Showing 144001 words to 147000 words out of 260321 words

Chapter 49 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42717

tayi wanka tace seda safe, dataga yana neman bata mata farin cikin data samu dole tayi wankan suka koma sukayi bacci.

Washe gari ma lafiya qalau suka tashi, ta cije ta daure tayi duk abinda ya kamata akayi sa’a kuwa harta hada masa abin karyawa suka zauna beyi qorafi ba. Seda ya gama suna zaune a palour yake cewa

“Yaran nan kinji shiru har yanzu babu wanda ya shigo ko basu tashi bane”.

“Eh qilan kasan jiya an sha ruwa gari yayi sanyi may be shi yasa basu fito da wuri ba” ta fada a fili a ranta kuwa zagi take auna musu tana Addu’ar Allah yasa kar su zo.

“Bari naje na karbo katin wuta shaf na manta jiya dana fita ban siya ba naji kuma mitar tana qara” ya fada yana miqewa, seda ya sako jallabiyya ya dauki muqullin motarsa kafin ya fita, yana fita itama ta miqe akan kujera ta kwanta ranta fes a qarshe dai ta samu irin rayuwar da take so ita da Yayanta a gidan su su kadai suna zuba soyayya.

BASHIR
Yana fita qofar gida ya ga yaran suna Ball, gaba daya suka gaishe shi banda Aliyu da tunda suka hada ido ya juya baya yana hada fuska se kawai Bashir din ya girgiza kai tareda yin qwafa ya kama hannun Abdallah yana cewa

“Kun tashi daman me yasa baku shgo gida ba toh?”

“Abbi Mami ta hana tace idan muka sake zuwa gidan seta cire mana kunne ko Yah Abdallah” Ahmad yayi zuruf ya fada dan daman duk cikinsu shine me dan banzan surutu ai kuwa Aliyu ya kai masa duka yana cewa
“Waya tambayeka me shegen surutun tsiya kawai”.

“Idan ka sake dukan sa Aliyu sena saba maka, ita Ma’un ce tace kar ku sake shiga gidan yayi kyau zan nuna mata kuwa na fita iko a kanku” Bashir ya fada kafin fuu ya juya ya koma cikin gidansa.

Amirah da har bacci ya fara daukanta bude qofar sa ya farkar da ita se ta miqe tana goge ido tace
“Wai har ka dawo? daga dan kwanciya ashe bacci ne yayi gaba dani ban sani ba”.

“Wai me Ma’u ta dauki kanta ne har ni zata ce Yarana karsu sake shigowa gidan nan saboda taga na saka mata ido na barta dasu ko? To shikenan ai kuwa a yau zasu bar wajenta idan yaso se naga wanda zata sakw hanawa zuwa wani gurin, ki fitar da kwalayen da kika zuba a can dakin yanzu zan fita za’a kawo sababbin gadaje a saka musu tunda ta kwashe wadancan, Amna da Farida kuma se su zauna a dakin ki kafin zuwa na samu wasu kudin suma a gyara musu dakin su” ya fada a mugun fusace ya wuce dakinsa dakko Atm dan ya manta ma dazun daze fita be dauka ba.

Har yakai bakin qofar Amirah data miqe tsaye tace “cabdi wadanne yaran ne zasu dawo gidan nan ni nace maka zan riqe maka yaya ne ko yaya? Harda ma wasu in basu dakina su zauna wallahi baze yuwu ba babu dan wanda zan riqe ehe”.

“Idan sunzo seki kore su kinji ko tunda baki da hankali ni zan koya miki har in fadi magana ki tsaya a gabana kina cewa ba za’ayi ba to ki jira na fito na tarar da ke anan gurin wawiya kawai” ya shige dakin ransa idan yayi dubu ya baci.

Me matan nan suka dauke shi ma? Ita waccen ta hana masa Yara zuwa gidan sa ita kuma wannan tana cewa baza su zauna a gidan ba, to ze gani idan gidan ubanta ne seta hana su ita kuma Ma’u ze kwace yaransa yaga in akwai abinda zata iya yi akai.

Sanda Ya fito Amirah ta shige dakinta dan haka yaja qwafa ya fita, yaso ya tarar da ita wallahi da se jikinta ya gaya mata tunda yaga alamar ita se an taba lafiyarta sannan take nutsuwa idan banda ma rashin kunya shi a matsayinsa Amirah zata kalla ya fadi abu tace bazatayi ba? Illar auran qaramar yarinyar kenan yarinyar da aka haifa akan idonsa ya raineta a gidansa da auran wuri ma yayi yasan tsaf se haifi kamarta amma yanzu tunda taga makwancinsa shiyasa take iya tsayawa a gabansa tana masa fitsara zeyi maganinta kuwa.

Amirah kuwa Dakin ta ta shiga, a fusace ta danna kiran Addah tana daga wayar kuwa ta saka mata kuka tana gaya mata yanda akayi.

“Kayyasan nan to ke me kika ce masa yanzu” Addah ta bada daga daya bangaren,

“Me zance masa kuwa Addah na gaya masa wallahi babu dan da zan riqe shine wai idan gidan uban wani ne se na hanasu zama ya gani”.

“Kina jina ko, lalabashi kuje a hakan zuwa musan abinyi dan ba mutunchi ne dashi ba kar muje ya sako mun ke kamar yanda ya saki uwarsu. Suzo din kisan mummuqe zaki musu a gabansa ki nuna kina son su a bayan idonsa kici ubansu yanda da kansu zasu gudu kinga qarshe se kefin ya koma kan uwarsu yace ita ce ta kitsa musu mugun abu” haka Addah tayi ta lallaba ta dakyar ta sauka ta yarda zata bashi haquri idan ya dawo ta kuma karbi yaran idan yaso a hankali ta gasa musu aya a hannu yanda zasu gudu da qafarsu su bar mata gidan.

Kafin ya dawo kuwa an kawo gado, haka ta danne baqin cikinta ta tsaya suka saka kayan harda wallpaper aka chanza musu masu suka gama suka tafi ta dawo palour ta zauna tana jiran taga shigowarsa da yaran tana nan zaune kuwa se gasu daya bayan daya suna shigowa kowa fuska jiqe da hawaye.

Muryar Bashir da tajiyo daga waje alamar shima yana dab da shigowa ya saka ta tashi ta taro Yan biyu tana cewa

“Meyasa kuke kuka da nan da gidan Mami ai duk daya ne kuje fa kuga yanda aka gyara muku dakin ku yayi kyau sosai”.

“Karki sakw tabasu kuma babu ruwanki damu a gidan nan kiyi harkar ki muyi tamu in ba haka ba kuma zaki sani” Aliyu ya fada yana fizge su daga hannunta kafin ya wuce dasu dakinsu yana sake balla mata harara Amirah kuwa da kallo ta bisu kawai baki bude, badan Bashir na waje babu abinda ze hana taci uwar yaron nan yau amma ai suna hade, Bashir din zeyi nisane wallahi seta koya masa hankali.

Kowa tayi ta zauna sega Bashir kaman wanda aka wullo, kallo daya yayi mata, yaso ace ta ci gaba da tata fitsarar ya ida saita mata nata hankalin tunda ya gama da Ma’u amma sabanin haka se yaga ta miqe tana murmushi tace

“Yara sun shigo suna kuka, ina ta lallashin su ma suka wuceni suka shige daki. Kaje ka lallabasu dan Allah badadi yaro ya ringa kuka”.

Wuce ta yayi ya shiga dakin nasu, suna nan har sannan sun hada kai suna kuka musamman Faridah da take ita kadai yau Babu Yah Amnah, Aliyu dai yana tsaye yana huci dan a fusace ya waiwaya da aka bude qofar ya zata Amirah ce ganin Bashir se ya mayar da kai gefe yana ci gaba da lissafi a ransa.

Bashir kuwa tsayawa yayi, seda ya irgasu kamar wasu yayan kaji kafin ya sake fita fuu kamar iska ya tafi gidan Ma’u, yayi Sa’a qofar a bude take dan tunda suka fita tana zaune tana kuka Ita da Amnah Anty kuma tana zazzaga mata masifa dan ta gaji da lallashin se ganinsa kawai sukayi ya fado yana cewa

“Ina Amnah? Nace ki tattara mun yarana shine zaki rage wasu akan wane dalili ke wuce mu tafi” ya qarasa yana kama hannun Amnah da tunda ya shigo ta miqe, tundazun taso ta bisu amma kukan da taga Mamin nayi ya sakata tsayawa daman jira takeyi idan tayi shiru se ta tafi daga baya.

ASMA’U

Toshe kunnena nayi naqi jin lallashin da Anty takeyi mun dan kuwa ba abinda zata fada mun tunda taqi hanawa Bashir ya kwashe mun yara, kuka nakeyi haiqan, daman ba wai na gama mantawa da abinda ya faru bane Aa kawai dai na bawa kaina haquri ne na dangana shine yanzu za’a sakeyi mun fami.

Bashir ya rabani da aure na, ya kuma rabani da yarana sannan kuma ace nayi haquri wai na dena kuka ai wannan zance ma be taso ba babu wanda ze fahimci halin da nake ciki se wanda masoyi ya tabayi masa yankan qauna a rayuwa.

Shigowar da Bashir yayi ban ko daga kai na kalle shi ba seda naji yaja maganar Amna tazo su tafi kafin na dago fuskata data jiqe da hawaye tayi jajir na kalle shi nace

“Ina tunanin abinda ka fara sha Bashir yana gaya maka qarya. Yaranka kace na baka kuma na baka, idan ka manta ne kuma bari na tuna maka Amnah ba yarka bace qanwata ce babu kuma abinda ka hada da ita dan zama na takeyi a gidan ka yanzu kuwa bata abinda ta manta a gidan ballantana ta koma su dai da yake gidan Ubansu gasu can an baka itama zata zauna a gidan da aka biya da kudin ubanta”.

Wani kallo ya watso mun da na kasa fassara kona menene idanunsa sunyi fici fice har wata kwallar masifa ce ta taru a acikinsu, nuna ni yayi da hannu yace “bani da lokacin ki yanzu dan ba gurinki nazo ba, idan kuma kin isa seki hanani tafiya da ita mu gani” ya fizgi Hannun Amna zasu fita na jawo ta baya da qarfi har seda ta fizge daga hannunsa kafin na daka mata tsawa nace

“Wuce ciki, kai kuma ka fita idan ba haka ba wallahi se nayi maka abinda harka mutu bazaka taba mantawa dani ba. Maganar lokaci kuma har abada karka tabayin lokaci na Bashir saboda a sanda kake tunanin kayi lokacin nawa kafin nan ni kuma nayi maka nisa tamkar tazarar sama da qasa sedai kallo.

Daga yau ka dauka cewa bamu taba hada komai da kai a rayuwa ba Bashir, aure ne dai ya qare a tsakanin mu yara kuma da suka hada To gasu nan kaje ka kwada su ka cinye duk tsiya dai baka isa ka canza musu wata uwar ba Asma’un nan dai tana nan a matsayin uwarsu”

Na dakata na share hawayen fuskata kafin na cigaba da cewa
“Daga yau idan Anyi duniya dan manzon Allah na gama qunsar takaicinka Bashir kuma ka qaddara cewa naka shafin baqin ciki da zubda hawayen yana dab da budewa a rayuwa” Ina gama fadar haka na wuce daki na barshi a tsaye yana bina da kallo, jiki a sanyaye kamar wanda aka zarewa laka ya juya ya fice daga gidan.

“Allah yasa da gaske kikeyi, dukda da ciwo amma idan kika daure kika mayar da komai ba komai ba Ma’u zakiga ribar hakan a gaba. Bance ki dena son Bashir ba amma Ki share daga zuciyarki, ki gayawa kanki koda Bashir ko babu shi zaki ci gaba da rayuwa ki kuma tsohuwar Asma’un ki wani koke koke duk ba naki bane abinda be faru ba shi ake tara wanda ya faru kuwa sedai a kiyaye maimaita irinsa.

Kina kallonsa yanda yake abubuwan sa tamkar babu abinda ya faru, gidan da kika fita ya dakko wata ya saka dan ya nuna miki dake din da babu ke babu abinda ze chanza masa kuma walwalarsa yakeyi amma ke yana takalarki da duk abinda yasan ze quntata miki kuma ki biye masa ina dalili?

Ai wallahi yanzu shi ya kamata ki nunawa yayi babban Rashin da baze taba maida irinsa ba, ki tattara hankalinki guri daya ki koma aikin ki, ki ci duniyarki da tsinke dama ce yanzu ubangiji ya baki ta ki samu duk abinda kika rasa a baya.

Kin auri Bashir saboda kina mugun son sa yanzu kingani ga damar ki ta se irin mijin da kike so zaki samu kin kuma san kura kuren da kika tafka a zaben baya yanzu zaki kiyaye su shine kuma zaki zauna kina baqin ciki da abinda Allah ne ya so ki ya qwato miki yan cin ki.

Koda ace gaba zaki koma gidan Bashir Ma’u ina so kafin lokacin yasan kima da darajar ki ta yanda koda Allah ya sake qaddara zama a tsakaninku zeyi miki ruqo na gaske da bare sake bari ki kufce masa ba, amma kin zauna abu kadan ya jangwaleki kiyita masifa yana jin dadi haka mana Ma’u ki farka daga wannan magagin da kikeyi” haka Anty ta cigaba da gaya mun maganganu har seda ni kaina na ji haushin kaina kafin ta barni ta koma gida.

BASHIR
Sosai yanayi da kalaman Ma’u suka dake shi, babu abinda yafi tayar masa da hankali irin hawayen daya gani suna zuba daga idonta, me yasa shi a koda yaushe yake zama silar kukanta ne? Wai takamaimai meye dalilin daya saka ya kasa bawa Ma’u irin kulawar data kamaceta tukuicin sadaukarwar ta a gare shi?.

A duk sanda ya kalli cikin idonta yana hango tarin so da qaunar sa a ciki irin wanda yake saka mutum aikata komai domin farin cikin wanda yake yiwa wannan soyayyar amma a yau sam bega hakan ba illah tarin tsanar sa da dana sanin kasancewa dashi daya hango a cikin idanunta da suke zubar da hawayen nadama.

Harga Allah yana son Ma’u, yana kuma tsoron kar wannan abun daya aikata ya saka ta tsane shi domin a duk sanda So ya koma qiyayya yana zamowa me zafin gaske, idan kuwa har ace tarin so da qaunar da Ma’u take yi masa suka rikide zuwa Qiyayya tabbas ya shiga gararin rayuwa dan kuwa babu wani ruwa a duniyar nan da ze ishe shi wanke kansa yayi hasken da zata kuma kallonsa harta maida masa da wannan so da qaunar daya rasa.

Abu daya ne idan ya tuna yake sakashi jin dama dama wato cikin jikinta, a qallah yana da watanni bakwai kwarara da ze taka duk irin rawar da yake so daga qarshe ko taqi ko taso ya mayar da ita dakinta a sannan kuma ko sama da qasa zata hade babu wanda ya isa ya saka shi ya qarashe sauran igiyar datayi musu saura a tsakanin su koda kuwa Ma’u zata ringa yankar naman jikinsa ne saboda qi sedai ya mutu sannan ta samu yanci amma badai ya sake sakinta ba wallahi.

Da wannan tunanin ya koma cikin gida, duk yanda yaso ya rarrashi yaran sunqi sauraren sa haka ya haqura ya qyale su, a cikinsu ma yafi tausayawa Faridah da take mace ita kadai, da Amnah tana nan bashida ko wacce damuwa yasan zata kula dasu tamkar Ma’u tana nan amma yanzu besan yanda zeyi da Faridah yasan bazata sakw da Amirah ba.

“Kodai na mayar da ita gurin Ma’u?” Ya raya a ransa,
“Kai amma ai in nayi hakan kuma na kwafsa na gama buyagin banza tun ba’aje ko ina ba kenan taga gazawata, haka zata haqura har ta sake da Amirah da sauqi ma tunda ba nisa Ma’u tayi ba kullum zasu ringa ganin ta a hankali ma zasu warware su saba da zaman kafin komai ya daidaita mu ci gaba da rayuwar mu cikin farin ciki” Alhaji Malam Bashir ya sakw ayyana hakan a ransa.

Da rana Amirah tayi iya yinta ta musu jalof din shinkafa taji busashshen kifi da nama, ganin Bashir na zaune data gama harda zuwa ta kirawo su suzo suci kai tsaye kuwa Aliyu yace bazasu ci ba.

“Yaya kaje kayiwa yaran nan magana su fito suci abinci mana ni naje sunce sun qoshi” ta fada tana zama a kusa dashi, seya miqe ya shiga dakin, suna nan jugul sun dena kukan dai amma kowa yayi tagumi.

“Oya muje muci abinci se mu fita yawo ko ina kuke so muje?” Ya fada yana tsugunnawa a gaban gadon da yan biyu suke zaune, su daman basu tsawwala ba dan ba wani fahimtar budurin da akeyi sukayi sosai ba kawai duk abinda Aliyu ya fada ne sauran se su mara masa baya shiyasa suka suke zaune a dakin amma tun dazu Ahmad yake zungurin tagwan nasa yana masa radar su fita shi ya gaji sa zama, daman yunwa suke ji dan haka suka miqe da saurin su ya kama hannu su suka nufi qofa.

“Baban Mami fa? Bazaka bi mu ba?” Ya sake fada yana kallon Abdallah daya rabe guri guda, se yaron ya maqe kafada yace

“Aa ni gurin Mami zanje”.
“Toh muje kaci abinci seka tafi Mamin ko?”

“Abbi nima haka” Farida ta fada kamar zatayi kuka. Se ya waiwaya yana mata murmushi yace
“Muje toh kuci abinci me son zuwa gurin Mami ya tafi wanda zamu je yawo mu fita toh” nan da nan suka hau murna suka bi bayansa banda Aliyu da Jafar da suke tsaye nan fuska kamar Hadari, shima be kula suba, ai su ba yara bane kamar sauran idan yunwar cikin su ta ishe su zasu fito su nemi abinci.

Haka suka ci abincinsu da yaran ya biye musu sunata labari, zuciyar Amirah kamar ta fashe tsabar baqin ciki, taso ace sunqi cin abincin in yaso ta huta da sake yi masa wani girkin da daddare seta ajiye abinta amma yanzu shine zasu wani fito suci gashi se wani biye musu yake suna surutu duk sun bata gurin ai kuwa bari su gana sedai su gyara ko kuma shi din yayi dan ta gaji wallahi.

Bashir kuwa suna gamawa yace suje gurin Mamin kafin ya shirya se su tafi, haka suka kwasa da gudu zuwa gidan be ko bi takan Amirah dake mitar an bata guri ba ya shige dakinsa ya shirya tana kallonsa ya ci kwalliya yace mata sun fita da yara kar tayi girkin dare zasu taho da abinci.

ASMA’U
Muna zaune shiru su Faridah suka shigo da gudu suna rige rigen fadawa jikina. Da murnata na tare su wata zuciyar tana cemun
“Badai ya haqura ya dawo mun dasu ba kai amma da kamar wuya”.

“Mami unguwa zamu je da Abbi yanzu Yah Amnah ki chanza mana kaya” Ahmad ya fada.

“Iye yan gatan Abbi to ai kayan naku suna can gidan kuma na jikin ku ma babu abinda sukayi zaku iya zuwa dasu” na fada ina duba rigunan jikinsu na cire musu rigar sanyin da na saka musu dazu saboda garin da dan sanyi sanyi yanzu kuma yanayin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login