Showing 249001 words to 252000 words out of 260321 words
Chapter 84 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
kike maganar haqqi Asmy kefa kika koreni kikace karna sake zuwar miki gida, to tunda bani na siya miki ba kinga dole na kama mutunchi na ai ko”
“Yusuf dan girman Allah kayi haquri wallahi kuskuren harshe ne nayi a lokacin ba abinda nake nufi ba kenan” na fada ina fashewa da kuka, seda yayi qoqari gurin danne dariyar sa kafin yace
“Na haqura, dan Allah ki dena kuka ke se ana maganr wasa kawai ki ringa kuka ki dena mana”
“Toh ni ya kake so nayi? Na baka haquri kaceka haqura amma banga Alama ba. Wallahi dagaske Yusuf INA SONKA, I love you more than anything you could imagine in this world ya kake so nayi da zan tabbatar maka ina sonka?”
“Na yarda Asmy base kin rantse mun ba”
“To kazo” na fada kawai dan na rasa me kuma zan sake ce masa
“Ki tsammaci zuwana a koda yaushe Asmy tunda kin gayyace ni da kanki” ya fada cikin wani irin farin dana kasa tantance dalilinsa.
“Kullum roqona kike kawai nayi haquri baki taba buda baki da kanki kince nazo ba, daman na gaya miki, bazaki sake gani na ba sedai in har ke da kanki kika gayyato ni” ya sake fada.
“Yanzu daman tuntuni kawai abinda kake jira na fada kenan? Duk magiyar dana ringa maka ba abinda nake nufi ba kenan?” Na fada
“Baki fito kince Yusuf kazo ba, amma Yanzu da kika fada zaki ganni, kuma duk ranar dana zo ranar zaki tare ki tabbata Ango nake babu maganar daga qafa sena kwashe gara yanda....”
“Kai dai baka da kunya wallahi” nayi saurin katse shi jin yana neman ya saki layi kuma.
“Ai bazaki tabbatar da bani da kunya ba se rabda kika zo hannuna Asmy, kedai ki shirya mun ki kuma nemi Tissue dozen dozen saboda wannan kukan sangarta da shagwabar da kike yi ina tabbatar miki ranar zakiyi me dalili”.
“Seda safe, na fada ina rufe fuska ta da Pillow”
“Kiyi bacci cikin Amince Wife, I love you”
“Love you more” na fada tare da aika masa da Kiss me qara irin me tara tsigar jikin nan kafin nayi saurin yanke wayar.
Ina kallo ya sake kira amma naqi dagawa daga qarshe ya rubuto saqon yana cewa
“Kinci Bashi Asmy ki shirya biyan sa”
Dariya nayi bayan dana karanta nayi juyi ina sake ruqunqume pillow da yake jikina. Idan aka ce mun a rayuwata zan sake son wani Namiji bayan Bashir tabbas zance qaryane amma se gashi cikin dan taqin lokaci komai ya canza.
Wata irin sanyayyar soyaya ya ringa gwada mun da ban ankare ba seda na kai tsakiya ruwa yasha kaina kafin na fahimci na kusa nitsewa a cikin kogon sonsa. Zuwa yanzu nayi amanna da Yusuf shine cikon rayuwata, duk wani mafarki da burina na gudanarda rayuwar aure me cike da farin ciki da walwala ina hasko ta a tareda Yusuf fatana ya kasance har gidan auran mu, wannan qaunar dana ke gani a gurin sa ta zamo ta gaskiya har qarshen rayuwar mu dan na tabbatar idan har na samu akasin haka daga gurin Yusuf, a irin yanda ya rigada ya gama illata zuciyata tabbas bazan sake moruwa ba.
Washe gari ta kama Asabar babu aiki, tun sassafe nake aikin mulke mulken Dilka da kurkum da Anty ta hadamun nakeyinsa sau uku a sati, cikin abinda befi wata daya da farawata ba ni da kaina idan ina zuba ruwa a jikina bana so na dena saboda yanda fatata take wani sulbi da sheqi kamar jikin tarwada.
Inagamawa nayi wanka na zura doguwar riga harda safa na tafi gidan Anty na dubata bata da lafiya.
Allah me yanda yaso bayan tsahon shekaru da suka kwashe suna neman haihuwa se gashi Allah ya kawo musu dukka su su biyun a lokacin da basuyi tsammani ba daga ita har Abokiyar zamanta suka samu ciki bayan da suka gwada wani maganin sanyi da ANTY ZEE MAMAN MUJAHID take siyarwa.
Tabbas na yaba da kyan maganin ni kaina saboda daga sanda na fara shansa Al’adar da nayi ta farko nasha mamakin abubuwan daya wanko mun dan seda nayi zato ko har sannan akwai ragowar barin da nayi da be gama fita ba tunda ba’ayi mun wankin ciki ba seda na kirata take gaya mun babu komai datti ne kawai banyarda ba seda naje Asibiti suka sake tabbatar mun da mataccen jini ne ya fita babu wata matsala.
Tabbas magani yayi ina kuma ina shawartar duk wata me matsalar sanyi ko abinda ya shafi Al’ada ta gwada, masu matsalar haihuwa kuma ba’a barku a abaya ba, shi magani dace ne idan Allah ya amince se a samu.(Ga masu buqata suna iya tuntubar Anty Zee Maman Mujahid akan 08162859027 Allah yasa a dace).
Ina shiga ta fara dibana wai Amarya.
“Kinga yanda kike wani sheqi da walwali kuwa Ma’u, ki daga qafa haka dan Allah karki saka Bawan Allah ya zauce fa idan ya ganki” dariya na sheqe da ita bayan da na zauna ina cewa
“Kai Anty kin fiya zolaya wallahi, ya jikin na ganki ma da sauqi ba kamar jiya ba”.
“Kinsan abin seda haka se kanayi kana dan qara wa abun gishiri bakiga yanda Yallabai duk yabi ya kidime ba har tausayi yake dan bani wallahi amma gara ya gane ba’a samun Da da sauqi ai” ta fada tana murmushi
“Kai Anty kema fa kin iya mugunta, karna manta ina wannan dakan na gama da wadancan duka” na fada dan karna tuna abinda ya kaini.
“Kai Ma’u, kai Ma’u nidai babu ruwana wallahi karkije ki kashe musu Da ana zaune qalau tam”
“Anty gara ka kankaro mutunchi baka san ya matarsa take ba kinsan dai halin mazan nan namu” na fada ina duba wayata da naji saqo ya shigo,
“Ki duba whatsapp dinki na tura miki saqo” na gani daga Yusuf.
“Banga laifinki ba qanwata gara ka kankarowa kanka mutunchi wadannan mazan zamanin masu ido a tsakiyar kai. Jira nake kawai ku tsaida ranar tariya ai sannan ne zamu fara shiri na gaske, badai mace a gaban ki ba wallahi sedai su biyo baya” hannu ta bani muka tafa ina cewa “se Anty na”.
Whatsapp na shiga ina bude chat dinsa naga wata yar banzar sticker daya turomun ni kunya ma ya bani har seda na rufe ido na, Wani Pdf document na gani na bude, catalog ne na wani Kamfanin siyar da kayan daki na qasar Turkey sena danna masa Audio call ya katse ya turo mun da cewar na masa chat.
“Wannan fa na menene?” Nayi tagging document din.
“Ki duba ki zaba, Four bedroom duplex ne da falo biyu, ragowan abubuwan dole se kinje kinga gurin, ki tayani zabar Gadaje guda biyu nawa da Set din kujera, bana son Royal” ya maido mun da amsa. Sena bude kayan na fara dubawa.
Ajiye wayar nayi a gefe dan ban gane abinda yake nufi ba, siya mun zeyi ko kuwa yana gaya mun irin kayan da yake so a saka masa a gidan sa ne tunda naga yanzu saboda rashin kunya irin ta maza qiri qiri suke fadar irin gadon da suke so ko siya musu.
Na dan jima muna hira da Anty kafin nayi mata sallama na tafi bayan ta bani Dakan da naje karba da wata zuma data ce na ajiye amfaninta ba yanzu ba wai ita Scorpion. Ina fitowa daga gidan muka yi kicibus da Bashir ya fito daga gidansa, Kallo daya yayi mun yayi qasa da kansa harga Allah seda naji wani iri, murmushi na qirqiro harya gota ni nace masa
“Baban Ali barka da rana?”
“Barka dai Ma’u ya gida ya aiki?” Ya bani amsa kamar yana jira na gaishe shi. Se na amsa masa da lafiya kafin naci gaba da tafiyata a jikina ina jin yanda ya bini da kallo har na shige gida na kullo qofa, Allah kenan meyin yanda yaso a sanda yaso.
BASHIR
A cikin watanni ukun nan ya samu canji sosai a rayuwarsa dujda seda yayi da gakse gurin jinyar zuciyarsa kafin komai ya daidaitar masa sakamakon Addu’a da irin nasiha da a kullum Ahajinsu yake kan yi masa akan muhimmancin yarda da qaddara musamman irin tasa da shine silar komai.
Kusan duk wani abu na yaransa ya dawo hannunsa yanzu a gidan suke komai, tsakaninau da gidan Ma’u sedai suje suyi wasan su dare yana yi Aliyu ze hado kansu su dawo.
Zaman sa da Amirah dai ba dadi babu wuya akace lahirar kare, bayan zaman wata daya da ya barta tayi a Gombe ta dawo dole ya kafa mata sharuddan da in har tana son zaman lafiya dashi dole ta bi to anyi dace ta dauka musamman saboda a Gomben ma da sukaje kwananta daya a gidan Dada babanta ya samu labari yace ta tafi gidan su can tayi zaman jegon dan baze sake sakin wani abu daya shafi Yayan sa a hannun Fattu ba.
Zaman da tayi da matan Baban nata sam ba me dadi bane dukda ita ta quntata kanta dan a gurinsu su basu da wata matslaa sam. da fari ta farayi musu rashin kunyar da suka saba sanda Addah tana nan suka taka mata birki se duk tabi ta tsangwami kanta bata sakewa da kowa haka duka tayi zaman ba dadi gashi babu inda take zuwa babu kuma me zuwa gurinta, Anty Binta Amaryar Alhajinsu ce ta dauki ragamar gyarata dayi mata wanka har na wata dayan kafin babu Arziqi ta tattara ta koma Lagos bayan dogayen sharuddan da Bashir ya gindaya mata akan zamansu dan ko Addah da take gidan Anty Talatu ana ta dibar tsiya bata san da komawarta ba se bayan ta tafi dan duk a shirinta tare zasu koma ai kuwa tasha zagi ta kuma tabbatar mata tana tafe dan ma yanzu tana shirye shiryen yin auran kisan wuta ne kamar yanda wani sabon Malami da Tatu ta kaita wajen sa ya gaya mata tayi kafin a gama aikin da zaa karkato da hankalin Alhaji Murtala kanta ta koma dakinta.
Tasha matuqar wahala sosai da irin sabon salon zaman nasu dan yanzu duk wani abu da cikakkiyar matar aure zatayi a gidan ta shi takeyi, girki sau ukun nan seta dora kuma ba irin na ganin dama da takeyi a da ba, shiyake gaya mata abinda yake so ayi ko yaran daya fuskanci bata iya wasu abubuwan bama makarantar koyon girki ya kaita, gyaran gida kuwa haka take wuni ta dauke wannan ta gyara wannan a haka ma dan yaran sam ba masu bata guri bane.
Badan ma ta kasa sakin zuciyarta ta jasu a jiki ba da ko su sun isa su ringa taya ta aikin gidan idan suna nan tunda duk abinda suka saba yiwa uwar su ne. Sauqin ta daya Bashir ya rage wannan fada da hargagin da yake mata da tayi kuskure ada, dukda yanzu shiru shirun sa ya dada qaruwa ne ko da yaushe ya zauna shi kadai zaka lura yayi zurfi a cikin tunanin amma ko laifi tayi masa cikin lumana yake fahimtar da ita kuma babu laifi a yanzu yana kyautata mata daidai da yanda itama take kyautata masa shida Yaran data fuskanci yanzu sune komai nasa dan yawan ci idan suka samu sabani to akan abinda ya shafi yara ne.
ASMA’U
Sati daya tsakani Yusuf ya gaya sanar mun a ko wanne lokaci yana iya dawowa sannan kafin lokacin yana so aje a duba gida dukda har sannan ban rigada na zabi kayan dayace shi ze siya ba, ina jira zanje Gombe na zauna da yan uwana naji shawararsu akan na barshi ya siya din ko mu zamu siya da kanmu.
Daya matsamun akan zancen aje a ga gida Anty Ladi na kira na gaya mata suka hadu ita da Junaidiyya da Anty Nasiban Yaya Abubakar se Zahra suka je ganin gidan. Na Bauchi kuma daga Gombe su Yah Fati suka tafi suka hade da Hajia Alawa qirjin biki suka gano gidan.
Wayyo Allah ranar kam nasha surutu harna gode Allah na santin gidan da suka ringayi ga Videos da suka dauko suka ringa turawa dangi.
A bakin su Anty Ladi nake jin gida daya zamu zauna tareda matarsa a Abujan dan na Bauchi kowa da gidanta na sani amma a Abujan bangaren kowacce daban dan a cewarsu ma tazarar dake tsakani ta isa a gina wani gidan a gurin filin wasanni ne ne da Garden harda swimming pool yayi a tsakiya se a bangaren ko wacce mace yanada dakuna biyu da palour banda wani qaramin flat da yayi a farkon gidan inda ze ringa sauke Jama’ar su yan siyasa se kuma Boys quarters a bayan gida.
Wannna zuwa ganin gida da akayi ya taso da guguwar zancen tariya kuma dan daman sunce duk ido kawai suka saka mun, yanda kasan auran budurwa haka yan uwana suka hau shirye shirye, Yusuf ya kafe akan zuba mun kaya a gidansa na Abuja kamar yanda ya rigada ya sakawa Intee haka kuwa akayi, kamfani sukaje suka tsara yan uwana kuma suka shirya mun na Baushi dan kwandala ta bata shiga ciki ba gudummawarsu suka hada data abokanan arziqi suka mun kaya na yar gata har kuka seda nayi da naga Video gidan bansan da me zan saka musu da irin qaunar da suke nuna mun ba sedai Muyi Addu’ar Allah yaci gaba da hada kanmu har mutuwa.
Dagaske dai Yusuf yaqi dawowa Nigeria har aka tsayar da ranar tariyata sati biyu masu zuwa ya kuma qi bari muyi magana balle na tuntube shi naji makomar aiki na ko kuwa dai an zuba kaya ne kawai a Bauchi da Abuja saboda idan zuwa ya kama mu.
Ranar Juma’ar daya rage saura sati daya tariyata kuma a ranar nake son daukar hutu tunda zamu tafi Gombe gaba daya zuwa Lititin dan yara sunyi hutun Aliyu ne kawai zamu bari saboda ze rubuta Jamb.
Bayan dana karbi takardar hutuna da suka bani har wata uku aka sake qaramun da wata da ban san kota mecece ba. Da wuri nayi sallama da abokanan aikina na kama hanyar gida dan ina so na tsaya na bada wasu kaya a Tasha da za’ayi mun gaba dasu.
Se yamma na shiga gida, ina cin abinci muna waya da Yusuf, ni yanzu na haqura da tambayar sa yaushe ze dawo ma tunda abin nasa ya zama wulaqanci, zancen hutun da aka bani daya mun dazu yasa takardar da aka bani ta fado mun a rai. Farida nacewa ta dakko mun su a cikin jakata, ina budewa na zaro ido ganin takarar transfer ce zuwa Headquarter mu ta Lagos harda qarin girma.
“Yusuf kai ne ko?” Na fada kamar zanyi kuka.
“Oh ni dai naga takaina me kuma nayi Asmy duk wani laifi ace nine, nine me?” Ya fada
“Transfer akayi mun zuwa Abuja nasan wallahi kaine bayan ba haka mukayi da kai ba kai kace zaka barni na zauna a Lagos”
“Ni babu ruwana su sukace miki da saka hannuna a ciki? Qila sun duba miki ne inda mijinki yake amma ni babu ruwana a ciki” ya fada yana yar dariya.
Duk se naji raina ya baci, yanzu kenan dagaske zan bar yarana na tafi wata rayuwa daban ba tare da su ba? Me yasa tun farko yayi mun qarya yace ze barni na zauna tare dasu
“Kinyi shiru Asmy, dagaske nake miki bani na saka ba amma idan kina so se na je na nemi alfarma idan ze yuwu su barki a inda kike, amma bakya ganin hakan da sukayi kamar yafi hankali na ze rabu da yawa ni Ina Abuja Intee tana US ke kina Lagos bani da hutu kullum ku tausaya mun mana” ya fada kamar zeyi kuka.
“Uhm, shikenan bari naci abinci mayi magana” na fada na kashe wayar.
Goggo na kira, tana dagawa na saka mata kuka ina cewa
“Goggo kin gani ya saka anyi mun Transfer zuwa Abuja bayan shi yamun alqawarin ze barni a Lagos yanzu kuma yazo ya canza gaskiya ni bazan yarda ba ku kirashi kuyi masa magana”.
“Wallahi Wallahi Wallahi sau uku kenan Asma’u kika sake kirana akan wannan shirme da rashin hankalin naki sena ci ubanki. Ke se an fara miki zaton kinyi hankali se ki sake kwanto wani sabon diban Albarkar naki ko? Da dab ubanki idan yace ki zauna se ki zauna ke? Me zakiyi ashe baki cire Bashir daga ranki ba? To Shikenan ki ci gaba dayi keda Allah kiyiwa kanki sanadin da zaki mutu a banza ki tafi wuta da auran wani akan ki zuciyarki tana ga wani shashasha da be san darajar ki ba wawiya kawai” Goggo ta fada cikin bacin rai
“Ni ba haka nake nufi ba ni babu ruwana da wani Bashir kawai saboda yarana nake so na zauna a nan kum....”
“Se kinci kutumar ubaki dake da yaran Asma’u idan baki rufe mun baki ba, ai daman na fadawa Qarami wannan lambon da kikayi mu saka ido na tabbatar indai Ke din dana sani ce sekin nuna halinki, to bari kiji ni na kira Yusuf din na gaya masa yasa ki bar aikin gana daya ma amma yace Aa za dai ayi miki canjin guri dukda kun rigada kunyi yarjejeniyar zaki zauna a inda kike.
Naga alamar so kike ki mayar dashi kamar dan da kika haifa se yanda kika ce za’ayi ko to ni bazan saka ido ina kallonki kina iskancin da kika ga dama ba, ko ki tattara kibi mijinki ko ki bar aikin gaba daya kuma na rantse da Allah babu dan da zaki dauka ki riqe, ita kanta Faridar dana ce an fasa ki hadasu da Amnah zasu koma gurin qarami dan ubanki ki je kiyi zaman aure Idan kinga dama kiyi abinda ba haka ba zan tabbatar miki da shirun da nake yi bawai dan ban iya bane ko kuma kunfi qarfina nima na iya maganin ko wanne dan Banza” Goggo ta fada cikin matuqar fada da hargagin da ban taba jinta tana yi ba.
Bata barni ma na sake magana ba ta kashe wayarta, wannan abun ya sake dugunzuma mun hankali, wayar Yusuf na sake kira yana dagawa na fara magana cikin kuka ina cewa
“Yusuf me yasa munyi Alqawari zaka saba sannan kaje ka hadani da mahaifiyata tun farko ai bani na roqa ba kai da kanka kace zaka barni na zauna kusa da yarana se