Showing 231001 words to 234000 words out of 260321 words

Chapter 78 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42729

ce zaki mun fadi ina jinki".

"Oh ga mahaukaci yana magana shine dukkan ku zaku mun shiru ko? Malam tashi ka fita ke kuma Ma'u zaki san ni kike wulaqantawa akan wani can dan iska da be san darajarki ba" Bashir ya fada a haukace kamar ze rufe mu da duka.

"Ko dai mu bari anjima na gaya maka a waya? Kaga yanzu akwai hayaniya bazata barmu mu tattauna da kyau ba kuma maganar tana da buqatar nutsuwa sosai" na fada ba tareda na mayar da hankali akan shirmen Bashir ba

"Aa muje waje toh ko cikin mota dangaskiya kika ga na tafi ba tareda naji dalilin kiran nna ba toh inaga yau bazan iya bacci ba"

Dariya nayi na miqe ina cewa
"Gaskiya dai muje nasan ko ka ji din ma duk haka take be zama lallai ka iya bacci ba yau" fizgoni da akayi baya yasa nayi shiru ina gama daidaita tsayuwata kuwa na kwashe shida mari a mugun fusace nace

"Rashin kamun kan nawa be kai kowanne gaja ya ringa dora qazamin hannunsa a jikina ba" na waiwaya na kalli Yusuf da yanayin fuskarsa ya chanza zuwa matuqar bacin rai nace

"Yusuf bazan iya magana yanzu ba saboda raina ya baci, kaje kawai ka gayawa Alhaji Qarami sati biyun daya saka sunyi yawa a mayar dashi Juma'ar nan me zuwa"

"Bangane abinda kike nufi ba Asmy? Me za'a dawo dashi wannan juma'ar ko daurin auran mu kike nufi?" Ya shiga jero mun tambayoyin a rikice, wani mugun kallo na jefawa Bashir daya dafe kunci yai mutuwar tsaye nayi kafin nace masa

"Haka nake nufi ko yayi maka wuri da yawa.." kafin na idar da maganata ya kife a gurin yayi sujjada ya dago cikin wata kalar madaukakiyar murna ya riqo Bashir yana cewa

"Nagode Nagode Bashir ka gaya mun dame zan biyaka a rayuwa? A da na dauka a matsayin babban abokin Adawa ashe ban san banida masoyi sama dakai ba tunda gashi kayi silar da zan mallaki muradin zuciyata.

Kai na rantse ka shirya samun double promotion, a ina kake aiki? Koda yake barshi zan binciko da kaina" seya sake shi ya juyo ya kalleni

"Wife! Ina fatan wannan hukuncin ya zama mafi Alkahirin hukunci da kika taba yankewa a rayuwarki bari naje zamuyi waya" ya kwasa da gudu kamar yaro ya fita, seda naga rufe qofar sa kafin na juyo kan Bashir muka hada baki ni ina cewa

"Fitar mun daga gida kafin nayi maka tijarar da baka taba zato ba dan daman saboda shi na daga maka qafa kar nayi abinda zan zubar da mutunchi na a gabansa"

Shi kuma yana cewa
"Aure zaki daura da wani namiji nan da sati daya Ma'u? Dagaske zaki iya rayuwa da wani bayan ni? Nasan kinyi ne dan ki baqantamun rai na yarda amma ki janye dan girman Allah.

Bana nufin duk abinda na fada subutar baki nayi da kishinki da yake damuna amma kema kinsan ba abinda nake nufi ba kenan" ya fada yana durqusawa kamar ze kamo qafafuna.

Juyawa nayi ina cewa
"Karka ja nayi abinda yayanka zasu tsaneni Bashir tunda sauran mutunchin juna a tsakanin mu ka fita, badai ni ka kira mara kamun kai ba? Ka jira na fito daga daki yau zan nuna maka qarshen rashin kamun kai kaji ko" na shige dakina ina tunanin me zan aikatawa Bashir da zan nuna masa bashi kadai ne saitin kansa yake gocewa ba, nima wani lokacin nawa notinnan suna tabuwa.



Posting se baba ta gani 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page. 61

AMIRAH A DAREN JIYA

Se dare Bashir ya koma gida har sannan tana nade tana jiran yazo ya rarrasheta. Bayan sallar Isha ya shiga lokacin ta gaji ta fito palour tana zaune tana kallo ga yunwa tana ji amma ta kasa tashi ta girka abinda zata ci, jira takeyi ya dawo se suje su siyo abinci.

A sake ya shigo gidan tayi masa sannu da zuwa ya amsa kafin ya ajiye ruwan dispenser daya siyo ya dawo palour ya zauna yana cewa
“Kawo mun Abinci yunwa nake ji”.

Seta tsaya tana raba ido, wane abinci kuma yanzu ita da take jira ya dawo su siyo shine ze zo yana wani tambayarta dan haka ta gyara zama a shagwabe tace

“Nima fa Yaya yunwa nakeji, kai nake ta jira tun dazu ka dawo se muje muci abincin”.

“Saboda babu kayan girki a gidan nan ko kuma baki da hannun da zaki dafa ko yaya?” Ya fada cikin muryar bacin rai, zata qara magana ya daka mata tsawa yana cewa

“Ki wuce ki samar mun abinda zanci Yanzu bana son bata lokaci, sannan daga yau ma idan zakiyi girkin dare ki ringayi tareda yara anan zasu ringa cin abinci”.

Harta miqe ta koma ta zauna tana cewa
“Wane Yara zan ringa girki dasu ba a gidan su suke ba sannan kuma ni zan ringa musu abinci gaskiya bazan iya ba”.

“Ba wai shawarar ki na nema akan zakiyi ko bazakiyi ba umarnine tunda gidan ubansu ne dole ki dafa abinci ki ajiye musu ko bazasu ci ba, kuma kitashi ki samar mun abinda zanci yanzu karki bata mun rai”.

Miqewa tayi ta tafi Kitchen din tana mita “haka kawai wallahi babu dan da zan yiwa girki yaran ma suna gurin uwar su ace ni zan basu abinci wannan ma bame yuwu ba bane ai”

Haka ta dora ruwa ta saka kwai guda biyu sannan ta dora wata tukunyar ta hau dafa musu Indomie, a maimakon ta jajjaga attaruhu ta zuba se kawai ta saka dakakken Yaji ko Albasa bata saka haka ta zuba masa a plate da kwai kwalli daya a gefe ta saka fork ta kai masa.

Akan centre table ta ajiye, ta koma ta dakko masa ruwa da lemo sannan ta dakko nata abincin harta fara ci sannan Bashir ya fito daga dakinsa ya chanza kaya da alama wanka yayi.

Seda ya zauna akan kujera kafin ya kalleta yace “Ina abincin nawa?”

“Gashinan tun dazu na gama baka fito ba Allah yasa ma bata huce ba”.

Wani kallon banza yayiwa farantin da abinda yake ciki kafin ya saka hannu ya dauka ya tona Indomin da cokalin ciki yana kallonta yace

“Ni zanci wannan abun? Meye wannan kikayi? Idan ma Indomin zaki dafa haka akeyi duk kayan hadin da suke a cikin Kitchen kika gagara sakawa shine zaki kawo mun abu kamar na yan birsin ga wani kwai guda daya akai”.

“Wallahi Yaya ka fiya qorafi kaci mana kaji ai tayi dadi ba gashi ni har na kusa gama cinye tawa ba kuma wane hadi za’ayiwa Indomie bayan wannan harfa yaji na zuba a ciki dan tayi dandano....”

A mugun zuciya ya wulla mata farantin Indomin Allah ya taimaketa be qarasa kanta ba ya fadi a qasa ya tarwatse abinka da tangaran, a tsorace ta kalle shi, ya miqe yayi yo kanta se kuma meya tuna ya kaiwa Iska naushi kafin ya zari key din motarsa yana cewa
“Allah yasa na dawo na tarar da gurin nan a haka” ya juya ya fita.

Badan tana tsoron abinda kaje ka dawo ba babu abinda ze sakata gyara gurin haka ta dakko tsintiya da mopper ta kwashe fasashshen tangaran da Indomin ta kai shara kafin ta saka ruwa ta goge gurin.

“Haka kawai mutum se baqar zuciya kamar kuturu ina laifina dan Allah dama na dafa, ni da yasan baze ci ba se ya bani na qara dan ban qoshi ba yanzu ya wa mutane Asara aikin banza kawai” haka dai ta gyara gurin tsaf ta wuce dakinta ta fada wanka, tana fitowa ta shiga shiri shafa wancan goga wancan ta gama ta saka wata hadaddiyar Night gown ta gyara gashinta tsaf ta wuce dakin Bashir dan har ga Allah a matse take.

Tana kwance tayi daidai tana chatting ya shigo dakin fuskar nan kamar hadiri, to jiki da jini gashi daman kwana ya dade rabonsa da abin dole ya ajiye fushi suka raya sunnah kafin sukayi baccinsu cikin salama dukda seda a ka kusa sake wani fadan da yace taje tayi wanka tace seda safe, dataga yana neman bata mata farin cikin data samu dole tayi wankan suka koma sukayi bacci.

Washe gari ma lafiya qalau suka tashi, ta cije ta daure tayi duk abinda ya kamata akayi sa’a kuwa harta hada masa abin karyawa suka zauna beyi qorafi ba. Seda ya gama suna zaune a palour yake cewa

“Yaran nan kinji shiru har yanzu babu wanda ya shigo ko basu tashi bane”.

“Eh qilan kasan jiya an sha ruwa gari yayi sanyi may be shi yasa basu fito da wuri ba” ta fada a fili a ranta kuwa zagi take auna musu tana Addu’ar Allah yasa kar su zo.

“Bari naje na karbo katin wuta shaf na manta jiya dana fita ban siya ba naji kuma mitar tana qara” ya fada yana miqewa, seda ya sako jallabiyya ya dauki muqullin motarsa kafin ya fita, yana fita itama ta miqe akan kujera ta kwanta ranta fes a qarshe dai ta samu irin rayuwar da take so ita da Yayanta a gidan su su kadai suna zuba soyayya.

BASHIR
Yana fita qofar gida ya ga yaran suna Ball, gaba daya suka gaishe shi banda Aliyu da tunda suka hada ido ya juya baya yana hada fuska se kawai Bashir din ya girgiza kai tareda yin qwafa ya kama hannun Abdallah yana cewa

“Kun tashi daman me yasa baku shgo gida ba toh?”

“Abbi Mami ta hana tace idan muka sake zuwa gidan seta cire mana kunne ko Yah Abdallah” Ahmad yayi zuruf ya fada dan daman duk cikinsu shine me dan banzan surutu ai kuwa Aliyu ya kai masa duka yana cewa
“Waya tambayeka me shegen surutun tsiya kawai”.

“Idan ka sake dukan sa Aliyu sena saba maka, ita Ma’un ce tace kar ku sake shiga gidan yayi kyau zan nuna mata kuwa na fita iko a kanku” Bashir ya fada kafin fuu ya juya ya koma cikin gidansa.

Amirah da har bacci ya fara daukanta bude qofar sa ya farkar da ita se ta miqe tana goge ido tace
“Wai har ka dawo? daga dan kwanciya ashe bacci ne yayi gaba dani ban sani ba”.

“Wai me Ma’u ta dauki kanta ne har ni zata ce Yarana karsu sake shigowa gidan nan saboda taga na saka mata ido na barta dasu ko? To shikenan ai kuwa a yau zasu bar wajenta idan yaso se naga wanda zata sakw hanawa zuwa wani gurin, ki fitar da kwalayen da kika zuba a can dakin yanzu zan fita za’a kawo sababbin gadaje a saka musu tunda ta kwashe wadancan, Amna da Farida kuma se su zauna a dakin ki kafin zuwa na samu wasu kudin suma a gyara musu dakin su” ya fada a mugun fusace ya wuce dakinsa dakko Atm dan ya manta ma dazun daze fita be dauka ba.

Har yakai bakin qofar Amirah data miqe tsaye tace “cabdi wadanne yaran ne zasu dawo gidan nan ni nace maka zan riqe maka yaya ne ko yaya? Harda ma wasu in basu dakina su zauna wallahi baze yuwu ba babu dan wanda zan riqe ehe”.

“Idan sunzo seki kore su kinji ko tunda baki da hankali ni zan koya miki har in fadi magana ki tsaya a gabana kina cewa ba za’ayi ba to ki jira na fito na tarar da ke anan gurin wawiya kawai” ya shige dakin ransa idan yayi dubu ya baci.

Me matan nan suka dauke shi ma? Ita waccen ta hana masa Yara zuwa gidan sa ita kuma wannan tana cewa baza su zauna a gidan ba, to ze gani idan gidan ubanta ne seta hana su ita kuma Ma’u ze kwace yaransa yaga in akwai abinda zata iya yi akai.

Sanda Ya fito Amirah ta shige dakinta dan haka yaja qwafa ya fita, yaso ya tarar da ita wallahi da se jikinta ya gaya mata tunda yaga alamar ita se an taba lafiyarta sannan take nutsuwa idan banda ma rashin kunya shi a matsayinsa Amirah zata kalla ya fadi abu tace bazatayi ba? Illar auran qaramar yarinyar kenan yarinyar da aka haifa akan idonsa ya raineta a gidansa da auran wuri ma yayi yasan tsaf se haifi kamarta amma yanzu tunda taga makwancinsa shiyasa take iya tsayawa a gabansa tana masa fitsara zeyi maganinta kuwa.

Amirah kuwa Dakin ta ta shiga, a fusace ta danna kiran Addah tana daga wayar kuwa ta saka mata kuka tana gaya mata yanda akayi.

“Kayyasan nan to ke me kika ce masa yanzu” Addah ta bada daga daya bangaren,

“Me zance masa kuwa Addah na gaya masa wallahi babu dan da zan riqe shine wai idan gidan uban wani ne se na hanasu zama ya gani”.

“Kina jina ko, lalabashi kuje a hakan zuwa musan abinyi dan ba mutunchi ne dashi ba kar muje ya sako mun ke kamar yanda ya saki uwarsu. Suzo din kisan mummuqe zaki musu a gabansa ki nuna kina son su a bayan idonsa kici ubansu yanda da kansu zasu gudu kinga qarshe se kefin ya koma kan uwarsu yace ita ce ta kitsa musu mugun abu” haka Addah tayi ta lallaba ta dakyar ta sauka ta yarda zata bashi haquri idan ya dawo ta kuma karbi yaran idan yaso a hankali ta gasa musu aya a hannu yanda zasu gudu da qafarsu su bar mata gidan.

Kafin ya dawo kuwa an kawo gado, haka ta danne baqin cikinta ta tsaya suka saka kayan harda wallpaper aka chanza musu masu suka gama suka tafi ta dawo palour ta zauna tana jiran taga shigowarsa da yaran tana nan zaune kuwa se gasu daya bayan daya suna shigowa kowa fuska jiqe da hawaye.

Muryar Bashir da tajiyo daga waje alamar shima yana dab da shigowa ya saka ta tashi ta taro Yan biyu tana cewa

“Meyasa kuke kuka da nan da gidan Mami ai duk daya ne kuje fa kuga yanda aka gyara muku dakin ku yayi kyau sosai”.

“Karki sakw tabasu kuma babu ruwanki damu a gidan nan kiyi harkar ki muyi tamu in ba haka ba kuma zaki sani” Aliyu ya fada yana fizge su daga hannunta kafin ya wuce dasu dakinsu yana sake balla mata harara Amirah kuwa da kallo ta bisu kawai baki bude, badan Bashir na waje babu abinda ze hana taci uwar yaron nan yau amma ai suna hade, Bashir din zeyi nisane wallahi seta koya masa hankali.

Kowa tayi ta zauna sega Bashir kaman wanda aka wullo, kallo daya yayi mata, yaso ace ta ci gaba da tata fitsarar ya ida saita mata nata hankalin tunda ya gama da Ma’u amma sabanin haka se yaga ta miqe tana murmushi tace

“Yara sun shigo suna kuka, ina ta lallashin su ma suka wuceni suka shige daki. Kaje ka lallabasu dan Allah badadi yaro ya ringa kuka”.

Wuce ta yayi ya shiga dakin nasu, suna nan har sannan sun hada kai suna kuka musamman Faridah da take ita kadai yau Babu Yah Amnah, Aliyu dai yana tsaye yana huci dan a fusace ya waiwaya da aka bude qofar ya zata Amirah ce ganin Bashir se ya mayar da kai gefe yana ci gaba da lissafi a ransa.

Bashir kuwa tsayawa yayi, seda ya irgasu kamar wasu yayan kaji kafin ya sake fita fuu kamar iska ya tafi gidan Ma’u, yayi Sa’a qofar a bude take dan tunda suka fita tana zaune tana kuka Ita da Amnah Anty kuma tana zazzaga mata masifa dan ta gaji da lallashin se ganinsa kawai sukayi ya fado yana cewa

“Ina Amnah? Nace ki tattara mun yarana shine zaki rage wasu akan wane dalili ke wuce mu tafi” ya qarasa yana kama hannun Amnah da tunda ya shigo ta miqe, tundazun taso ta bisu amma kukan da taga Mamin nayi ya sakata tsayawa daman jira takeyi idan tayi shiru se ta tafi daga baya.

ASMA’U

Toshe kunnena nayi naqi jin lallashin da Anty takeyi mun dan kuwa ba abinda zata fada mun tunda taqi hanawa Bashir ya kwashe mun yara, kuka nakeyi haiqan, daman ba wai na gama mantawa da abinda ya faru bane Aa kawai dai na bawa kaina haquri ne na dangana shine yanzu za’a sakeyi mun fami.

Bashir ya rabani da aure na, ya kuma rabani da yarana sannan kuma ace nayi haquri wai na dena kuka ai wannan zance ma be taso ba babu wanda ze fahimci halin da nake ciki se wanda masoyi ya tabayi masa yankan qauna a rayuwa.

Shigowar da Bashir yayi ban ko daga kai na kalle shi ba seda naji yaja maganar Amna tazo su tafi kafin na dago fuskata data jiqe da hawaye tayi jajir na kalle shi nace

“Ina tunanin abinda ka fara sha Bashir yana gaya maka qarya. Yaranka kace na baka kuma na baka, idan ka manta ne kuma bari na tuna maka Amnah ba yarka bace qanwata ce babu kuma abinda ka hada da ita dan zama na takeyi a gidan ka yanzu kuwa bata abinda ta manta a gidan ballantana ta koma su dai da yake gidan Ubansu gasu can an baka itama zata zauna a gidan da aka biya da kudin ubanta”.

Wani kallo ya watso mun da na kasa fassara kona menene idanunsa sunyi fici fice har wata kwallar masifa ce ta taru a acikinsu, nuna ni yayi da hannu yace “bani da lokacin ki yanzu dan ba gurinki nazo ba, idan kuma kin isa seki hanani tafiya da ita mu gani” ya fizgi Hannun Amna zasu fita na jawo ta baya da qarfi har seda ta fizge daga hannunsa kafin na daka mata tsawa nace

“Wuce ciki, kai kuma ka fita idan ba haka ba wallahi se nayi maka abinda harka mutu bazaka taba mantawa dani ba. Maganar lokaci kuma har abada karka tabayin lokaci na Bashir saboda a sanda kake tunanin kayi lokacin nawa kafin nan ni kuma nayi maka nisa tamkar tazarar sama da qasa sedai kallo.

Daga yau ka dauka cewa bamu taba hada komai da kai a rayuwa ba Bashir, aure ne dai ya qare a tsakanin mu yara kuma da suka hada To gasu nan kaje ka kwada su ka cinye duk tsiya dai baka isa ka canza musu wata uwar ba Asma’un nan dai tana nan a matsayin uwarsu”

Na dakata na share hawayen fuskata kafin na cigaba da cewa
“Daga yau idan Anyi duniya dan manzon Allah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login