Showing 75001 words to 78000 words out of 260321 words

Chapter 26 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42685

Abbi bane kin san su Anty Amirah har gidan bokaye suna zuwa qilan Asiri sukayi masa" ta fada muryarta na rawa alamar kuka zatayi.

Sena juyo na kalleta ina murmushi nace

"Kinsan menene Amna?" Seta girgiza kai alamar Aa, numfashi naja kafin naci gaba da cewa

"Abbin ku be kyauta mun ba, inda ya fadamun ba yau ze dawo ba kinga da ban sha wahalar hada masa abinci ba. Kina kallo fa jiya ko baccin kirki banyi ba ina gasa masa zabo amma duk wannan wahalar ta tashi a banza kuma fa da magriba ma fa seda mukayi waya yace sun dawo yanzu ze taho gida".
Na qarasa ina share hawayen daya zubo ta gefen ido na, gaya matan da nayi se yasa naji wani sanyi sanyi a zuciyata.

"Haka ne Mami, nidai kiyi haquri ki dena damuwa daman abinda suke so kenan"

"Na haqura Amna, kije ki kwanta ki huta toh nima idan na karya bacci zanyi" na fada ina miqewa na bude wardrobe na dakko Doguwar rigar Yadi me laushi na saka. Tura abincin kawai na ringayi dan bakina sam babu dadi. Bayan na gama na sha Paracetamol na kwanta.

Dakyar ya yakice tunanin abinda Bashir yayi mun na samu bacci me nauyi ya dauke ni, gana jiya da banyi ba ga bashin na shekaran jiya.

BASHIR

Tun washe garin da ya sauka a Delta da daddare suna waya da Amirah tana ci gaba da yi masa kukan data ara ta dorawa kanta.

Cikin kukan take cewa "Kowa ya kira ni yayi mun gaisuwa dangi na kusa da na nesa amma banda Anty, ai ko ba komai tsakanina da ita ya kamata ace tayi mun gaisuwa ko su Aliyu ma ai duk ya kamata su kirani ko banza qanwarsu ce" .

"Ma'u bata kira ki ba?" Ya tambayeta da mamaki,

"Bata kirani ba mana inda ta kira ai Zan gaya maka  indai kuma ba murna take da mutuwar Iman ba". Amiran ta bashi amsa. Wannan fushin cewa bata kira Amirah ta mata gaisuwa ba shi ya hana shi kiranta har tsahon kwanakin da yayin.

Ko ranar data kirashi da Amiran suke waya, sanda kiran ya shiga harga Allah yaso ya daga dan yayi missing dinta amma daya gayawa Amirah nan da nan ta rikice ta fara masa kuka, basu kuma gama wayar ba se gurin sha biyu dan haka suna gamawa bacci ya kwashe shi.

Gaba daya yanzu shi tausayin Amirah yake ji. Koshi me Ÿaÿa Shida rasuwar yarinyar nan ta tabashi sosai bare ita me guda daya sannan ga irin wahalar da tasha shiyasa yake biye mata ko zata samu sassaucin abinda take ji.

Rabar laraban kuma da zumudin son ganin Asma'u ya taho, yasan be kyauta mata ba ya kuma bari ne se ya dawo sannan ya goge laifinsa, sanda ya kirata dagaske yana Lagos saukar su kenan amma suna ajiye waya Amirah ta kirashi tana kuka tamkar ranta ze fita.
Akan gashi har anyi sati da rasuwar Iman amma beje ya ganta ba.

"Ni daman nasan baka sona Yaya, baka qaunata farin cikin Anty da Ÿaÿan ta ne kawai matsalar ka baka damu da ni na rayu ko na mutu ba. Karinga tunawa nima matarka ce kamar ita, kuma ina da haqqi akan ka. kuma idan har ban yafe ba kasan Allah babu ruwan sa seya kama ka da haqqina". Tana gama fadar haka ta kashe wayar ta, bugun duniya kuma taqi dagawa.

Gaba daya ji yayi hankalinsa ya tashi, shifa duk abinda za'ayi kar a saka batun Allah ya isa. Ya fito kenan ze taho gida suka hadu da daya daga cikin Directors dinsu shima dan Gombe ne suka gaisa se yake gaya masa Gombe ze tafi yanzu.

"Sir Daman akwai jirgi yau ko a mota zaka tafi" Bashir din ya tambaye shi, se yayi murmushi yace
"Haba Engineer mota kuma a daren nan ai kayi mun fada, a jirgine His excellency yazo wani taro, kasan Abokina ne, toh na samu alfarma za'a rabani Private Jet mu tafi.

"Ai Sir ku manayan mutane ne da zan samu a rabani nima ai dana biku na dana" ya fada yana shafa kai, se Director yace "dagaske kake ko wasa se na kira Protocol naji idan ze samu".

Beyi zaton za'a samu din ba kawai ya amsa, yana kiran protocol din kuwa yace su taho yanzu su akw jira. Babu damar yayi wa Director wasa da hankali dole ya bishi suka tafi dukda shi kansa yasan be aikata daidai ba, amma yasan Asma'u tana da Fahimta, gara ya fara gyarota da Amirah sannan ya dawo kan Ma'un sa dan yasan ita bazata taba yi masa Allah ya isa ba kome zeyi mata.

A Flight mode ya saka wayarsa dan karma ta kirashi besan me zece mata ba, seda ya sauka a Gombe, yana kan hanyar zuwa gidan su ya tura mata da wannan Text din.

Sanda ya isa har sun rufe gida seda ya kira Naziru ya bude masa tukkana. Da mamaki Nazirun yake kallonsa, ya karbar masa Jakar suka shiga ciki kai tsaye ya wuce dakinsu da Jakar shi kuma Bashir ya wuce Dakin Dada dan burinsa yanzu yaga Amirah yaga halin da take ciki.

Palour babu kowa dan har sun kashe fitulu alamar sun kwanta, kai tsaye dakin Fainusa ya nufa inda yasba ze samu Amiran. Har ze tura qofar ya daka saboda tuna ba ita kadai bace a dakin baisan a yana yin da ze tarar dasu ba seya dakata.

A hankali yayi knocking, seda ya buga sau uku sannan Fainusa ta taso ta bude qofar tana hamma a zaton ta ma Dada ce, seta yi saurin saita kanta ta shiga gaishe shi, a ranta tana mamakin daga ina da tsohon daren nan kuma.

Fita tayi daga dakin ta koma palour shi kuma ya shiga. Abin mamaki matar da Tace bata iya bacci da ta kwanta mafarkin Iman takeyi se gata tana shaqar baccinta kashirban se a iya sace ta ma bata sani ba.

Tashinta ya shiga yi amma ko motsi se wasu surutaj banza data ringa masa qarshe ya haqura ya koma dakin Naziru ya kwanta dan already Nazirun ya gyara masa Gadon sa shi kuma ya koma Dakin Sa'ad ya kwanta.

Juyi ya ringa yi kawai ya kasa baccin, tunanin halin da Ma'u take ciki kawai yake. "Allah sarki Ma'una yar Aljanna nasan ke me haquri kuma zaki fahimce ni" ya fada a fili kamar yana gabanta. Dakyar ya samu yayi bacci ya qudurce a ransa dai In sha Allah gobe ko a mota ne seya tafi Lagos.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 27
Amirah
Da Asuba duk tashin da Fainusa ta ringa yiwa Amirah tayi sallah ko motsi batayi ba. Ba wai dan bata jin ta ba, A’a kawai ita ta tsani wannan tashin Asubar da sukeyi tun kafin ayi assalatu.

Tana lafe akan gado ta jiyo Fainusa tana gayawa Dada zuwan Bashir din jiya da daddare, seta miqe zaune. “Kardai ya shigo ya ganni ina sharar bacci” ta fada tana zaro ido.

“Wayyo ya zanyi yanzu” ta sake fada a fili tana tunanin mafita. Tunda akayi rasuwar take masa qaryar bata iya bacci da daddare shi yasa kullum suke raba dare suna waya se yayi dagaske take barinsa ta kwanta.

Jiyan ma abinda yasa bata kirashi ba baccin taji da wuri, seta shirya a ranta da safe in sunyi waya se tace masa ai tasan ya koma gida ne bata so ta kirashi Anty taji haushi toh yanzu gashi qilan ya ganta wai ya ma akayi be gaya mata ze zo a jiyan ba. Yanzu ita wace qaryar zata zabga masa?

Ganin ba mafita ya sakata tashi da niyyar ta yiwo alwala idonta ya sauka akan Maganin tari akan Mudubi. Nan take ta tuno ranar sadakar uku aka siyowa Yaron Anty Amina Babbar Yayar su Bashir da take aure a Bauchi, se akayi rashin sa’a aka karbo na manya dan haka bata bashi ba ta ajiye a dakin.

Da sauri ta dauke shi, seda ta leqa ta jikin qofa ta hango Dada da Fainusa suna Nafila kafin ta bude kofar Toilet a hankali ta shiga ta tuttar da fin rabin maganin a rariya kafin ta koma ta kwanta bayan ta ajiye shi saitin kanta ta bar kwalbar a bude.

Har qarfe shida tana kwance a gurin, Fainusa data gama Azkar dinta ta shiga dakin yin wanka dan zata fita gurin aiki tana koyarwa a makarantar secondary dake kusa dasu ta tarar da Amirah a bararraje tana bacci babu Alamar ta tashi tayi sallah.

“Lallai yarinyar nan, daman baki tashi bama kikayi sallar nidai naga randa zakiyi hankali” ta fada bayan da ta danawa Amirah duka a cinya ta bude ido da sauri dan dukan ya shigeta.

“Akan me zaki zo ki dakeni, Allah ya isana wallahi” ta fada tana sosa inda ta dake tan.

“Ni kike yiwa Allah ya isa mara kunyar banza kawai” Fainusa ta hayayyaqo mata, Dada da tajiyo hayaniyar tasu ta shiga da sauri tana cewa

“Bismillahi safiyar taku tayi zaku fara ba, kamar masu ganin hanjin juna yanzu kuma me akayi?”

“Dada wai fa wannan mara kunyar tunda na tashe ta da Asuba ashe bata tashi tayi sallar ba, shine yanzu fa dana shigo na sake tashinta ta fara zagina tana mun Allah ya isa”.

Bude baki Amirah tayi da niyyar magana ta hango Bashir ya turo qofa, se kawai ta fashe da kukan qarya harda sheshsheqa tana cewa

“Wallahi Dada ba haka akayi ba, ni ban ji sanda ta tashi ni ba ban ma san safiya tayi ba kawai yanzu tana shigowa ta hau dana mun duka wai na kwanta ina bacci kamar wata kafura bayan tasan ko baccin bana iyayi, kuma ni maganin mura nasha shine bacci me nauyi ya kwashe ni” ta fara qoqarin miqewa, tana sane ta ture kwalbar maganin dan sauran na ciki ya zube ita kuma ta koma dabas ta zauna a dole jiri take gani.

Sake yunqurawa tayi ta miqe se ta tafi kamar zata kife Bashir yai saurin tarota yana cewa “yi a hankali mana” nan idonsa ya saka akan kwalbar maganin, seda ya zaunar da ita kafin ya daga kwalbar yana kallonta yace “Amirah kina hauka ne, syrup kika sha saboda kin kasa bacci?”

Kuka haiqan ta saka masa tana cewa “to ni yaya ake so nayi? Bana iya bacci ni kadai nasan damuwar da nake ciki babu wanda ya damu da ni har kai din ai baka zo ba bate kasan halin da nake ciki”.

Seda ya yi qoqari ya hadiye bacin ransa, kafin ya sassauta murya yana cewa “shikenan, yanzu ki daure kiyo alwala kiyi sallah, lokaci yana qara ja” ya juya ya fita jin ana kiran wayar sa.

Seta miqe tabi bango, dab da zata shiga bayin ta waiga tareda ballawa Fainusa harara ganin babu wanda yake kallonta ta shige ciki.

Daga Dada ko har Fainu bude baki sukayi suna kallon wannan Drama, ita Dada mamakin yanda zata ce bata bacci kuma kowa babu me kula da ita, to wanne baccin ne batayi yarinyar da duk dare seta leqo su kuma ta ganta tana baccin ta qalau kai har na rana yi take, gaba daya fa jimamin na kwana biyu tayi ta ware se idan taga idon mutane ne zata wani koma kalar tausayi duk fa tana ankare da ita.

Ita kuwa Fainu Murmushin takaici tayi ta nemi gefen gado ta zauna tana cewa “Allah ya kyauta” lallai Amirah ba qaramar makira bace, kullum tana jin yanda take kalallame shi a waya tana raina masa hankali to Yayan shima ba kirki ne dashi ba bare ka gaya masa gaskiya amma dai jiki magayi.

Sanda ta fito Fainusa kawai ta tarar a dakin, bata so ba dan har wani kwararrabe fuska tayi a zatonta Bashir yana nan ganin Fainusan yasa ta saki tsaki ta dauki Hijabinta tana cewa “aikin banza mutum bashi da aiki se sa ido”.

“Wai Amirah ni sa’ar kice? Ni kike gayawa wannan dan uwarki” Fainusa ta fada tana miqewa tsaye

“Karki sake zagar mun uwa nidai” Amirah ta fada tana murguda baki,

“Idan na zaga me zakiyi?” Cewar Fainusa tana qara matso Amiran,

“Nidai karki sake zagina dai tam” Amiran ta fada kafin ta juya ta tada sallah, idan badan tsoron kar ko Bashir yana kusa ba da ramawa zatayi ai uwa bata fi uwa ba.

Kwafa Fainusa tayi, taso ta fadi wani abun da be mata ba wallahi seta tsinkawa shegiya mari idan yaso duk abinda Yayan ze yi yayi. Ai daman saboda taga tana auranshi ne yasa ta raina uban kowa ko amma zatayi maganin ta wallahi.

“Haka kawai dan mutum yana baqin cikin ana auran dan uwansa baze iya dauke kai yaga ana abin arziqi ba shine ze takurawa mutane, idan anji haushi mutum ya koma gidan mijinsa mana” Amirah ta fada daidai sanda Fainusa ta fito daga wanka.

“Idan gidan uban ki nake zaune se kice an takura miki, sannan aure da kike magana kibi a sannu qaddarar zawarci bata wuce kan uban kowa ba” tana fadar haka ta qarasa gaban mirrow ta hau shiryawa, amma tabbas yau se yar iskar yarinyar nan ta bar mata daki.

Ita Amirah zatayiwa gorin zawarci yarinyar da a shekaru ta girme mata da har shekara shida shine zata tsaya tana gaya mata wadannan maganganun dan kawai taqamarta tana auran yayanta? Tabbas dole tayi maganinta wallahi.

Ita kuwa Amirah sum sum ta fice daga dakin ganin yanda fuskar Fainusan ta chanza tasan tsaf zata iya rufeta a daki ta nada mata mugun duka. Tayi tunanin zata taradda Bashir a Palour seta ga babu kowa, zama ta tayi tana jiyo motsin Dada a Kitchen din amma hankalin ta be bata ya kamata ta shiga ta taya ta aiki ba.

Bayan Bashir ya gama amsa wayar, harya danno Number Asma’u ze kira se ya dakata. Wani nauyinta yake ji besan me ze ce mata ba idan ya kira. Seya karkata kiran zuwa Number Aliyu amma a kashe.

Dadi ma yaji da ya sameta a kashe dan qilan ya zama yana tare da Ma’un hakan kuma ze zama qari akan laifinsa.

Dakin Alhajinsu ya shiga ya same shi a zaune kan sallaya yana lazumi. Bayan sun gaisa da mamaki Baban yake tambayarsa yaushe yazo.

Seya shiga shafa qeya yana cewa “jiya da dare Baba, Engineer Sha’aban na biyo zasu taho tareda His excellency bayan mun dawo daga Delta.

“Kace ko gida ma baka je ba kayi yo nan” Baban Ya fada yana kallon fuskarsa, rasa abin cewa Bashir yayi dan haka yayi shiru kawai.

“Ka kyauta, tashi kaje” Baban ya fada ya maida hankali ya ci gaba da jan carbinsa.

Yana fitowa ya tare Naziru da ya fito daga Palour Dada da Kofin shayi a hannunsa.

“Ji mana” ya dakatar da Nazirun kafin ya fara masa magana wayar sa tayi qara. Team leader sune yake gaya masa ranar Monday suna da presentation, dan haka yau idan sun huta gobe Friday zasu hadu a office dan su tattara reports din hannun kowa” bayan sun yi sallama Bashir ya kalli Naziru yace

“Kayi mun booking morning flight gobe”.

“Ai Yaya babu jirgi fa, an samu yar matsala sun dakatar da jirgin Gombe zuwa lagos till further notice. Sedai ka hau mota kaje Kano tukunna ka tafi ta can”.

Kallon sa Bashir yayi kamar me son ganin gaskiyar maganar a fuskar sa, da hannu yayi masa alama da ya tafi, kafin ya lalubo Number Wani Agent da yake siya masa ticket ya kira.
Irin bayanin da Nazirun yayi masa dai ya maimaita se ma qari daya masa akan Yau jirgin qarfe bakwai da rabi ne se na sha biyun rana, gobe kuma babu jirgin Safe se Shidan yamma.

Godiya ya masa ya kashe wayar kafin ya shiga lissafin yanda zeyi, qarfe 10 na safe ake buqatarsa a office goben, dama babu zancen yau dan jirgin safe ya tafi yanzu kuwa qarfe takwas na safe ta gota, indai ba fiffike zeyi ba baya tunanin akwai ta yanda ze isa Kano kafin sha biyu na rana. Goben da yayi tunanin samu ance sena Magriba shida yake da Meeting qarfe goman safe to yanzu yaya zeyi??

Wai wane tsautsin ma ya saka shi tahowa yanzu gashi ya saka kansa a cakwakiya da hargitsin da yake jiransa a can gida, Mafita daya ce kawai Ya tafi a Mota in sha Allahu dai daga nan zuwa cikin dare ai ya isa. Da wannan shawara yayi Na’am dan haka ya juya ya shiga palour Dada.

Amirah na kwance akan kujera ya shiga seta miqe ta zauna tana gaishe shi, kujerar dake kallonta ya zauna ya amsa dai dai sanda Dada ta fito daga Kitchen din ta try a hannunta. Fainusa ta kwalawa kira ta fito cikin shirin fita, Try din ta bata tace ta kaiwa Alhajin su sannan ta kalli Bashir tace

“Yanzu zaka karya ne ko se an jima?”
“Eh yanzu Dada, dana gama zan kama hanya ne ma”.

Daga ita har Amirah kallonsa sukayi,
“Da wuri haka?” Dadan ta tambayeshi, se ya miqe yana cewa “Wallahi Emergency ne ya taso mun a office, kinsan jiya muka dawo toh kuma ana buqatar wasu bayanai gobe gashi na taho dasu nan kuma babu jirgi dole mota zan bi”.

“Tab amma kaima da ganganci kake, me yasa ka taho kasan kana da ayyuka a gabanka. Yanzu a yanda hanya take zaka bi mota har Lagos, to kana da tabbacin ma zaka isa kafin goben nan ina se dare motocin suke tafiya koh?” Dada ta fada tana riqe baki.

“Addu’a za’a mana Dada In sha Allah zamu je lafiya, yanzu dana shirya zanje Tashar, Idan babu masu tafiya yanzu inaga Zan dauki Shatar mota ne kawai na tafi dan kinsan su office babu ruwan su dole na kai musu takaddun nan gobe qarfe goma”

“Toh Allah ya rufa asiri, se kije ki hada masa abin karyawar ki kai masa tunda sauri yake” Dadan ta fada tana kallon Amirah data daskare a gurin. Dakyar ta yunqura ta tashi, lallai ma. Daga zuwansa jiya da daddare zece yau ze juya, wallahi qarya yake ta tabbata babu wani kiran office kawai Matarsa ce tace ya dawo shine ze fake da wani aiki ai kuwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login