Showing 87001 words to 90000 words out of 260321 words

Chapter 30 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42683

dashi a gari an ce ya ajiye karuwa ya taso ta a gaba wai tazo su bawa Ma’u haquri tun bakwan safe take zaune se yanzun dana fito ga wannan Dramar da yakeyi kuma har wata kwallar takaici ce ta taru a idonta. Cikin muryar bacin rai tace

“Ni Yaya ka dakko ni tun safe ko wanka banyi ba bare naci abinci gashi yanzu Azahar tayi gaskiya ni yunwa nake ji”.

“Waya hana ki kici abincin ai gaki ka Kitchen nan duk bake kika jawowa mutane ba” ya hayayyaqo mata, seta miqe zata tafi Kitchen din nayi sauri tare ta da cewa “Ji mana, karki shigar mun Kitchen malama ku koma can inda ya aje ki ki nemi abinci ba’a nan ba” ban qarasa cinye biredi na ba na daure ledar kawai na kwankwade shayin na tashi. Seda na kullo qofar Kitchen din da mukulli na zare kafin na shige dakin su Aliyu na bar Bashir da Amirah baki sake suna bina da kallo.

Aliyu da Jafar na zaune da alama duk suna jin abinda yake faruwa se nayi murmushi na zauna ina cewa “me kuka bawa yan biyuna har yanzu basu tashi ba?”

“Game sukayi tayi Mami basu kwanta da wuri ba jiya dakyar suka tashi dazu suka ci abinci ma” Jafar ya fada. Whatsapp na bude a wayata ina shiga message din Maman Shukra ya fado nayi murmushi na bude
“Maman Farida ina fatan dai bada tashin hankali kika tunkare shi ba ko, kinsan fa irin wannan abun se a hankali da Addu’a kuma in ba haka ba a maimakon a samu sauqi se ka qara tunzura mutum” ta rubuta, se na mayar mata da cewa

“Ai baki sani ba, ashe Amaryar sa ce tazo sh ya sauke ta acan kin gansu tun dazu ya dakko ta tana nan”.

“Tab amma se abar Engineer, to ke me kakace yanzu?”

“Me zance kuwa, gasu can na barsu a palour ni ina daki ma bacci zanyi se anjim mayi magana” na fada dan na datse hirar.

Alawiyya yayata na duba naga bata online, fita nayi daga dakin na koma nawa dan ina so na l kirata, sanda na fito palour Bashir kadai na tarar har na wuce na yi kwana na shiga dakinsa. Addu’a nake Allah yasa tana ciki yau na gwada musu danyan kai daga shi har ita se Allah ya temaketa babu kowa har Toilet na duba bata ciki na kullo qofar na fito se ya tare ni yana cewa

“Ta tafi gidan Ghali daga can gobe seta wuce Gombe” (Ghali dan wan Baban su Bashir ne).

Wunin ranar zir haka yayi shi a palour daya ji motsina ze taso yana so yayi mun magana amma naqi bashi fuska sam da daddare ina jinsa suna waya yana ta masifa nidai qala bance masa, daya biyo ni dakina ma abinda tun tsahon zaman mu a gidan nan be taba kwana a ciki ba yana kwanciya na juya mukayi kai da qafa yana fita sallar Asuba kuma na saka Key.

Haka muka cinye satin, har zuciyata na huce kodan irin ban haqurin da ya ringa yi mun amma ban nuna masa ba, yanzu dai ina dafa abinci dashi kuma in yayi mun magana ina amsawa sakin fuska ne dai babu na kuma dena shiga sabgarsa sannan na koma dakina da kwana kullum kuwa se ya bini.

Bansan ya suka qare da Amirah ba nasan dai ta tafi, dukda abinda ya aikata ai ba laifi bane ko babu komai ai matarsa ce daman ai yana da ikon kaita ko ina amma yanda ya biyo da abun ne babu tsari a ciki. Dan haka fushin kwana biyu na qara kafin na ware muka koma daidai kamar bamu samu wani saba ni ba.

Amirah
Da baqin ciki da takaicin Ma’u da Bashir ta koma Gombe, har kuka tayi sanda take labartawa Addah abinda ya faru.

“Se kinga yanda ya rikice Addah harda durqusawa yana bata haquri a gaba na ita kuma se yankwana shi takeyi saboda ta nunamun ta isa dashi. Saboda wulaqnaci fa gidan Ghali ya turani na qarasa kwana sannan da zan taho ma Taxi yasa ta kaini Airport se a waya mukayi sallama”.

“Tab lallai Asma’u ta gawurta yanzu Bashir din ne ya duqa mata, lallai dole mu sake tashi tsaye. Ni ina ganin komai yayi lafiya yanda kwana biyun nan aketa abin arziqi ashe da sauran rina a kaba” Addah ta fada tana kama baki.

“Ai wallahi bata ci bulus ba, yanda ta rusa mun tsarina nima sena rama” Amirah ta fada, daga nan suka shiga qulle qullen yanda zasuyi su rama abinda Ma’u tayi mata.

Lagos
Ranar Juma’a data kama litinin a koma makaranta Amna da Farida suka dawo, ban gayawa Bashir ba na saka Naziru ya siya musu Tickets dan daga Yola Gombe aka kaisu se ganinsu kawai yayi ai kuwa ya ringa masifa akan me zan doro masa yara a jirgi su kadai me yasa ba’a gaya masa yau zasu dawo ba yaje ya taho dasu ko shi Nazirun ya rako su nidai nayi banza dashi tunda sun dawo ai magana ta qare.

Monday qalau muka rabu kowa ya tafi aikinsa ranar na dan jima a office saboda shirin Tafiya Abuja da mukeyi wani conferees se bayan Magriba na shigo gida. Seda mukaje kwanciya sannan nake gayawa Bashir dan saura sati daya tafiyar.

“Lallai Big woman anya nima bazan zo a dan sama mun guri ba naga fa kuna kwasa da yawa a office din nan naku” ya fada da dan murmushi yana danne danne a wayarsa, sena gyara zama ina cewa

“Kaidai bari wallahi yanzu ma fa package din tafiyar nan naji Accountant yana cewa kusan 700 huns za’a bamu each kudin TP da accommodation ni daman gidan Alhaji Qarami zan sauka kaga sena soke kudina, Goggo nake so ma na biyawa Umarar Azumin su tafi tareda Maman Ayman”.

“Hakan yayi kyau, nima idan na samu yanda nake so se mu tafi da ke ita kuma Amirah se taje Hajji”.

“Allah ya yarda toh” na fada sannan muka ci gaba da hira har bacci ya dauke mu.

Weekend din daya kama satin da za’a shiga zanyi tafiyar ranar Asabar da daddare na sake gaya masa zancen tafiyar base ranar Monday ya ganni da jaka ba.

Yana zaune na kawo masa coffees da yace yana so nake masa zancen ina cewa “Allah ma ya taimake ni Amna na gida yanzu da bansan yanda zanyi tafiya harta sati guda ba”.

Shiru ya mun yaci gaba da shan coffee dinsa nima se na mayar da hankali na kan Tv seda ya mula dan kansa se cewa yayi “wai dole ne se kinyi tafiyar nan?”

Ban waiwayo ba na bashi amsa “Kaji Baban Ali da wata magana, tun fa last week na gaya maka, me ze kaini toh idan ba dole ba”.

Tsakin daya ja ne ya saka ni waiwayawa na kalle shi, fuskar nan a mugun hade seda gaba na ya fadi dan rabon da nagan shi a irin haka an kwana biyu.

“Lafiya” na fada ina gyara zama na fuskan ce shi da kyau, se ya miqe kawai ya shige dakinsa nima na rufa masa baya.

“Kibar tafiyar nan kawai dan bazan iya zama har sati guda ni kadai ba” ya fada yana cire rigar jikinsa da alama wanka ze shiga. Sena marairaice cikin lumana ina cewa

“Haba Engineer satin fa kamar yaune qilan ma baza mu kai haka ba, kayi haquri ka daure In Sha Allah gaba idan haka ta taso zan nemi a chanza wani dani amma yanzu lokaci ya qure kaga jibi ne fa tafiyar”

A maimakon ya sakko se nagama kamat fetur na qarawa wutar dan hargagi ya shiga yi mun yana cewa “nidai na gaya miki kawai, ke ni aikin nan ma gaba daya bana sonsa daman idan mace taga tana samun kudi gani takeyi kanku daya tunda babu abinda zata nema a gurinka, kai ta yaya ma za’ayi mutum yana da mata amma ta tafi wani guri tayi har sati daya meye marabar sa da gwauro” bam ya shige Bandaki ya bugo qofar sena rakashi da ido kawai ina karanta Hasbunallahu wani’imal wakeel a zuciyata.

Abin ya motsa kenan, haka naja jiki a sabule na fice na koma dakina. Rasa wanda zan kira na gayawa wannan abu nayi ina zaune sega kiran Babbar yayar mu a dakin mu Anty Suhaima da take America ta kirani.

Bayan mun gaisa mukayi shiru dan babu sabo sosai tsakanin mu saboda ita da wuri tayi aure ta auri dan Abokin Baffan mu yan Kano ne a lokacin Baban sa shine Ambassador na Nigeria a America dan haka tunda tayi aure can aka kaita kusan shekara Ashirin da biyar yanzu.

Jin shirun naw yayi yawa ya sakata cewa “Ma’u lafiya kuwa kamar akwai abinda yake damun ki” haka kawai naji kuka ya taho mun ba kuwa ta hanani ba ta barni na yi abuna seda nayi shiru dan kaina kafin na gaya mata yanda mukayi da Bashir.

“Daman baya son aikin naki tun farko ne ko yaya” ta tambaye ni,
“Wallahi Anty be taba nuna baya so ba, tun ma ba yanzu ba kinsani kafin wannan nayi wau qananun ayyukan kuma be taba hanawa ba a koda yaushe yana bani goyon baya, yanzun mafa ya yarda yau ne kawai dana sake gaya masa zancen tafiyar shine kuma ya bullo da wannan maganar”.

“Shikenan, ki rabu dashi ki ci gaba da Addu’a zuwa goben ku sake maganar idan be yarda ba ki haqura karki tafi ba tareda izinin sa ba idan yaso ki gayawa Alhaji qarami se aji me yake nufi da aikin naki daman ai zaman aure dole akwai qalubale Ma’u Allah dai ya sa mu dace kawai” nasiha taci gaba da yi mun kafin mu ka gaisa da yaranta dukka su hudu sannan mukayi sallama bayan na tura musu da Number Aliyu da Amna da suka ce.

Ban koma dakin Bashir ba a zato na kuma ze biyo sahu amma har dare ya tsala naji shiru.

Da safe na sake tun kararsa da maganar se kuwa cewa yayi “In dai izinina kike nema toh ban yarda ba” ya sa kai ya fice daga gidan.

Yana fita na dannawa Dadan su kira dan kuwa bazata sabu ba, tas na gaya mata yanda mukayi tace na kwantar da hankali na zata masa magana, ilai kuwa da daddare ina zaune se gashi fuskarsa nan kamar Hadari yace

“Wato qarata kika kai Gurin Dada ko? Shikenan kije amma ki tabbata sena dauki hukunci akan hakan”.

“Tunda dai ka barni ai zance ya qare” na fada bayan daya fice daga dakin, washe gari na cale zuwa Abuja bayan na barwa yara komai da zasu buqata karma ya huce haushi na akansu.

Amirah
Sosai ta kunnowa Bashir wuta tunda ta fuskanci shi mutum ne me son a girmama shi ba kuma yason raini se tayi amfani da wannan damar gurin nuna masa ai Asma’u ta raina shi kuma abinda take nuna wa mutane kenan cewa tafi qarfinsa.

Da Samirah qanwar sa suka shirya komai dukda ita Samiran bata san amfani da ita Amirah tayi ba. Tana zaune ta kirata take bata labarin abinda ya faru ai Bashir ya durqusaw Ma’u, Smairah kuma irin masu dan banzan surutun nan ne idan taji abu kamar dukka dangi kowa yaji ne dan haka kafin kace me wannan Labari ya karade kowa kamar wutar Daji cikin haka maganar ta koma kunnen Bashir.

Amma saboda rashin Adalci irin nasa a maimakon ya ji haushin Amirah data fada tunda a gabanta akayi se laifin ya koma kan Ma’u a cewarsa da batayi masa boren da tayi ba ai da be durqusa matan ba har Amiran ta samu abin yayatawa ba wannan fushin ya qudure a ransa.

Kwana biyu tsakani har ya huce tayi masa zancen biyawa Goggonsu Umarah se akayi dace washe gari Bala ya kirashi, suna cikin waya yake ce masa

“Mutumina ashe Ma’u ta siyi gida nan kusa damu, jiya mun zagaya ta gurin naga gidan hadadde nake tambayar na waye akace na matar ka ne kamar ma guda biyu ne fa ko Su Aliyu ta siyawa ne”.

“Anya kuwa Ma’u ta siyi gida ba tare da na sani ba me zatayi dashi, ina ga dai ba nata bane sedai wata daga cikin yan gidan su ko” Bashir ya fada.

“Lallai Bashir baka san mata ba, ka manta lokacin baya kenan yanda yan uwanta suka tinga zugata akan karta doraka akan dukiyarta. Yanda take karbar kudin Hayar gidajenta ga Albashi me tsoka ai dole ta ringa siyan kadarori tana boyewa baka sani ba,

nifa wallahi nama ga baikenka kana zaune na tabbatar yanzu ta ninkaka sau uku a arziqi wallahi in bakayi wasa ba kwanan nan zaka zama mijin Hajia se yanda tayi dakai tunda tafi qarfin komai babu abinda zata nema a gurinka.

Da zaka ji ta tawa ma kasa ta ajiye aikin nan wallahi dan tana dab da finka Albashi bashi ne taqamarka ba”.

Wadannan maganganun na Bala dana Amirah su suka yi tasiri a ransa dan yana ganin abinda Balan ya fada gaskiya ne.

Tunani ya shigayi Rabon da ya dauki kudi ya bata ma shi harya manta daidai da kudin sati na man mota da yake bata yafi wata shida be bayar ba kuma bata tambaye shi ba.

Daman cefane baya yankewa a gidan kusan zece buhun huna kadai yasan yana siya amma sauran abubuwa tunda daman ita yake bawa kudin tayi mantawa yake kuma bata tambayarsa haka zega komai a ajiye. Yanzu a satin daya wuce ta ce masa Bilal ya turo mata wasu motoci idan yana so ita ma zata chanza tata ko School Fees din makaranta na wannan term din ita ta biya se daga baya ya mayar mata da kudinta gashi kuma a kullum cikin yin suturu na alfarma take daga ita har Yaranta har shi tana siya masa takalma da Agogo ga turaruka.

Wadannan abubuwan daya hasaso a shirmensa su yake ganin zasu sa tafi qarfinsa har ya kasa juyata gashi kuma sauran mutane ma sun fahimci cewa Asma’u tafi qarfinsa a ganinsa babbar gazawa ce kamar shi ace matar sa tafi qarfinsa dan haka dole ya dauki mata ki akai.


Kunsan December ansha Bukun kuna
Allah ya bawa Amaren mu zaman lafiya ya kawo na yan baya 🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 30

ASMA’U

Cikin kwanaki biyar muka gama abinda ya kaimu, ada naso na yi weekend na huta ne har nadan zaga dangi amma saboda yanayin rabuwar mu da Bashir yasa na fasa daga gidan Alhaji qarami ko gidan Yayata Junaidiyya da mijinta yayi Accident, naso naje na dubashi amma gudun kar sauran suce banje musu ba yasa kawai na haqura.
A ranar Juma’ar da muka gama na bi jirgin dare zuwa Lagos.

Kadaran kadahan Bashir ya karbe ni, ban damu ba na shiga sabgogina ina dai ta qoqarin ganin komai ya daidaita a tsakanin mu amma yaqi bada hadin kai sam.

Ranar Talata da daddare bayan mun gama cin abinci Bashir da Aliyu suka fita siyo Biredi sauran yaran kuma duk suka koma cikin palour ni kuma na zauna a Gurin Dining din ina danna waya, kiran Muslim Yaya nane ya shigo wayata, mun dan jima muna magana kafin mukayi sallama yana kashewa Khadija qanwata ta kirani.

Abdallah ne ya taso ya kawo mun littafinsa na quantitative reasoning ya kakare a wani guri daman ina jinsu da yayyan yanata su koya masa kowa yaqi dan haka na saka wayar a speaker muna hirar ina nuna masa.

Hirar wata faccalarta takeyi mun, babansu yana da kudi kamar su kashe shi amma irin matsolon nan ne ba’a cin kudin sa se akayi dace data tashi aure ta auri me kwadayi dan shi dalilin auranta ma saboda kudin baban nata ne.

Tofa tunda akayi aure yaga babu lashi se rashin mutunchin yau daban na gobe daban qarshe ya yiwo mata kishiya ma shine yanzu ba’a dade ba baban nasu ya rasu anyi musu rabon Gado ta samu kudi sosai se kuma ya dawo kamar yaron ta se yanda take so yakeyi har Kishiyar ma yanzu ya mayar mata da ita kamar me aiki kome take so shi za’ayi a gidan nan.

“Wallahi Anty se kin ganshi jiya da mukaje sabon gidan da tayi yana tsaye yanda kika san dan aiki daga tayi motsi ze zaburo yace Hajia me kike so Hajia me za’ayi, ni ban taba ganin meson zuciya irin Rabi’u ba wallahi” Khadija ta fada.

Dariya nayi ina cewa “kudi ake gaya miki huce takaici kenan, ai idan mace ta gawurta zakiga har mijin ma wani shakkar ta yakeyi balle kuma kishiya. Shiyasa kika ga mun dage muna neman su maganin wulaqanci” na fada dai dai sanda Bashir da Aliyu suka shigo, wani kallo dana kasa fassara ma’anarsa ya yimun kafin yasa kai ya shige dakin sa.

Hirar mu muka ci gaba sannan mukayi sallama lokacin na gamawa Abdallah Homework din se na tashi daga gurin nima na shiga dakin Bashir.
Qarar ruwa da naji yasa na gane yana Toilet, sena zauna a gefen gado ina jiransa ya fito.

Kudi nake so na ara a gurinsa ina so na qarasa mana siyayyar kayan sallah dan haka nakeyi kafin lokacin yazo na siyi komai idan ya bani kudin se nayi wasu hidimar dasu yanzu kudaden hannuna duk na tattara na bada kudin Umarar Goggo daman Kudin Hayar da zan karba na saka rai dasu to su kuma tun kafin suzo ma na bada Aron su.

Seda na barshi ya gama shiryawa ya zauna sannan nace “Baban Ali Aron kudi nake so dan Allah”.

Shiru yamun ban damu ba na cigaba da cewa
“Kasan na gaya maka zancen tafiyar Goggo to na bada kudin, wadanda kuma nake saka rai na hayar gidajen nan wallahi Yaya Abubakar ya rance wai ya cikawa su Bilal sun tada ginin gidajen su bayan Babbar Sallah nan muke saka ran bikinsu”.

A maimakon ya amsa ze bani ko baze bayar ba se ji nayi yace “Lallai Ma’u karanki ya isa tsaiko.
Wato ban isa ki tambayeni kudi ba sedai kice na ara miki ko? To bari kiji ni ba sakaran namiji bane da har kike tunanin dan kina riqe wasu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login