Showing 18001 words to 21000 words out of 260321 words
Chapter 7 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
Jallabiyya Baqa da tayi bala’in masa kyau duk da kasancewarsa ba fari qal ba, Bashir nada kyau irin na Maza me sanyi daya hadu da kwarjinin da Allah ya bashi.
“Kayi kyau Baban Ali” ta fada da zuciya daya dan ita bata iya munafunci irin nasa ba kuma rashin yabon kwalliyarta be taba sare mata guiwa akan ta denayi ba.
Kallon ta yayi yana dan Murmushi kafin yace “Koh?”
Seta amasa masa da sarar sa tace “Uhm” tana qoqarin kauce masa a ranta tana mita. A zaman shekara Goma sha shidda baza ta tuna ranar da a karan kan Bashir ya budi baki ya yabi kwalliyar ta ba tun tana qorafi idan tayi se ta tambayeshi tayi kyau sannan ze yaba har ta gaji ma ta dena, yanzu da yaranta suka girma kuwa indai tayi kwalliyarta se sunce Mami kinyi kyau shiyasa ma ta dena damuwa da yabawar Bashir dukda abun da zafi amma ya zakayi (Mazan hausawan Mu Allah ya shirye ku dai 🥺🥺).
Wuce shi tayi ta shiga dakinta itama ta daura Alwala shi kuma ya hada kan yaran suka fita. Data idar da sallah zama tayi ta qara gyara fuskarta dakyau sannan ta fito, sun zauna a Dining da gani ita suke jira dan haka ta qarasa gurin.
Seda tayi serving kowa sannan ta zauna suka fara cin abinci kowa na santi karma Bashir yaji labari dan kunnensa har motsi yake. Besan yawan abincin daya nada ba seda ya qara saka serving spoon ze debo abincin a karo na uku bayan wanda ta zuba masa yaji wayam aiko suka kwashe da dariya suna kallonsa. Seya bata fuska kamar yaro yace
“To ai yunwa nake ji for almost a week fa bamu ci abincin Mami ba, please Mami karki kuma tafiya ki barmu, we are so sorry mun ji jiki wallahi, we missed you alot”.
“Zobon da Asma’u ta kurba ne ya sarqe ta ba shiri ta watso shi tsabar yanda mamakin kalaman Bashir suka nemi kasheta a zaune.
“Bashir dai data sani ne yake wannan maganar?” Kai ita kam badan ciwo ba dadi ba da tace ta ringayi duk wata ko Allah ze saito mata Bashir zuwa abinda ta dade tana fata.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
Na Maryamah_Mrs AM(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)
Page 8
To Aka ce mata da Miji se Allah dan kuwa Ma’u da Basharin ta suna qulewa a daki sukai muqus aka shiga sharafin soyayya dan dama an dade ba’a hadu ba qarshe har makara tashi bacci sukayi. Safiyar ranar duk su biyun da ka kallesu zaka san suna cikin walwala.
Ta cancada kwalliyarta da skirt and blouse na Atamfa komai ya fito se juyi take tana saka kwakwalwar Bashir jijjiga. haka ta hada musu breakfast me rai da lafiya suka ci suka wuce makaranta dukda sam be so yau ta zama ranar aiki ba ya so ace suna gida yau yaci duniyar sa da tsinke ya more amma ba komai ai Gobe Friday zasu hadu.
Suna fita Qarasa yan abubuwan da suka rage mata tayi kafin ta shiga dakin ta ta kwanta dan huce gajiyar da Bashir ya tara mata, “Bashir is too good” ta ayyana aranta. Wato yasan ta yanda duk ze wanke laifinsa ta wannan fanni gwanin malami neda ta tabbatar samun irinsa se an tona.
Tana tsaka da tunanin shauqin daren jiyan ta jiyo qarar door bell da kuma ringing din wayarta. Wayar ta fara jawowa ta duba, Anty ce matar ogan Bashir dake Flat din da yake kallon nasu, seta miqe tareda daukan Qaramin mayafi dan dankwalin kanta ya zame.
A palour suka zube tare da Anty da ta farayiwa Asma’un tsiya tun daga qofa”
“Kai Ma’u kinga wani kyallin goshi da kike daga fitowa daga Asibiti har za’a maida wani kenan”. Daria Asma’u tayi tana cewa
“Haba dai ai na gama nikam wadan nan ma sun isa Allah ya raya mana sisi na kwai zan ci gaba dayi”
“Inafa kika gama kedai ki shirya dan qila wasu biyun ne a tafe”
“Ba amin ba Anty” ta tare Antyn.
Gaisawa sukayi kafin Antyn tace mata
“Shekaran jiya na dawo wlh se dare ma nashigo Honey yake cemun Ai kina Asibiti ba lafiya, har zamu zo jiya da magriba kuma yace sun hadu da Baban Aliyu a Masallaci ya ce masa kin dawo gida”
“Eh wallahi jiya da rana aka sallamoni ai gaskiya Anty kinsha gida kusan 3 weeks fa” Asma’u ta fada.
“Ki bari kedai zama nayi na huta nayi gyara sosai dan anan ba wani lokaci kake samu ka baje yanda kake so ba mutum na saka maka ido” cewar Anty tana bawa Asma’u hannu suka kashe
“Kai Anty a ringa tausayin Baba na dai karki qarasa mana tsohon mu”
“Ke barni fa dole na kwaci kaina sarai kin san Uwargida na bata wasa da gyara dole nima na zage kar a raina ni.
Hira suka shigayi Anty ta shiga fito da abubuwan da tayo wa Asma’u tsaraba tana cewa “Gashinan se a ci gaba da gashi ban ce ki raga masa ko na second daya ba atoh” suka tuntsure da dariya Asma’u tana cewa “Anty baki da dama”. Se wurin 12 sannan ta mata sallama ta tafi bayan ta rakata qofa ta dawo tana tattare kayan zuwa dakinta a ranta tana qara jin qaunar Antyn dan yanda ta dauketa take kula da ita kamar qanwarta da suka fito ciki daya.
Anty Suwaiba matar Engineer Abdullahi Gusau ce ogan Bashir.
Itace Matar sa ta biyu uwar gidan ta ma anan Lagos take da zama amma ba unguwarsu daya ba. Mace ce me tsananin kirki dukda ta dan girmi Asma’u amma yanda take mu’amalantarta kaman qawaye ko shaqiqan yaya da qanwa suke dan tunda suka fara haduwa jinin su ya hadu da Asma’un.
Ita kanta Asma’u tana ji da Antyn dan Ita tunda suka hadu rabon da tace ta siyi wani abun gyara da kudinta, a koda yaushe Anty cikin yo musu aike kaya gangariya daga Zamfara garinsu take kuma duk sanda Asma’u ta tambayeta nawane ta biya seta nuna bacin ranta. Ta kance da Asma’un
“Ni a qanwa na dauke ki, banida kowa a Lagos seke yanzu”.
Wasu daga cikin kayan ta fitar ta fara amfani dasu a ranta tana hasaso haduwarsu da Malam Bash dan tasan yau kam se tafi jiya Armashi. Kafin ta gama an kira sallar Azahar dan haka tayi alwala tayi sallar sannan ta kwanta zuwa La’asar kafin tasan abinda zata dafa musu kuma.
Couscous tayi musu da miyar hanta ganin lokaci ya qure, setayi marinating kifin da zata gasa musu su qara dashi zuwa can anjima kafin a kwanta. Yauma batayi wasa ba gurin cin kwalliya ta daukar magana dan har tafi ta Jiya. Wasu riga da skirt ta saka na kanti Oxblood da suka kama jikinta kamar tanayin nishi zasu yage. Bata daura dankwali ba ta faka dogon baqin gashinta daya sha gyara se qanshi yake yi kafin tabi kowanne lungu da saqo na jikinta ta shafe da hadaddun turarukanta da ita kadai tasan wadanda take mixing da duk bala’in kwakwkwafin mutum baze taba cankar wane turare bane.
Abaya ta fitar Baqa tareda mayafinta ta ajiye a gefe saboda yaranta maza ne, dukda qanana ne tana takatsantsan da irin shigar da zata fita gabansu da ita. Qugin motarsa data jiyo ya sakata saurin dora abayar ta yafa qaramin veil dinta akanta tareda zura slippers din ta ta nufi waje dan ta taro su.
Bashir
Fitowarsa daga mota yayi kyakykyawan gani, Ma’un sa ce kamar wata yar budurwar Balarabiya, tundaga nesa ya fara shaqar qamshin da takeyi wanda be taba jin sa a jikin wata mace ba bayan ita. Tamasa kyau yanda tayi rolling mayafin ya zagaye kyakykyawar fuskarta tareda bayyar da gaban gashinta daya ke nan luf a kwance ya qara qawata kwalliyar tata.
kallonta yake har besan sanda wayar hannunsa ta subuceba. Yana jin yanda yaran suke zuzuta kyan da tayi amma nasa bakin kamar wanda aka sakawa qaton kwado a ka kulle ya kasa koda budeshi se idanu daya zuba mata kawai.
Qarasawa gaban sa tayi ta durqusa tareda dakko masa wayar da ya yar bata miqa masa ba se jinta yayi gaba daya ta rungumoshi, saitin kunnensa ta furta “Welcome home SH (sweet heart)”. Kamar wanda ta tsoma a ruwan qanqara haka ya daskare a gurin yana jin kamar ya shide saboda muryarta da kuma numfashinta daya sauka a cikin kunnensa. Hannunsa ta kama ta zura masa wayar kafin ta juya tabarshi da shaqar qamshinta, batayi ko taku biyar ba taji an janyota ta baya yai mata wata kyakykyawar runguma tareda sauke mata kiss a gefen wuyanta da mayafi be ida rufewa ba.
Zaro ido tayi tana riqe hannunsa, “Baban Ali a waje fa muke” ta fada ganin gogan na neman kauce hanya 😂 se a sannan ya farga dan shifa a lokacin ita kadai yake gani se kuwa yaja hannunta qii suka shige cikin gidan dan tuni yaran suka kama gaban su. Mantawa yayi da batun wata yunwa da gajiya daya kwaso suka shige dakinsa kai tsaye , ai be ida birkicewa ba seda yai arba da ainihin kwalliyar Ma’unsa tuni labari ya chanza 🏃🏽♀️🏃🏽♀️.
Basu fito ba se qarfe goman dare, Babu kowa a palour alamar yaran harsun kwanta. Ma’u da duk tayi laushi ta nemi kujera ta zauna Bashir kuwa Dining ya wuce dan se yanzu yake jinsa kamar ze fadi saboda yunwa. Ya manta sam rabonsa da abinci tun na safe. A Babban plate ya juyo dukka abincin ya sakko da shi inda take ya ajiye sannan ya koma ya dakko kwanon Fish din da Amna ta gasa.
Yana ci yana bata a baki har suka cinye se wani tarairayarta yakeyi kamar kwai, yanda yake rawar jiki da ita se yake tuna mata da lokutan baya a sanda yana Bashir din Ma’u kafin zaman majalisa da sababbin abokai ya sauya mata shi zuwa wani mutum na daban. Tana tuna irin gata da tarairayar daya ringa nuna mata a shekarar farko ta aurensu. A lokacin ya kan sakata taji tamkar tafi kowacce mace dacen miji duk kuwa da bata samu yanda take so ta bangaren kayan more rayuwa ba amma soyayya da tattalinta da ya ringayi yafi mata komai dan dama ita ai dan soyayya ta aure shi bawai kudi ba.
Suna gama cin abincin dakin suka koma, ta gaji tibis dan haka ta haye gado ta kwanta yana matsa mata jikinta. Wayarsa ce tayi qara, a tare suka duba sunan Amira da ta gani yana yawo yasa ta dauke kanta. Satar kallonta yayi karaf kuwa suka hada ido, haka kawai yaji wani abu kamar nauyin Asma’u ya kamashi cikin son basar wa ya dauke idonsa ba tareda ya amsa wayar ba.
Kiran da ya yanke wani ya sake shigowa ya sakata cewa “ka daga mana ba kiranka akeyi ba” seya dauki wayar, be zauna anan ba ya fita falo. Da kallo ta bishi tana qoqarin hana shedan yin tasiri akanta “Itama matarsa ce matsayinmu daya da ita” ta fadawa kanta sejin hawaye kawai tayi suna bin fuskarta.
Bata san randa zata dena jin zafin yankan bayan da suka mata ba. Da ace wata can Bashir ya aura koda cikin dangin nasa ne damuwarta bazata kai haka ba amma fa Amirah, Amirah data dauka tamkar Amna. Yarinyar da ta gama sanin sirrinta ciki da waje ita ya auro mata a matsayin kishiya se kawai ta rushe da kukan takaicin da duk sanda ta tuna yanda auran Bashir ya kasance seta yi shi.
Babu wanda ze gane zafin da takeji se wadda aka kwatantawa irin abinda akai mata, se yanzu take ganin dalilin da yake saka wasu matan aikata abubuwa da dama akan kishiya ko ma mijin kansa dan wallahi in akayi maka wani abun in ba me qarfin imani da tawallaki ba se kaji kamar bazaka yarda ba se ka dauki mataki. Har bacci ya dauketa Bashir be shigo ba se Asuba ta farka ta ganshi a bayanta.
Ko a fuska bata nuna masa komai tayi sallah a dakin sannan ta fita gurin yara dan jiya basu samu ko yin magana ba. Seda ta hada musu abinci suka shirya tareda zama suka fara breakfast sannan ta koma dakin ganin Baban Ali be fito ba.
A tsaye ta ganshi yana zuge jakar da yake tafiya da ita Gombe, dauke kanta tayi kamar bata gani ba tana cewa”Sun shirya fa gasu can sun fara cin abinci basu jiraka ba” tayi gaba da niyyar shigewa toilet dan bata so yai mata maganar tafiyar sa sedai tun kafin ta shiga ta jiyo shi yana cewa
“Ke zaki dauko su daga school yau zan wuce Gombe ne daga office bazan dawo ta nan ba” ba tareda ta juyo ba tace masa “Allah ya tsare ka gaishe su” tai shigewarta abinta.
Bin kofar yayi da kallo kafin jiki a sanyaye ya dauki Laptop bag dinsa da jakar kayan ya fita, seda ya kaisu mota sannan ya dawo shima ya hau Dining din amma se ya kasa taba komai.
Shiru yayi yana kallon yaran suna cin abincinsu har suka gama Ahmad ya kalleshi yace “Abbi ina Mami zamu tafi”
“Kuje mu tafi wanka take yi” ya fada yana miqewa. Har sun fita ya juyo zuwa cikin gidan, Bayaso su rabu da bacin rai kodan albarkacin farin cikin data bashi a kwana biyun nan. Harya kama Handle din dakin shegiyar zuciyar da take masa famfo ta zugo shi “to me kayi da zaka ke bata haquri ma?” Zuciyar ta raya masa, Seya saki qofar ya juya kawai.
Asma’u da ke zaune tana jiran tsammanin zuwan Bashir ya rarrasheta, ajiyar zuciya ta sauke jin an taba qofa harda qara narke fuska tana ayyana abinda zatayi ta gigitashi se taji shiru, the next thing ko se jin tashin motarsa tayi ta yaye window da sauri har sun wuce se qurar daya tayar, baki bude take kallon motar harya qule mata, “Hmmm” ta sauke numfashi kawai ta shiga shafa mai, bataso ta tuna abun ma bare ranta ya baci ita dai addu’arta idan Bashir nada rabon ganewa to Allah ya maido shi kan hanya.
Gombe gidan Addah
A daren ranar da Bashir ya turo musu da kudi tayi ta kiran Number da Malam Wizy ya basu bata samu ba, bata haqura ba tayita gwada Number har washe gari amma shiru gashi ta kira wayar Hajia Balaraba ma a kashe.
Jikinta dabe gama warwarewa bane ya hanata fita ta bari akan zuwa talata tasan ta warke seta je gidan Hajia Balaraban ta dai ci gaba da kiran wayar tasa ko zata samu cikin Sa’a kuwa ranar Laraba da safe tana kira ta shiga.
Ta gama ringing ba’a dauka ba seda ta sake kira aka daga. Muryar wata tsohuwa taji daga ji taji duniya har ta gaji tana cewa “kai ku duba nan waye ya bugo, Wizy da qaninsa Iliya suna zaune a dakin Kakarsu daidai lokacin sunzo gaishe ta, miqa wa Wizy wayar tsohuwa tayi tana sake cewa ya duba ga gani.
Sallama Adda ta sakeyi, fes Wizy ya gane muryarta se yai saurin datse kiran ya miqe yana cewa Kaka yana zuwa.
Can wani lungu ya buya yayi recharging wayar kaka ya dannanwa Adda kira.
“Salamu alaikum malam ina wuni” ta fada cike da zumudi
“Lafiya lau dawa nake magana” ya tambaya irin be gane ta din nan ba
“Nice Malam wadda Sani ya kawo mu (sunan da Me Napep ya gaya musu kenan)
“To to hajia ya gida naji ki shiru da alama buqata ta fara biya kenan”
“Wallahi malam na danyi rashin lafiya ne kwana biyu kuma na kikkiraka ma wayar a kashe” Addah ta fada
“Eh wallahi kwana biyu kam na kashe waya dan na shiga halwa ne inata ayyukan ku dafatan ana ganin haske ko”
“Sosai kuwa Malam ya fara samuwa”
“To haka ake so yanzu to ya akayi?” Ya sake tambayarta.
“Dama na samu wasu kudin ne nace bari na turo a ci gaba da aikin mu sameshi gaba daya”
“Kin kyauta kuwa ai ina tabbatar miki idan aiki ya kammala hajia nasan indai kin riqe amana har ni dinnan se kin mun kyautar kujerar hajji” Wizy ya fada yana tsallen murna jin wata banzar zata fado.
“Insha Allahu kuwa malam yanzu dai ka bada akawun a tura kudin nan ayi a ci gaba”
“Ba matsala da mun aje waya zan turo miki” sukayi sallama yana qara karanta mata qanzon kurege.
Harya fara typing account details dinsa wani tunani ya kawo kansa, idan ta tashi fa za’a Iya tracing dinsa ta banki, se yai saurin gogewa ya danna mata kira. Tana dagawa yace
“Hajia nace kudinnan ki cire su, akwai yaro da na aika qauye ya siyo ragunan wasu aiki bari naji in be tafi ba se ya biyo ya karba kawai ya wuce” da haka sukayi sallama.
Minti kadan ya sake kiranta yace ze turo yaro, nan ta zayyana masa Address ashe ma basu da nisa ya ma gane gidan daya daga cikin yaran mijinta abokinsa ne. Isma’il me Napep ya dannawa waya suka tafi tareda wani qaninsa me suna Nasiru da yai shigar me zuwa kasuwar qauye. Ko kafin su Iso Adda ta aika Ummi an ciro mata 80k kudin rago biyu yaro na zuwa ya shiga har palour ta ta bashi kudi ya jefa a buhu ya fice.
Gaba suka qara aka tsaya kowa aka bashi rabonsa ya zuba a Aljihu Malam Wizy ya zare sim din Kaka ya ballashi biyu ya zubar yana cewa “mun tatseta ya isa haka” suka sheqe da dariya.
To Addah Allah ya maida Alkahiri ya kiyaye na gaba 🤷🏽♀️🤷🏽♀️🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
Na Maryamah_Mrs AM (Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)
Page 9
Gombe
Ana kiran magriba Bashir ya shiga gidan sa na Gombe, tun qarfe hudu da rabi suka sauka tazarar tafiyar daga Akko zuwa Gombe ta kaishi Magriba.
A qofar gidansa Me Taxi din daya dauko shata daga Airport ya sauke shi ya fito dakyar yana jan qafa ga yunwa ga gajia tiqis saboda yau yasha aiki a office ga kuma tafiya dukda a jirgine.
Yana qoqarin bude get din a ransa yana ayya Allah yasa ma ta dawo gidan dan yana daga ciki rashin sanin ya kamatan Amirah a duk sanda zezo hankalin ta be taba gaya mata tazo ta gyara gida tayi girki dan tarbarsa ba se in ya tuna mata. Dama can tun tana yarinya yasan qazama ce ta gaske