Showing 237001 words to 240000 words out of 260321 words
Chapter 80 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
sa hakayaga Yusuf ya qyale dan kwana yayi yana sallahda tasbihi na nuna godiyarsa ga Allah bisa cika masa wannan babban buri na rayuwarsa, gani yake ko Yanzu ya mutu ya samu farin cikin da ya dade yana kwadayi. Ma'u ta amsa soyayarsa ta yarda dashi a matsayin Mijin da zata aura.
Qarfe Sha biyu na washe garin ranar ta kafa tarihin da ko a hasase be taba hasko faruwarsa a rayuwarsa ba. Suna zaune gaban shugaban qasa a lokacin, tattaunawa ce me matuqar muhimmanci sukeyi saboda yana cikin kwamitin tsaro na qasa gaba daya hankalin sa rabi ne akan tattaunawar da sukeyi inda ya kasa rabin a jiran tsammanin sakamakoj neman auran da aka tafi masa.
Kunnensa maqale da Bluetooth yana sauraran duk abinda yake faruwa acan Kumo gidan Baffa Isiya saboda seda ya jaddadawa Qaninsa da aka tafi dashi akan suna zuwa ya kirashi a waya yana so yaji duk abinda akayi karma suje suce a qara lokaci akan abinda ya gaya musu.
Sanda yaji an fara karanto Siga tsakanin Baba Sale Wakilinsa da Baffa Isiya wakilin Ma'u miqewa tsaye yayi cikin tsananin mamaki haka mutanen da suke zaune tare dashi gaba daya suka saka ido suna kallonsa dan dama tuni sun lura da hankalin sa baya kan abinda sukeyi.
Besan lokacin daya sulale yayi sujjada a inda yake ba ta godiya ga Allah lokacin dayaji wani da be shaida muryarsa ba yana jaddada dauruwar aure tsakanin Yusuf Sulaiman Wunti da Asma'u Abdullahi Tukur se gani akayi hawaye suna tsere akan fuskar sa, abin dariya abin takaici fuskarsa shabe shabe yana haqaye kuma yana dariya yake gaya musu abinda ya faru, nan da nan suka hau taya shi murna dan duk wanda yasan Yusuf yasan Asma'u, kai ko mace me sunanta ya hadu da ita se taci wannan darajar ya karramata.
Dole ya datse mitin ya fice suna ta tsokanarsa, ya ringa neman Layin Asma'u ya gagara samunta se ya mayar da Akalar kiran kan Alhaji Qarami suka hadu suna ta jimamai dan tuni Malam Kabiru ya kira ya zayyana masa dan shine ma Ummul aba'isin da suka sake fanfa Baffa Isiya akan a daura kawai to me za'a jira.
"Wato Yaya nasan halin Asma'u sarai shaqiyyar yarinya ce, wato ainihin dazu da safe ta kirani. Daga muryarta na fahimci ta kira tayi mun shaqiyancin nata ne se na yi kamar ban gane ba, tana ta wani hanya hanya ainihin danaga zata batamun lokaci kawai nace mata muna Kumo ai gashi ma har baqin sun iso ainihin idan sun tafi zan kirata alhalin a lukacin ma ina shan Shayi ne da Kubza ko shiryawa banyi ba" Bayanin da Yaya Kabiru yayi wa Alhaji Qarami kenan.
Duk yanda Yusuf yaso ya daure kasawa yayi dole ya yanki tikitin komawa Lagos na qarfe shidan yamma. baze iya ba yana buqatar ganin Ma'u a yau, ya rungumeta a jikinsa ya kirata da matarsa halalinsa aure ya bashi ita yanzu yana da dukkan wata cikakkiyar dama da iko a kanta wai dadi kashe shi shi Yusuf yau ya zama Angon Asmy.
Yana hanyar zuwa Airport Intee ta fado masa a rai, dafe kansa yayi, tun a daren jiya yaso ya shaida mata maganar auran da zeyi se gashi abubuwan sunzo a yanda babu wanda yayi zaton faruwarsu.
Lambarta ta America ya daddanna ya kira amma akace masa a kashe take, seda ya hadiye wani abu daya taso masa na bacin rai akan wannan dabi'ar ta Intee da sam bata dauke shi da qima ko mutunchi na Miji ba. Ya tabbatar da tafiya tayi wata qasar ba tareda ta nemi izininsa ba ko da yake abinda aka sabane ai, idan har ta gaya masa zataje wani guri to kudi ne bata dashi tana da buqatar ya bata.
Lambar mahaifiyarta ya nemo har ze danna ya tuna da a cikin watan nan da aka shiga akwai bikin qanwarta da suke uba daya da za'ayi a nan Nigeria zata iya yuwuwa sun taho bikin ma shine bashi da qimar da zata sanar masa seya canza akalar kiran zuwa lambarta ta Nigeria cikin Sa'a kuwa ta shiga.
Seda ta qaraci ringin ta katse ya sake kira dana dab da yankewa ta daga cikin muryar bacci tace
"Hello Sweet"
"Intee zaki taho Nigeria amma baki sanar dani ba me yasa kike..."
"Ai kaga halinka sweet qorafi qorafi baka da aikinyi kai se anyi maka laifi toh idan na gaya maka zanzo me zaka mun? Bana son takura ne nasan ina gaya maka zakazo ka fara damun mutum da jarabarka shiyasa ma ban neme kaba" Intee tayi saurin katse shi.
Shiru kawai yayi yana jinta, to meye ma baqo a cikin halinta ne wai shekara bakwai ai sun zama jiki sedai ya mata fatan shiriya idan tana da rabo, tunowa da abinda yasa ya kirata ya saka shi sakin wani murmushi a idonsa yana hango Asmynsa yana ayyana irin Albarkatun da ze diba a jikinta dan ko ba'a fada ba daga kallo kasan Asmy irin matan da Allah ya wadata su da komai ne ma'ana kyau na zahiri dana badini wanda ya same su sedai yai ta sujjada yana godewa Allah.
"Se mutum yayi magana ka fara fushi kuma, to jiya fa nazo ban taho da Asmy bane shi yasa ban kiraka ba kuma kaga hidimar biki zamu fara saura sati daya ina da buqatar na samu hutu saboda kwalliyata tayi kyau" Intee ta fada cikin shagwaba.
"Ba fushi nayi ba ai bakya laifi Yammata ya kamata kam ki huta kiyi kyau sosai kinji, dama ina so na gaya miki ne kin tuna maganar da mukayi kwanaki ko?"
"Wacce magana kasan nifa ban fita riqe abubuwa marasa muhimmanci da basu shafe ni ba"
"Hakane, toh maganar aure na da nayi miki" ya fada bayan daya ja numfashi yana jinjina halin matarsa a ransa
"Oh wai wannan maganar to ai tun lokacin ni na gaya maka bani da matsala da wannan kawai dai ka tabbata idan ka tashi auran ka samu classy mace wadda idan aka nunata aka ce mijin mu daya da ita bazan ji kunya ba kuma zata kulamu dakai dakayu sosai shine kawai ni damuwata"
"Intee kina sona kuwa?" Ya fada cikin tsananin mamakinta saboda be yarda ba duk sanda take gaya masa gashi yanzu ta sake maimaita wa anya yarinyar nan tasan abinda take yi ma kuwa
"Ina sonka mana Sweet me yasa kake tambaya?" Ta fada ba tareda damuwar komai ba.
"Babu komai, kin tuna Asma'u? Takwarar Asmy wadda kika kaita gurinta a Lagos?"
"Uhm bazan iya tunata ba saboda bata da ajin da zan tsaya na kalleta har na gane kamanninta" ta fada a yatsine. Murmushi yayi me sauti kafin yace
"Koh? Toh ita zan aura ko nace miki ita na aura dan yau akaje tambayar mun auranta se kawai aka daura auran gaba daya"
"Haka iyayenta suka gaji da ita lalai me yasa Nigerians kwata kwata basu da lissafi ne se kace ana neman kai da ita da kyanta da komai daga zuwa tambayar auranta kamar wata tsohuwa za'a bada ita babu jan aji gaskiya an cuceta wallahi" Intee ta fada ranta a sake babu alamar wai Mijinta ne yace mata ya qara aure balle abin ya dadata da qasa.
Dariya Ya fashe da ita jin wai babu jan aji babu komai aka bada ita cikin sigar tsokana yace mata
"Toh ai abin daga ni ne, idan kin manta na tuna miki kema fa kina ganina kika rikice kika cewa Dady idan bani ba se kin fada rijiya haka babu jan ajin babu komai aka bani ke toh itama yanzu kin gani aka bani ita"
"Koma dai mene ne zan koma bacci na, da kasan wannan maganar cema da text kayi mun kawai, Allah ya sanya Alkahiri ka gayawa Amarya ta kulamun dakai sosai, Ina sonka se anjima" tana hama fadar haka ta kashe wayar.
Murmushi ya ringa saki wato ta kowanne bangaren Intee babu abinda ya shafeta ita kanta kawai ta sani, tayi wanka tayi kwalliya yau tana wannN qasa gobe tana waccen shikenan abinda ta saka a gaba babu zancen wasu haqqoqin aure ballantana har ta zauna tana kishinsa to Allah ya kyauta.
Harya shiga jirgi yana ci gaba da gwada Layin Ma'u yanzu ko yana shiga dagawa ne batayi, jikinsa yaji yayi sanyi duk karsashin da ya taho dashi yayi qasa besan wace tarba ze samu a gurinta ba. Da amincewarta aka daura auran nan ko kuwa itama shammatarta akayi irin yanda abun yazo masa?
To koma dai yaya ne aure ya dauru ba saki ba yaji duk abinda zatayi sedai tayi amma ko duniya zata taru bega ubanda ze iya kashe auran nan ba.
Yana sauka a Lagos kai tsaye gidanta ya wuce dan daman Driver sa na Aiport yana jiransa. Tundaga qofar gidan yana iya jiyo hayaniya daga ciki sedai baya gane abinda ake cewa, kwankwasawa ya shigayi amma shiru ba'a bude ba se ya koma mota da sauri ya dakko wayarsa daya bari ya shiga kiran layinta cikin sa'a Yanzu ta daga.
BASHIR
Farkawa yayi ya ganshi akan gadon Asibiti ga ledar qarin ruwa da aka saka masa harta qare Jini ya fara tafiya, da sauri ya zareta dan shi kadai ne a dakin babu kowa, ya jura qafafunsa qasa da niyyar tashi yana yunqurawa Kansa ya sara yayi saurin komawa kan gadon yana dafe kan da hannu biyu.
"Sannu ka tashi kenan?" Wata siririyar nurse data shiga dakin ta fada cikin harshen turanci tana qarasawa kusa dashi, hannun sa ta kama ta duba taga ya cire ruwan seta mayar da hannunta kansa inda ya dafe tana cewa
"Kan yana ciwo ne? Ka kwanta tukunna na dubaka be kamata ka tashi zaune ba daman se jikinka ya qara daidaita".
Seda taje ta yaye labulen window haske ya ratso dakin abinda ya tabbatar masa da cewar safiya tayi kenan kafin ta dawo ta hau auna Bp dinsa dasu pulse duk tana yi tana rubutawa bayan ta gama ta kalle shi tace
"Har yanzu jininka be sauka ba Mr, ka kwanta bari baje na kira likita ina zuwa" ta juya zata fita. Dakyar ya bude bakinsa da yake jin kamar muryarsa ma ta tafi gaba daya yace mata
"Ina so nayi sallah"
"Kayi haquri yanzu likita zezo" taja qofa tayi waje abinta.
Kwanciya yayi kansa yana bala'in sara masa zuciyarsa kanta wani bugu take fat fat kamar zata fasa qirjinsa ta fito kai shi gaba daya ma dubiyar juya masa take, me yasa tunda ya rasa Ma'u ya rasa kwanciyar hankali a rayuwar sa ne shi.
Yana nan kwance har Nurse suka dawo tare da likita, Dattijone ya manyanta nan da nan ya rufe Bashir da fada dan sanda suka shigo ma gaba daya yayi zurfi a tunani Likitan nata yi masa magana sam be ji ba seda ya taba shi kafin yayi firgigit ya farka.
"Da girmanka da komai kake abu kamar wani qaramin yaro, ta yaya kake tunanin zaka samu lafiya bayan ana qoqarin ganin jininka ya sauka kuma kana qara saka kanka a tunani? Koma me yake damunka yanzu ai ajiye shi zakayi ka ji da lafiyar ka amma kana neman ka kashe kanka a banza da tunane tunane haha mutane ku ringa yiwa kanku fada mana".
Shidai Bashir yayi shiru har ya gama dube duben sa yacewa Nurse din ta kama shi ta kaishi qofar bandakin da yace ze shiga. A cukule yace musu ze iya, haka ya daure da bin bango ya shiga dan duk takun da yayi ji yake kamar ana kwada masa guduma a kai.
Seda yayi sallar Asubar da ta kufce masa dan lokacin kusan tara na safe kenan, yana zaune yana lazumi rabi kuma tunanin Ma'u yake da yanda zebi ya gyara kwabarsa. Amirah ce ta fado masa a rai da jaririnta yayi saurin shafa Addu'a ya miqe dakyar dan se yanzu ya tuna da batun suturar jaririn ma.
Da karfin hali da komai ya gama cike duk takaddu aka bashi gawar Babyn a Ambulance suka tafi gida dan ya rigada ya kira Limamin masallacin da suke sallah na cikin Estate dinsu.
Yanzu da a gida yake cikin yan uwansa da komai anyi shi a tsanake amma yanzu bashi me yi masa dole ya daure duk wani ciwo ya tafi yayi.
Se bayan da aka gama Jana'izar Babyn daya sakawa Muhammad Bashir kafin ya shiga gida dukda Asibiti ya kamata ya koma dan shi kadai yasan abinda yakeji a jikinsa bayan ciwon kai yanzu harda zazzabi ne yake neman kama shi.
Addah na zaune zuru a palour ya tura qofar ya shiga, da bala'in sauri ta tare shi tana cewa
"Yanzu Bashir daga fita tun jiya se yanzu zaka dawo ina Amirar? Tun jiya nake kiran wayoyinku a kashe gaba daya hankali na ya tashi har su Nafi na kira na gaya musu da tace Naziru ma ze taho a jiyan amma Babanku ya hana wai ai da babu Lafiya za'a sani
Na ganka kai kadai ina ita Amiran? Qila ma gantalinku kuka tafi kuka barni a gida kwal kamar mayya bayan kasan baqin halin yayanka ba kulani suke ba".
Kujera ya samu ya zauna dan baze iya tsayuwa ba kafin yace mata
"Tana Asibiti"
"Na shiga uku meya sameta? Badai wata matsalar bace kuma?" addah ta fada tana dafe qirji, se yai jim kafin yace mata
"Ki shirya, bari na watsa ruwa muje" ya daddafa ya qarasa dakinsa.
Da sauri Addah ta shige dakin da take ta dauko wayarta da mayafi ta dawo falo ta rafka tagumi jikinta har tsuma yakeyi. Tana nan zaune ta jiyo horn daga waje, har zata leqa sega Bashir ya fito daga dakinsa ita se sannan ma ta fahimci layi yake idan yana tafiya haka tabi bayansa suka fita bayan da yace ta kulle gidan suka hau motar sa da ya saka Samuel ya dauko suka koma Asibitin.
Sun tarar da Amirah na zaune suna yar hira da matar da take dayaj gadon da yake dakin da take. Tana ganin su ta takwarkwashe fuska ta saka kuka Addah tayi kanta da saurin gaske taba tambayar lafiya musamman da bataga cikin Amiran ba se wara ido take gefe da gefe tana neman jinjiri.
Bashir kuwa yana ganin ta fara kukan ya juya ya fice, bashi da buqatar qarin damuwa a yanzu. Dakin da aka kwantar dashi dazu ya koma, yana shiga suka ci karo da Likitan nan ya kuwa rufeshi da fada kamar ze kai masa bugu akan ina ya tafi? Wama ya bashi izinin tashi daga gadon da har ze kama hanya ya tafi wani guri.
Shidai haka ya koma ya kwanta, seda ya karya da Abincin Asibitin da sam babu dandano ko kadan kafin aka masa Allurai harda me saka bacci nan da nan kuwa yayi awon gaba dashi.
Qarfe Biyar na yamma aka basu sallama daga shi har Amiran dan babu abinda yake damunta sedai ta koma gida kuma ta cigaba da jego Allah ya bada rayayye a gaba.
Musa abokinsa daya biya duba shi bayan sun tashi daga aiki ne ya roqa daya kaishi gida saboda gujewa surutuan Addah da suka hau motar sa Samuel ya kaisu gida
tun data samu labarin mutuwar Jaririn fa take kuka da hawaye yanda kasan itace ma Amiran, Gombe kuwa babu lokon da labari be isa ba acewarta dukda an saki Ma'u baqin Asirin da tayiwa Amirah na karta haihu a gidan be karye ba ai kuwa duk inda zata shiga se taje ta nemo makarinsa sedai baqin ciki ya kashe ta amma Amirah seta haifi Yaya a gidan Bashir.
Suna shiga gidan ya wuce dakinsa, wayarsa da ya saka a Silent ya ciro daga Aljihunsa jin tanaVibrating. Ya gane Lambar da ta kira dukda babu suna, Bala ne, da mamaki ya ringa kallon wayar rabon da suyi magana tun waccen ranar kusan wata nawa yanzu, lokaci daya wani bacin rai ya taso masa na tunawa da furucin Balan akan Ma'u se kawai ya ajiye wayar ya shiga cire rigar sa yana ayyana dalilin da ze sa Bala ya kirashi a yanzu bayan abinda ya faru har yana tunanin ze sake hada wata hulda dashi ne?
Alwala ya shiga ya dauro dan an kira sallar Magriba, seda ya saka jallabiyya a jikinsa kafin ya dauki wayar har ze zura a Aljihu yaga saqo akai daga lambar Balan, tsaki yaja ya fita daga dakin yana qoqarin goge saqon dan idan ma haquri yake bashi yayi ta banza dan shi dashi dai har Abada, har ya iya kallon fuskarsa yace idan da matar daya rabu da ita zata yarda daya aureta a matsayinsa na Amininsa ai wallahi in ba muqullin Aljanna bane a hannun Bala baya sake kula shi ba shima sedai idan shi kadai yake rabawa sannan.
Iqamar da yaji an tayar ta saka shi jefa wayar a Aljihu ba tareda ya goge saqon ba ya qara saurin tafiyarsa, a masallacin suka hadu dasu Aliyu, kallo daya yayi masa ya sunkuyar da kai shima be tsawwalla ba yana kallo suka fice daga masallacin dukda yana son magana da Aliyun, dole su chanza wani plan din tunda wannan ya rushe dan baze fa zuba ido yana ji yana gani ya rasa Ma'u ba.
Seda yayi sallar Isha kafin ya kamo hanyar gida, kiran sa akayi daga gidan abincinda yayo musu order ya daga ya qara yi musu kwantance yana kashewa saqon Bala daya bude dazu be kai ga gogewa ba ya dawo kan wayar.
"Ina tayaka baqin cikin yin wuf da tsohuwar matarka da akayi, gaskiya Bashir ka cika mara sa'a tunda har ka rasa mace Irin Asma'u"
Abinda aka rubuta a saqon kenan.
Wani tsaki yaja kamar ze tsinka harshensa ya goge saqon, ransa a bala'in ya shiga magana kamar wani sabon kamu yana cewa
"Wallahi Bala gamo na da kai baze yi kyau ba, saboda bala'i bazaka fita daga sabga ta ba ko shikenan Allah ya hadamu zaka maimaita abinda ka rubuta yanzu, nida Ma'u kuwa mutu ka raba sedai baqin ciki ya kashe duk me yinsa"
Ko gani dakyau baya yi ya haye kan step din qofar gidan sam be lura da Anty dake tsaye kamar wadda aka bawa aiki ba seda ta kira sunansa.
A dan firgice ya juya ya kalleta, fuskar ta a washe tana Murmushi me kama da dariya babu wannan hararar da take masa duk sanda suka hadu kamar zata rufe shi da duka