Showing 78001 words to 81000 words out of 260321 words
Chapter 27 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
bazata sabu ba wallahi.
Kayanta hada ta kai masa Dakin Nazirun, sanda ta shiga yana wanka, seta nemi guri ta zauna tana jiran ya fito dan babu yanda za’ayi ta barshi ya tafi wallahi.
Da gudun bala’i ta fada jikinsa tareda fashewa da kuka lokacin daya fito daga wankan, gaba daya yayi baya kamar zasu fadi Allah ya taimaka ya dafe bango dan a bazata ta fado masa se ya tureta daga jikinsa yana cewa “ke mahaukaciyar ina ce zaki fadowa mutum haka idan da na fadi naji ciwo kuma fa, mtsw” yaja tsaki yana hararar ta.
“Yanzu dan Allah ko tausayina bazaka ji ba, daga zuwanka jiya ko zama bamuyi ba kaji damuwata ba yau zaka ce zaka tafi saboda wadda ka baro acan tafi ni, shi kenan kaje, amma sedai ka zaba ko ni ko ita wallahi dan na gaji da yanda kake nuna banbanci a tsakanin mu. Gara ka rabu dani kaje can ka zauna da matar so”.
Kallonta ya ringayi har ta kai aya. Wai ya zaba ko ita ko Ma’u shi abun ma dariya ya bashi a ransa yace “idan zabi za’a bani dole sedai na zauna da daya yarinya aike zan saitawa hanya, na rabu da Ma’u nabi ina naga haske??
A fili kuma se ya saki murmushi ya janyo ta jikinsa yace “Allah ya huci zuciyarki haba Amaryata, yanzu kina kallo ko gida banje ba jiya na taho garin nan ko iya wannan be isa ya nuna miki yanda na damu dake ba.
maganar na zaba a tsakaninku kuma ai bata taso ba kinfi kowa sanin Yanda Nake Son Ma’u, ban kuma ga abinda ze raba ni da ita ba se mutuwa sannan kema saboda ina sonki na aure ki dan haka ki dena kawo maganar rabuwata da daya daga cikin ku.
And official call na samu dole na bar garin nan a yau, idan kuma so kike a kore ni daga aikin na rasa kudin siya muku abinci shikenan”.
Qara lafewa tayi a jikinsa, taji haushin yanda ya wani fadi yana son ma’u amma ai ba qarya bane ita ma ta sani, ganin yana cikin yana yi me dadi yasa ta ce bari ta gwada sa’arta.
Tana jikinsa suka qarasa kan gadon ya zaunar da ita ya dakko mai ya fara shafawa, taya shi ta shiga yi kafin cikin muryar shagwaba tace “Yayahh”
Kallon ta yayi ba tareda ya amsa ba, ganin hankalin sa yana kanta taci gaba da cewa
“Toh naji Yaya ka tafi amma da ka gama abinda zaka yi ina jiranka ka dai san alqawarin da kayi mun ni uku nake so ma ba biyu ba” ta fada tan rufe fuskarta da hannayenta.
Murmushi yayi yace “karki damu, just be ready for me”.
Murmushin ita ma tayi kafin ta ci gaba da cewa
“Se kuma Yaya gaba daya kayan dakina an lalata su kuma...” ganin kallon da yake mata lokaci daya fuskar sa ta chanza ya sakata yin shiru,
“Uhm ina jinki kuma me” ya tambaye ta yana saka rigar sa, seta girgiza kai tace “ babu komai”
“Gara da ya zama babu komai din” ya fada yana zama ya jawo kayan abincin ya fara ci. Seda ya gama tsaf ya zuge jakarsa sannan ya kalleta yace
“Karki sake kawo mun maganar kayan dakin ki ko wani abu, saboda banyi lissafin nawa damage din nace a biya ni ba ko?
Zan tafi yanzu, zuwa gobe ki koma gida”.
Seta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace “Dan Allah yaya gidan yayi mun girma da yawa tsoro nake ji, ka barni na koma gidan Addah kaga in nace zanzauna anan ma kullum fada muke da Anty Fainusa”.
Seda ya kalleta na dan wani lokaci kafin yace “ok ki koma din, shikenan ni zan tafi”.
Ganin bata motsa daga gurin ba sema yan hawaye da take gogewa yasa yace mata
“Come on babu ko goodbye” ya fada yana dagata tsaye, light kiss ya mata kafin ya saketa yayi gaba ta bishi a baya. A qofar dakin Alhajin su taci burki, harya saka qafa jij ta tsaya yasa ya waiwayo ya kalleta
“Shigo mana” ya fada yana qarasawa ciki. Se Alhajin ya dago ya kalleshi yana murmushi yace “Amirah ce ko, ka barta kawai ban san menayi mata da bata iya zuwa mu gaisa ba”.
“Hmmm” kawai ya iya cewa sukayi Sallama da Baban yayi masa fatan sauka lafiya ya fito. Shareta yayi ya shiga dakin Dada itama sukayi sallama kafin ya fito har Naziru ya saka masa jakar sa a mota.
Tana bayansa kamar Jela suka fita, tunda yaji bata zuwa tana gaida Baban ransa ya sake baci, gaba daya dana sanin zuwa ma yake yi dan dai babu biyan buqata se kayan takaici daya kwasa kawai haka ya shige motar Naziru yaja tana tsaye kamar ta kurma ihu, yanda suka faro a dadin rai taso su qarashe haka ko ba komai ta samu kudin kashewa yanzu gashi ya tafi da sabon fushi.
Sanda suka isa ya taki sa’ar samun qaramar mota sharon saura mutum biyu dan haka ya biya kudin mutum biyun kawai ya shiga suka dau hanya. Seda tafiya ta fara miqawa sannan ido ya raina fata.
Rabon daya je Lagos a mota kusan Shekara Goma sha biyu kenan sanda ya taba samun wani aiki har aka kirashi interview daga qarshe aka ce wai ba’a dauke shi ba.
Wannan aikin ko lokacin daya same shi da aka kirashi documentation harda ticket din jirgi Alhaji Qarami ya hada masa na zuwa da dawowa tundaga nan kuwa da Al’amura suka bude masa shida tafiyar mota sedai inda jirgi baya zuwa.
Akace tafiya yankin Azaba tabbas Bashir ya kwashi Azabar tata. Wata irin tafiya yayi da a rayuwarsa ze iya cewa be tabayin me wahalarta ba. Haka suka kwana suna tafiya sau uku kacal suka tsaya shima sallah kawai sukeyi wasu su nemi abinda zasu ci sannan a qara wuta.
Bashir dai Azumin dole yayi in banda ruwa babu abinda ya shiga cikinsa har suka Isa Lagos da Asubar Ranar Juma’a.
Firkai firkai dashi kamar wanda ya qwato daga hannun Yan Kidmashin ya shiga kwankwasa gidan bayan da Shatar Taxi din daya dauko ta sauke shi.
Lokacin Asma’u na kitchen sauran yaran kuma suna zaune a palour suna qarasa saka sport wear dinsu dan yau Juma’a. Da farko duk basu zaci gidan ake kwanwasawa ba tunda waye ze zo musu da sassafen nan shida ma yanzu tayi.
Jin Basu bude ba yasa Bashir neman dutse ya hau buga qofar kamar an aiko shi dan a yanda yake ba shida qarfin da ze fara binciko keys a jakarsa, daga ciki Asma’u ta fito daga Kitchen din tana kallon yaran da sukayi cirko cirko tace
“Waye wannan yake mana bugu kamar mara hankali” seta nufi gurin qofar. Seda ta leqa ta yar bular da ake ganin mutum, da mugun mamaki taja baya. Fuskar Bashir ce, tasan a kowanne yanayi bazata kasa gabe shi ba amma da seta ce wannan me kama da shi ne.
Qofar ta bude da sauri tayi gefe ganin yana neman fado mata ya wuce ciki bayan ya watsar da kayan sa a bakin qofar, seta kwalawa Aliyu kira ya tafi da sauri ta nuna masa kayan tana cewa “shigar masa dasu dakinsa” ta juya ciki tana mamakin daga ina yake.
Bashir kuwa Yana shiga ya zube akan kujera, yunwa, gajiya da bacci sun hadar masa gaba daya. Kallonsa yaran suka shigayi kamar sunga baqo kafin suka gaishe shi ya daga musu kai dan baze iya bude baki ba.
Yanda Asma’u tayi kamar bata san da wanzuwarsa a gurin ba yayi bala’in bashi mamaki, shirinta ta ci gaba daya yi. Yana kallo suka qarasa cinye abin karin su yaran sukayi masa sallama suka fice gurin mota ita kuma ta shiga daki ta dakko jakar ta.
Ina sane nayi tamkar na manta dashi a gurin, yana ganin nayi hanyar qofa yai saurin dakatar da ni da muryarsa a har dashewa tayi saboda yunwa yace “Ma’u baki ganni ba zaki tafi kuma”.
Seta na dakata na kalle shi, da dan guntun murmushi a fuska ta nace “Na ganka Baban Ali ai nayi maka sannu da zuwa tunda ka shigo ko baka ji ba?”
“Hmmm” ya fada kafin ya yunqura yana cewa “Nagaji wallahi a mota na taho, gashi qarfe goma ya kamata inje office ki taimaka mun da abinda zanci bari nayi wanka”.
Se da na saki wata dariyar takaici, ina kada key din hannuna nace “wato ka rantse dai se ka biyo mota toh ai gashi dai kaji abinda ake ji. Abinci kuma akwai komai na buqata a Kitchen se ka nemawa kanka kaga mun makara ma se mun dawo” na juya nayi tafiyata ina jin yanda ya raka ni da kallo har na kulle qofar.
Wato daga dan rainin hankali se Bashir, Allah ya qara. Abinci kuwa babu komai a Freezer mun cinye kwana biyun nan kuwa ban zauna ba bare nayi ko miya ce na ajiye.
Malam Bashir kuwa dakyar ya iya miqewa ya shiga Kitchen din, ya zata ze samu ko ragowar abinda sukaci ne ya tarar da wayam, ya bude Freezer nan ma danyun nama ya tarar babu ko guntun abinci.
Cike da takaici ya bude Fridge din shima babu komai se tarkacen ruwa da lemo se wani guntun nama ya samu a foil paper ya dauka da sanyin sa da komai ya cinye.
Ganin fa babu mafita ga yunwa ga lokaci na sake qure masa yasa ya kunna Fanfon Kitchen din ya tari ruwan zafi, Madara da Milo ya zuba sosai ya dagawa daya ya kwankwade ya sake hada wani yasha rabi ya hango bread ya dauka ya hada, seda yaji cikin sa ya dan farfado sannan ya haqura yaja kafafuwansa ya tafi daki.
Wayar s ya fara sakawa a chaji dan tun a hanya da dare ta mutu, Yau daya se be ji haushin abinda Ma’u ta masa ba, idan da haka kawai ne tayi masa wannan wulaqancin yasan me raba su se Allah amma yau daya tuna girman nasa laifin se yaga ai ba komai tayi masa ba.
Kamar me maye haka yana layi yayi wo wanka ya fito, badan ba kwanciya zeyi ya dan rage bacci amma yasan tabbas ya kuskura ya kwanta a yanda yake jin baccin nan qila sedai ya farka yaga magriba tayi.
Bayan ya saka kayan sa ya tattara abinda ze buqata kafin ya kunna wayarsa yayi order Bolt, se ya fito qofar gidan ya zauna kamar wani Almajiri, yunwa yake ji dan ba wai ya qoshi bene kawai haqura yayi idan ya fita se yaci abincin sannnan ga bacci har ji yake kamar zazzabi ze rufe shi, haka ya hau motar suka kama hanya.
A cafeteria office din su yaci abinci, Patrick abokin aikin sa da suka shiga tare ya ringa kallonsa da mamaki ganin yanda yake lodar abinci kamar wanda ya shekara be ci ba, kasa daurewa yayi yace masa
“Bash lafiya kuwa ji yanda kake cin abinci?”
“Bazaka gane ba, rabo na da abinci tun shekaran jiya”.
Dakyar ya iya kaiwa qarshen meeting din, suna gamawa suka fita sallar Juma’a. Bayan sun dawo Office din sa ya koma ya kwanta ya ringa bacci ba shi ya farka ba se qarfe bakwai shima Security da suke bi office office ne bayan an tashi suka ga fitilar sa a kunne dan haka sukaje su duba ko lafiya tunda be saba kaiwa dare a gurin ba.
Haka ya tattara a gida ya wuce gida, da murnar sa ya shiga dan tun daga waje ya jiyo qanshin tuwo da miyar kuka harda man shanu abinka da me jin yunwa.
Ya bude qofar ya shiga, fuska a sake Ma’u tayi masa sannu da zuwa harda tambayar ya akayi yau ya dade yace bacci ne ya kwashe shi.
Da zumudinsa yai sallar magriba da Isha ya sako jallabiyya ya dawo palour aka kame akan kujera yana jira ayi masa tayij abinci ya kwashi gara amma har kusan minti goma da zaman sa yaji shiru sema harkar gaban su kawai suke.
Gyaran murya yayi yana kallon Ma’u dake dannan waya yace “Akwai abinci ne yunwa nake ji”
Seta dakata ta dago ta kalleshi da murmushi tace “ai kuwa babu dan ban san zaka dawo ba”.
“Kamar ya baki san zan dawo ba ce miki nayi zan tafi wani gurin ko yaya, sannan nida gida na ayi abinci ace baza’a a jiye mun ba saboda me? Haka fa dazu da safe kika ce mun akwai abinci na duba ko ruwan zafi baku ajiye ba” ya fada a hasale, dan ya rigada ya gama saka rai da Tuwon.
“Ko ajikina na sake gyara zama nace “Aa abin bana zafi bane bafa Baban Ali, gani nayi yanzu ai Idan zakayi tafiya baka fada seka isa inda zakaje toh gudun kar mu ringa asarar abincin yasa mukeyi dai dai cikin mu, idan kace zaka ci se a dafa dakai”.
Abubuwa sun sha kaina, idan na samu sarari zaku jini gobe idan kuma ban samu dama ba se Monday In Sha Allah 🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)
Wattpad @MaryamahMrsAm
Page 28
Washe Gari Asabar tunda nayi sallar Asuba na koma bacci ban farka ba se goma na safe. Ko yaya Bashir ya qare jiya oho dan tunda na gaya masa babu abinci naji ya fara jan kwafa da tsaki na kwashi qafafuna na bar musu gurin, dan karma a biyo ni a dameni seda na murzawa qofata key sannan na kwanta.
Tsaf na shirya cikin wani Material baqi doguwar riga bayan nayi wanka, tundaga dakin nake jiyo kaya kaya alamar Game suke ko ana musu akan wani abun ina bude qofata Yan biyu na suka taso da gudu suka riqe ni.
“Kai ni yunwa nake ji karku kadani me kuka ci ne” na fada ina kama hannayensu, se Ahmad yace “Indomie Yah Amna tayi mana da Tea Abbi kuma gashi can yanzu aka soya masa Irish”.
Kallon inda yake nuna mun nayi muka hada ido da Bashir daya watso mun wata harara kamar idonsa ze fado, duk yanda naso na basar seda dariya ta kufce mun dan haka na wayance ina nufar inda yake nace “Baban Ali barka da safiya, kace kaima yanzu ka tashi? Bari nazo muci dan Allah yunwa nake ji idan bamu qoshi ba se a qaro wani” nayi maganar ina jan kujerar da take kallonsa na zauna.
Ban damu da shirun daya mun ba na fara hada Tea na ina masa surutun da na tabbatar sake qular dashi nakeyi, na gama naja kwanon dankalin, sena bude baki ina kallonsa nace
“Kai Duk wannan da kai kadai zaka cinye shi?”
Can qasa kaman an fuzgo maganar daga bakinsa naji yace “Banci abinci da daddare ba jiya da yunwa na tashi”.
Kallonsa nayi, naji tausayinsa kadan dan nasan Bashir da abinci ci ne dashi kamar dan kwallo, cikin jimamai nace “Ayya meyasa ka kwanta da yunwa da ka saka Amna ko Spaghetti ce ta dafa maka ai”.
Shiru ya sake yi mun, nima ban sake magana ba na fara cin abinci na, ya rigani gamawa, seya miqe ya shiga dakinsa ba dadewa ya fito ya chanza kaya ya saka Caftan na Yadi kansa babu hula. Key din motarsa ya dauka, be mun magana ba ya fice yara suna masa a dawo lafiya.
Harya tada motar se gashi ya shigo, ko me ya tuna oho se ji nayi yana cewa “zan fita amma ba jimawa zanyi ba saura yauma karku ajiye mun lunch”.
“Wa ya isa yaqi ajiye maka, jiyan ma aka si aka samu baka ce zaka dawo ba, amma yanzu tunda munsan kana nan ai zamu girka da kai” na fada ina dan murmushi. A raina nace “da bakayi magana ba wallahi yau ma dakaga Akuya sedai ka siyo ko kayi wunin yunwa.
Jellop rice nayi da pepper soup din tarwada, sena yiwa Bashir pepper meat dan baya cin Tarwada shi se gasashshiya.
Muna cikin yin lunch Amna ta kalleni tace “Mami idan mun gama muje gidan Baba?”
“Za kuje ku dame su ko kunsan dai yau Weekend Baba yana nan zaku hana shi hutawa”.
Bashir ne yace “Baya nan Ya tafi Zamfara tun jiya, idan kun gama kuje dama yau baza mu fita ba sedai ko gobe”.
Muna gama cin abincin kuwa bayan sun tattare kwanukan suka tafi ita da Farida dasu Ahmad, Aliyu da sauran kuwa Ball suka dauka suka tafi Filin da suke bugawa gidan ya rage daga ni se Bashir.
Qin zama nayi na shiga qaqale qaqalen ayyuka dukda na fahimci nufin Bashir, ganin da yayi bani da niyyar saurar sa, ina tsaye ina goge show glass din farantai a Gurin Dining kawai naji anyi sama dani, duk yanda naso nayi tawaye a dole fushi nake amma yaqi bani dama, daman abin be kai zuci ba kuma nima nayi kewar sa nan da nan nima na bada kai bori ya hau sosai kuwa na gigita Bashir.
Ina zaune a gaban mirrow ina Busar da kaina bayan nayi wanka ya shigo dakin yana waya, ta cikin mudubin muka kalli juna murmushi me kyau da narkar da zuciya ya sakar mun kafin ya qaraso ta bayana yana taba Gashina yaci gaba da maganar sa be jima ba ya kammala seya ajiye wayar akan mirrow ya karbi Dryer yana cewa “Dama baki wahalar da kanki ba dan ba’a gama ba”
“Wasa kenan” na fada ina zaro ido, saman da yai dani yasa sauran maganar suka maqale ban samu kaina a hannun sa ba seda aka kira Magriba.
Ranar haka mukayi kwanan farin ciki duk fushin nan seda Bashir ya bi ya kore mun shi. Se wani nan nan yake dani ranar ba’ayi wata doguwar hira ba kowa ya tafi ya kwanta. Muna kwance a dakin sa nayi pillow da dantsen hannunsa yace
“Dan Allah Ma’u karki sake horani da yunwa kinji”
Dariya na sheqe kafin nace “wannan din ma bada gayya nayi ba, aka si kawai aka samu”.
Lafiya qalau muka cinye Weekend din mu ranar Monday Amnah suka fara WAEC, da yake practical suka farayi sha biyu zasu fito dan haka nace mata ta taho gida kawai idan ta gama sauran idan sun tashi Zan dakko su yanda muka saba.
Dawowar da Amnah takeyi