Showing 66001 words to 69000 words out of 260321 words
Chapter 23 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
nasan ba tunani ne dake ba tsaf za’a iya zugaki ace ki fita ai be sani ba kinga kuwa auranki ya mutu” yana gama fada ya juya ya fice yabar Amirah da baqin ciki ya cika mata ciki kamar tayi bindiga.
Dakinta ta shiga tana duba wani littafi da ta kwafe numbobinta a lokacin Ummi nata mata iskanci wai rashin aikin yi me sa hauka gashi yanzu ze mata rana. A garin neman littafin ta samo tsohon layin ta da ba sosai take amfani dashi ba, da murna ta saka tana Addu’a Allah yasa basu kulle shi ba ai kuwa tana gwada kira ya tafi amma babu kati seta loda katindaya siyo mata ranta fes ta samu numbobin harma da wasu masu amfani da bata dasu a wancan layin.
Ummi ta kira ta hadata da Addah, tiryantiryan Addah ta bata labarin yanda akayi anje an siyar da gida miliyan uku da dubu dari shida, an biya me Gwal kudinta Miliyan Daya da dubu dari tawkas da Arba’in dan seda ta kawo resit din sarqar aka je da warin dan kunne gurin masu gwal suka fadi nawa gram din sa yake sannan aka buga lissafi a gurin aka siyar da warin ma aka bawa Addah kudin.
Ragowar masu bashi ma tas seda Alhaji ya cire wa kowa aka biya dan abinda yai saura kuma ya riqe a hannun sa yace ze saka mata a kasuwa, ta qarasa tana cewa “Nayi baqin ciki amma dai hankali na ya kwanta da yanzu qila ina firzin, yanzu idan an kwana biyu kuma se muga yanda za’ayi ki maida abubuwan da aka lalata miki yanzu dai ki kwantar da kai ku shirya da Bashir dan a jikinsa zaki samu ni kuma zan nemo mana hanyar da zamu bi ta qarqashin qasa a samu komai daidai ba matsala”.
Sallama sukayi Addah na gaya mata kartazo gida yanzu ta bari se an kwana biyu tukunna se a sannan ta gaya mata yanda sukayi da Bashir.
“Ki rabu dashi, lambo zamu musu dagashi har uban naki zan nemo mana inda za’a tasar mana kansu dan shi kansa Alhajin shi ya siyi gidan sena san yanda na dawo da abuna amma yanzu muyi luf tukunna, zan turo miki Ummi seta taya ki zama. Waccen Magen yar kuma gara ki barta a Asibitin ma in aka dawo miki da ita qarin wahala ne” .
Da haka sukayi sallama ta dan ji dama dama tunda an kashe waccen babbar wutar.
LAGOS
Kusan kwanan zaune Bashir yayi dan farkawata biyu ina ganinsa ido biyu yana faman tunanin da ban san koh na menene ba, yo ina dalili haka kawai ze saka kansa a damuwa akan abinda yasan bame yuwuwa bane ba ma. Ko masallaci basu fita ba a gida sukayi sallah yana idarwa kuma ya koma ya kwanta, ganin haka yasa na fita na fara hadawa yara abin kari su kuma suna shirin makaranta.
Indomie na soya musu dan har na dakko doya Abdallah yace bazasu ci ba sauran ma suka amsa Aliyu daya baya cin soyayyar Indomin na soya masa kwai ya hada da Bread suka karya. Har suka gama ba Bashir ba labarin sa, se na miqe na shiga dakin dan in gaya masa sun shirya fa.
Yana zaune a gefen gadon ya dafe kansa da hannu biyu na shiga.
“Baban Ali lafiya dai baka shirya ba ga yara can suna jiranka” na fada ina zama a gefensa. Beyi magana ba ya tashi ya shiga Toilet minti kadan ya fito yana goge hannunsa da qaramin Towel, Rigar jikinsa ya cire ya dora Jallabiyya akan dogon wandon sannan ya dauki key da wayar sa ya fita yana cewa “kiyimun kunun gyada da kosai” ya sa kai ya fice.
“Ko ba kunun gyada da qosai” na fada a fili ina hararar qofar daya fita, gadon na shiga gyarawa, babu dattin komai a dakin dan haka na dauke robobin ruwan da muka sha da dare na fita dasu. Seda na jiqa wake wanda daman bayarwa nake da yawa a gyara a surfa mun se a shanya shi ya bushe idan na tashi amfani kawai jiqawa nake na markada. Na debi gyada da farar shinkafa suma na jiqa.
Palour na koma na gyara palour da Dining din tsaf na kunna turaren sannan na shiga wanka. Riga da Zani na saka na Atamfa na kashe dauri jelar kitson da aka mun two step sun zubo kan bayana. Juyi nayi a gaba mudubin nida kaina na burge kaina bare kuma Bashir ya ganni dukda ba cewa zeyi nayi kyau ba amma nasan har ransa ze yaba ai.
Seda na markada gyada da shinkafar na saka danyar citta da kanumfari dan kadan dan kar yayi baqi sannan sake wanke blander na zuba waken na markada shi da attaruhu da Albasa se yar tafarnuwa. Kunun na fara damawa bayan yayi kauri na zuba ruwan lemon tsami yayi fari tas gwanin sha’awa na juye a Flask ragowar kuma na zuba a Wani qaramin flask din da niyyar na kaiwa Anty idan na gama.
Ina ajiye Flask din kunun akan Dining Bashir ya shigo da sallama ciki ciki na amsa ina kallonsa tareda yi masa sannu da zuwa.
“Yanzu zakaci na siya qosan?” Na tambaye shi, se ya girgiza mun kai yana cewa bari nayi wanka tukunna ya shiga daki na bi bayansa.
Seda ya fara shafa mai bayan yayi wankan na fita na dora ma suya na yanka Albasa sannan na shiga buga qullina sosai bayan na saka kwai guda daya saboda ya qarawa qosan laushi, gishiri na saka da daskomiya dan kadan se Albasa dana yanka qanana na shiga suyar qosan, gaba daya kasko biyu da dan kadan nayi dan bashi da yawa, ina kwashe na qarshen na jiyo shi yana kira na sena kashe wutar na juye a Bowl na dakko na fita palour.
Yana zaune a Dining din ya saka Jeans blue da Farar Short sleeve a gabanta an rubuta “HANDSOME” na kalleshi da murmushi nace “handsome indeed”. Murmushin ya mayar mun na ajiye kwanon na jawo Babban Mug na tsiyaya masa kunun na saka Sugar yace na saka masa Madara a raina nace “sarkin son dadi” na gama na tura masa komai gabansa harna zauna na tuna da kunun Anty sena miqe ina cewa
“Bari na kaiwa Anty kunun nan”.
A bakin qofa na miqa mata na juyo duk yanda ta keta magiyar na shiga amma naqi dan nasan in muka zauna qilan se Bashir ya biyo baya. Bayan na koma zama nayi nima na zuba kunun ina juyawa na kalle shi nace “Wai yau hutu ka samu ne bazaka office ba?”
Seda ya cinye qosan bakinsa kafin yace “Eh zamuje fieldwork ne Delta so an banu kwana biyu mu shirya”
“Toh Allah ya taimaka” na fada naja kununa da qosai na fara ci. Ya rigani tashi daga wurin nima ina qarasawa na kwashe komai naje Kitchen na ajiye dan na gaji gaskiya tun asuba idan na huta anjima na wanke su.
Kan Three sitter na kwanta ina cewa “wash na gaji wallahi anya bazan nemi me aiki ba”
Hankalin sa nakan Tv ya ce mun “idan da takura se ki nema din ai amma bame kwana ba”
“Nima ai bana son me kwanan, abinda yasa ma ban damu dame aikin ba kaga ba wuni muke a gidan ba zaman gaba daya weekend ai” na fada ina gyara kwanciya ta yanda zan kalli TV dakyau.
“Hakane” ya fada, se ya juyo yana kallona kuma yace “me kika yanke akan maganar mu?”
Kallon rashin fahimta na masa, ya gane hakan se yace “maganar da mukayi jiya da daddare nake nufi kin gama shawara?”
Na gano me yake nufi se nayi murmushi nace “Wai maganar Iman? To tunanin me zanyi ai tun jiya na gaya maka amsata ko” na fada ina kafe shi da ido kamar yanda yake kallo na shima, se ya sauke numfashi ya dan zamo gaba yana hade hannyensa guri daya yace
“look Ma’u Alfarma zakiyi mun ki karbi yarinyar nan, kinsan uwarta sarai ba wai nutsuwa ce da ita ba bare har ta iya kulawa da wani halayenta duk se a hankali. Yarinyar nan mace ce karta tashi taga abinda takeyi ta dauka daidai ne, bana so ta tashi daban da yan uwanta ina so ta samu kula da tarbiyya irin daya....”
“Anzo dai dai gurin” na raya a raina ina sheqa murmushi, tashi nayi dakyau na zauna kafin nace
“Wai tsaya Baban Ali, da baka yarda da tarbiyyar ta ba ka aureta har ka hada zuri’a da ita”, se ya watsa hannu ya koma cikin kujerar sosai kafin ya juyar da kai gefe daya yace “ba haka nake nufi ba, beside Amirah ai tarbiyyar kice itama kawai.....”
“To ai ka gama magana, tarbiyya tace kaga zata koyar da ita harda qari ma ko, sannan idan ma wani hali ne da ita na daban da baka so yarinyar ka ta dauka ai aikin gama ya gama tunda har ta dauki cikinta jininsu ya gauraya ta haifeta sannan tasha Nononta duk wani halayya kuma ai ta gama diba sedai ai fatan na kirkin su rinjayi na banza ko?”
Zancen gaskiya ka bar mata yarta, nasan ma duk wannan maganar da kake bata sani ba dan bazata yarda ba itama. Babu uwar da tana ji tana gani za’a rabata da yarta hakanan ba wata gagarumar jinya ba ko mutuwa kai ko mahaukata se anyi da gaske ake iya raba su da Yayan su bare ita yar tilo haihuwar farko ko nicefa bazan baka ba.
Idan Dan rashin lafiyar ta ne Allah ya hore maka ai ka barta a Asibiti suyi ta kula da ita har zuwa sanda suke ganin tayi kwarin da zata juri ko wanne kalar yana yi amma ba maganar ka bani ita, nawa ma idan za’a ragi wasu aciki bayarwa zanyi”.
Shiru yai yana kallona harna dasa aya ina sake turo dankwalina gaban goshi, ajiyar zuciya yayi kafin yace “yanzu dai bazaki karba ba kenan?”
“Allah me iko, da Hausa fa nayi maka jawabi dalla dallah amma kake sake tambaya ta kuma?”
“Eh saboda kinsan ni bana son dogon surutu, amsa daya nake buqata Eh ko Aa kawai” ya fada a dan hasale alamar ya fara barin cool site dinsa ze koma Bashir dinsa na gaskiya, se kuwa na tura baki gaba nace “Toh a taqaice dai bazan karba ba”.
“Shikenan, amma ina da ikon da zan kawota cikin gidan nan ko tunda gida nane” ya fada yana miqewa, nima sena miqe tsaye jin wani qundumemen rainin wayo,
“Tabbas gidanka ne ka isa ka dakko kowa nene ka kawo shi ciki, zaka iya kawo ta tunda itama gidan ubanta ne ai se ka hado dame kular maka da ita, ko kuma kai zaka aje aikin ka ka zauna rainon duk ba matsala ta bace ni” na fada ina dauke kai gefe, ina jin yanda yake qare mun kallo kafin yaja tsaki tareda sakin kwafa ya shige daki na rakashi da harara ina cewa a fili
“Wallahi ba tsaki ba kome zakayi sedai kayi, bazan karbi raino ba, rainon ma yar Amirah yarinyar da duk zamana da ita idan dana ze tsaga guri saboda kuka bazata dauke shi ba balle aje ga tsarkin kashi ko wanka shine ni ga jaka yanzu ta haifa za’a dakko a kawo mun in riqe mata toh ko daga turu aka kuntota qarewar rashin nutsuwa sedai duk handa za’ayi ayi”. Tsaf nasan yaji ni dan da qarfi nayi saboda yajin, na koma kan kujera na zauna, se kuma na miqe na dakko wayata na dokawa Dadar su kira dan fa karma inji wata magana daga baya.
Ringing biyu ta dauki wayar, a taqaice na gaisheta ta amsa kafin na shiga koro mata jawabin yanda mukayi da Bashir, na rufe da cewa “Iya gaskiya ta na fada ko bana aiki bazan riqe mata ya ba kowa ya kula da nasa Allah ya taya masa, idan kuma Ya dage akan hakan to sedai na bar masa nawa nima ya nemo wadda zata riqe masa su ni intafi”. Shiru Dada tayi har na kai qarshe sannan ta numfasa tace
“Ya kirani ya gayamun kuma na gaya masa wannan ba me yuwa bane, todai yanzu duk se hankalin ku ya kwanta tunda Allah ma ya raba muku gardamar ya karbi abarsa, se kowa yayi haquri ya maida wuqar” Dadan ta fada cikin sanyin murya,
“Hasbunallahu wani’imal wakeel, ta rasu jikin ne ya sake tashi?” Na tambayeta a rude dan maganar ta dake ni dagaske, “ta rasu yanzu Likitan ya kira Naziru yake gaya masa lafiya lau dan yau sukayi niyyar sallamarta ma har an yi mata wanka ma sun bata madara tayi bacci to daga baccin ne kuma bata farka ba”.
“Allah yasa me ceto ce, ya musanya mana da wadda tafi ta Alkahiri” Na fada a sanyaya tareda sauke wayar daga kunne na, ina dagowa muka hada ido da Bashir daya fito kamar wanda aka koro.
“Se ki zuba ruwa a qasa kisha, da baki karbeta ba ta mutu” ya fada yana jifana da wani irin kallo kamar ni na kashe masa ita. Sena miqe na nufe shi ina cewa “karbarta ko akasin haka be isa ya chanza hukuncin Allah akanta ba tunda babu dayan mu daya halicceta ko kuma ranta yake hannunsa dan haka ko tana gidan nan tunda wa’adinta yayi dole ta mutu, in zuba ruwa a qasa nasha kuma bani zaka gayawa ba Uwarta da tai sanadinta can zakaje ka gayawa dan ita ta nuna a fili bata damu da ita ba” na wuce shi na shige dakina tareda banko qofa, in banda ma rainin hankali ji abinda fa yake cewa fa.
Ina ciki naji tashin motarsa alamar fita yayi a raina nace a sauka Lafiya Allah ya gani qilan zamanta ze iya zama fitina shiyasa Allah ya karbi abarsa, Har qarfe biyar ina dakin fito ba, gaba daya zuciyata a jagule take ga alhinin rasuwar Iman ga soki burutsun Bashir na sake kiran Dada nayi musu ta’aziyya ta cikin wayar ina iya jiyo kururuwar Amirah da muryoyin mutane wasu na tausarta wasu kuma suna mata fada akan kukan da takeyi.
Na tausaya mata harga Allah Kuka kam dole tayi shi wannan duka wani kan wani amma yata iya haka Allah ya tsara abinsa masu samari da yammata ma ake dauka bare ita jaririyar da ba dadewa tayi ba.
Har na miqe da niyyar zuwana dora abinci wani tunani yazo mun, ta yuwu fa Bashir ya tafi Gombe be gayamun ba ga yara a makaranta lokacin tashin su tuni ya wuce, Hijabi na na dauka da wayata na fita, bari naje na ari motar Anty na dakko su dan tawa tana gurin Service ba’a dawo da ita ba, ina kulle qofar gidan motar sa na tsayawa da yaran ya dakko su se na bude na koma ciki ina jiransu.
“Mami ina zakije” Abdallah ya fada bayan daya rungume ni, “Da zuwa zanyi na dakko ku na zata Abbi ya tafi Gombe” na fada ina kallon Bashir daya shigo a sanyaye kaman wanda aka sheqawa ruwan sanyi.
“Abbi yace Baby Iman ta rasu wai Mami” Farida ta fada fuskarta kaman zatayi kuka, sena riqo hannunta ina cewa “ta rasu Farida” kaman tana jira kuwa ta saka kuka tanacewa “kenan banida sister mace yanzu har fa na fadawa friends dina yau a school step mum din mu ta haifo mun baby sis”
“Dallah malama yi mana shiru, kina kallon yarinya kamar mage dama ai kinsan mutuwa zatayi kuma ai ma...”
“Shut up You are very stupid Aliyu” Bashir da yake shan ruwa a dispenser ya katse Aliyu cikin tsawar da harni seda na tsorata amma ko gezau yaron nan beyi ba sema ido daya zubawa uban suna kallon kallo kamar wasu zakaru.
“Zaka wuce daga nan ko sena zo na same ka wawan yaro har fada kake daman mutuwa zatayi kenan so kake ta mutu koh” Bashir din ya sake fada cikin bacin rai, se na saki hannun Farida da Abdallah na miqe da niyyar yin magana Aliyu ya rigani yana cewa
“Toh ni Abbi me nace kawai dan na fadi gaskiya wayace su jagwalgwalata sannan su sakata a sanyi ai dole ta mutu....” be rufe bakinsa ba Bashir ya dauke shi da mari da har seda gefen bakin sa ya fashe kafin ya fizgo shi ya hau dukansa.
Kuka yaran suka saka gaba daya ganin abinda be taba faruwa ba a gidan yau Bashir ne yake dukan Aliyu kamar wanda ya samu jaki, tsakiyar su na shiga ina qoqarin kwatar Aliyu da ko gezau sema cewa da yake yi
“Ai daman seda nace miki ki koreta daga gidan mu muguwa ce kika qi seda ta aure shi, gashi nan yanzu yafi son su akan mu tunda ta haifi yarinyar nan kina kallo yanda hankalinsa ya koma kanta komai ita har comapany da ze bude da sunan Farida ma ya chanza na gani sunanta ya saka, shi yasa kullum nayi sallah sena yi Addu’a Allah yasa ta mutu dan akan Abbi ze iya yin komai gashinan kuma kina gani”.
Bige bakinsa nayi ina fashewa da kukan nima dan na kasa tare dukan da Bashir yake masa shi kuma yaqiyin shiru nasan kalaman sa ne suke qara tunzurashi seda ya gaji dan kansa kafin ya kyale shi ya shige dakinsa ya banko qofar ya barmu muna rusa kuka kamar nan ne gidan mutuwar.
Wannan wane irin bala’ine, ni na kashe yarinyar ko Yara na da ze huce akan mu? Ai kuwa wallahi da sake zan dauki komai amma banda irin wannan dukan da kalaman da basu dace ba akan yarana.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)
Wattpad @MaryamahMrsAm
Page 25
Ina kuka ina gasawa Aliyu fuskarsa da ta kumbura sosai saboda marin daya sha a hannun Bashir, tausayin sa ya cikani tabbas be kyauta ba amma ai dukan yayi yawa, Yanda ya zage ya ringa dukansa kamar wanda yake dambe da sa’ansa.
Gaba daya yaran suna tsaye sunyi cirko cirko kowa fuska da hawaye kana kallonsu kasan a tsorace suke, bude qofar da Bashir yayi da qarfi yasa suka zabura kafin kace meye wannan sun maqalqaleni wani kan wani Jafar yana cewa “kice masa yayi