din ce ta shafi su amma ace a gurinsu basu da abokin hamayya seni.

Sosai nasha kuka na ba tareda Baba ya hanani ba in banda “kiyi haquri Asma’u” babu abinda yake cewa.

“Naji zan haqura Baba bazan tanka musu ba amma kayi haquri bana jin zan iya ci gaba da zama da Bashir. Bazan iya ci gaba da zama cikin Ahalin da basa qaunata ba Baba. Sannan Baba Amirah fa, yarinyar dana raina da hannuna ita zan hada miji da ita wallahi bazan iya ba.

“Zan bi umarnin ka a yanzu zan koma ba tareda na cewa kowa cikin su komai ba amma Baba karka roqeni ci gaba da zama da Bashir saboda ina girmamaka bazan iya tsallake unarninka ba amma tabbas zan cutu. Zuciyata zata iya bugawa a dalilin haka muddin zan zauna inuwa daya da Amirah a matsayin kishiyata” na fada cikin sheshsheqa me qarfi.

Se Baba yayi murmushi wanda da ganinsa na takaici ne kafij yace
“Asma’u ke Yarinyar kirki ce sannan abar Alfaharin duk Miji me hankali da yayi katarin samun irin ki sannan ko wanne uba zeyi alfaharin zamtowarki Suruka a gare shi.

Bazan so na rasa nagartacciyar suruka irin ki a cikin zuria’ata ba domin ke din mayafi ce da kika lullube Bashir duk kuma ranar da wannan mayafin ya yaye ba baki nayiwa Bashir ba tabbas se rayuwar sa ta shiga cikin gararin rayuwa.

Idan har ki ka ce bazaki ci gaba da zama da Bashir ba ni me tsaya miki ne in tayaki kwatar yancin kanki amma yanzu kije ki samu nutsuwar zuciya, karki yanke hukunci cikin fushi idan kika nutsu duk abinda kika yankewa zuciyarki ki dawo ni ki gaya mun in Allah ya yarda zan baki goyon baya dari bisa dari ki share hawayenki yanzu”.

“Baba bana tunanin ina da buqatar yin wani dogon nazari ka taimakeni kawai kasa Bashir ya sawwaqe mun dan ina da yaqinin ko ba yanzu ba watarana se sunyi nasarar fiddani daga dakina” na fada cikin kuka, se ya tare ni da cewa

“Haba Asma’u ke da na sanki jaruma ya zaki karaya tun yanzu ki bada qofar da za’a ci galaba akanki? Maganar su fitar dake daga dakinki kuka babu wanda ya isa yayi Abinda Allah beyi ba, kije gida ki huta ki bawa zuciyarki haquri idan kuma kinga bazaki iya karbar Al’amarin ba ki dawo zan tsaya miki”.

“Shikenan Nagode Baba Allah ya qara girma”
“Nima na gode Asma’u Allah yayi miki albarka keda zuri’arki gaba daya”. Haka mukayi sallama da Baba seda yasakani na share hawayena tas yace naje na dauraye fuskata a bayin da yake cikin palour sa kafin na fito.

Ina fitowa naci karo da Dada da yayanta sun fito daga dakinta, Yanda kasan anyi ruwan sama an dauke haka sukayi shiru gaba daya suka zubo mun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login