Showing 162001 words to 165000 words out of 260321 words
Chapter 55 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL
ka nemar mata gurin kwana, haka kawai banida sirri nida dakina" Amirah ta fada cikin qunquni tana hararar Farida data tafi dakinta, wucewa Bashir yayi ciki tabi bayansa tun kafin ta zauna ya juyo a mugun fusace yana cewa
"Wannan ya zama karo na qarshe da zaki sake gaya mun magana a gaban yayana, sannan ke kike zamana ko ni nake zamanki dan Saboda baki da tarbiyya zaki kalleni kice ban isa nayi abu ba, so kike ki qure ni ko Amirah? Bazaki ji dadin abinda zan miki ba wallahi ki bar ganin ina daga miki qafa, ranar dana waiwayo kanki bazaki ji da dadi ba"
"To nima a dena yimun abinda bana so indai ana son zaman lafiya" ta fada ba tareda ta kalle shi ba, da mamaki ya ke kallonta, kallon wai daman haka take ko kuwa yanzu ne tazama hakan.
A da dai duk rashin kunyarta bata tsayawa a gabansa ymta gaya masa magana sedai taqi bin umarninsa amma yanzu a gabansa qiri qiri yana fada tana fada bata ko shakkarsa yaushe suka fara haka.
Gani yayi idan ya biye mata qarshe ze iya lakada mata dukan da zata kasa tashi se kawai ya haye gado ya barta a tsaye tana ci gaba da qananun mita, har kansa yaja bargo, yana jinta ta kashe fitilar ta hau kan gadon tana matsawa jikinsa ya tureta yana cewa
"Kika sake tabani sena kwada miki mari wallahi, saboda bakida kunya ki gama zagina sannan kizo kusadani dallah matsa can kafin na make ki"
"Allah dai yana kallo idan kuma aka take mun haqqina ba yafewa zanyi ba ehe" ta fada tana murguda baki kafin ta sauka daga gadon ta koma kan kujera.
Zaune Bashir ya tashi shima ya zuba mata ido kawai yana kallonta amma taqi bari su hada ido, shi tayi wa Allah ya isa? Shi Amirah ta ke zagi harda Allah ya isa
Wani irin tuquqi zuciyarsa ta shiga yi masa idonsa ya kada yayi jajir kamar wuta, cikin kakkausar muryar da seda ta bata tsoro yace mata
"Fita daga dakinan, idan kika bari nazo inda kike sena illataki Amirah, kuma wallahi ko tashin Faridah kikaje kikayi daga bacci yanzu se nayi miki dukan da na lahira seya fiki jin dadi wawuya mara hankali kawai".
Da sauri ta fice, a palour tayi kwanciyarta ko banza dukkan su zasuyi kwanan baqin ciki, yanda ya bata mata itama tayi masa fiye da haka ai su zuba su gani ita da shi za'a ga wanda ze gaji tunda tagane duk abin nasa ma hargagin qarya ne.
Bashir kuwa kasa kwanciya yayi sya shiga safa da marwa a dakin, Allah sarki Ma'u a zaman sa da ita baze taba cewa ga ranar data zageshi ko ta gaya masa maganar da zata sosa masa rai haka kawai ba.
Iya qarshen ladabi da biyayya tayi masa amma ya raina abinda takeyi yake ganin kamar bata girmana shi irin yanda ya kamata qarsheya saketa a dalilin wata, watan da gata nan tun ba'aje ko ina ba ta fara tsayawa a gabansa taba qare masa tanadi tabbas kuwa dole ya dauki mataki akan hakan, ya hukunta wadda batayi masa laifin komai ba balle ita data siya da kudinta dan haka ta shirya karbar sakamako daidai da abinda ta aikata masa.
Washe gari ta kama Juma'a tun asuba ya gayawa Amirah ta hada musu abin karyawa, yanayin yanda yayi magana ya saka bata musa masa ba ta dai bishi da harara daya fita tana idar da sallah ta hau firar dankalin kafin bakwai ta soya tas harda qwai ta dafa ruwan shayi.
Yana zaune a palour dan da wuri ya shirya ya fito tagama jera komai, yaga alamar saken daya bata ya saka raini shiga tsakaninsu a yanzu ne ze tabbatar mata da be chanza ba yana nan a Bashir dinsa data sani.
A daure yace mata taje ta kirawo yaran suzo su karya, suma kuma basu musa ba harda Aliyu duk suka zauna a Dining din kowa ya hada shayi, Aliyu ya turawa yan biyu farantin daya zuba musu dankali Ahmad na taunawa ya watsoshi waje yana cewa
"Kai kai muba haka Mami take yi mana ba".
Ahmad ya fada yana bata fuska, ai kuwa Amirah ta zaburo masa tana cewa
"Aa ba Mami ba uwar Mami ce ba haka takeyi muku ba shege me qaton kai"
"Se dai taki uwar Addah, kuma wallahi kika sake zagar mana uwa se mun hadu mun miki duka a gidan nan" Aliyu yayi wo kan ta kamar ze daketa a lokacin, seda ta ja baya gurin kujerar Bashir daya hada hannu biyu yana kallonsu kafin tace
"Ni zaka daka ashe zaka iya dukan uwarka Asma'u kuwa in dai zaka dake ni"
A mugun zuciye Aliyu yayi kanta kafin Bashir ya miqe har ya kai mata gula da qafa ta sunkuya ya sauke mata qafar a daidai kunne ai kuwa ta fasa qara ta zube a gurin be tsaya ba ya sake yin kanta amma kafin ya kai mata wani dukan Bashir ya tareshi tareda zabga masa mari.
"A gabana Aliyu zaka daki matata?"
"Ai a gaban naka ta zagi uwata kuma baka hanata, wallahi tunda ka saki uwarmu akanta itama bazata taba zama lafiya a gidan nan ba, ku tashi mu tafi" Aliyu ya fada babu ko dar a fuskar sa, ya kada qannensa waje suka fice suka bar Bashir da Amirah a gurin.
Amirah dake durqushe a qasa ta riqe gefen fuska tana kuka ta kalli Bashir tace
"Kana kallo sun tafi bayan ya kurmantar dani, wallahi bazan yarda ba se an bi mun haqqina"
"Dallah ki rufewa mutane baki, duk ba ke kika jawa kanki ba? Sau nawa zan gaya miki ki dena shiga sabgar sa a kan me zaki zagi uwarsu sa'arki ce? Sannan ai ba qarya Ahmad din yayi ba kin soyawa mutane abu salam babu ko digon gishiri tayaya ze cuwu, se ki tashi kije ki samu ruwan dumi ki gasa gurin idan da man zaitun ki tsiyayaqa kunnen gobe ma ki sake zagin musu uwa su sun san darajar ta" yana gama fada shima ya dauki jakarsa ya fice.
Yauma dai haka ya fita beci abinci ba shidai bashi da maraba da gauro yanzu gauron ma mara galihu.
A bakin motar ya hango su Asma'u tayi parking daidai gurin suna magana kafin ya qarasa taja motar ta ta wuce dan haka ya bude musu motar suka shiga, haka ya kaisu makaranta ya ajiye su sannan ya tafi ya siyo musu breakfast a wani gidan abinci kusa da gurin ya sake kai musu kafin ya wuce office dinsu zuciyarsa kamar zatayi bindiga saboda takaici.
AMIRAH
Suna fita ta tashi dakyar ta dakko wayar ta ta dannawa Addah kira, a speaker ta saka dan da gaske fa kunnenta yaji duka tana dagawa ta saka mata kuka tana cewa
"Wallahi Addah na gaji bazan iya ba, haka kawai na zama kamar jaka shi ya dakeni sannan yanzu takai yayansa su dake ni nidai na gaji tahowa kawai zanyi"
"Ki taho ina? Ni Fattu kashe ni kuke so kuyi ne ko me, nan ga wannan shegiyar ta dibgo mun abun kunya ke kuma kina shirin kaso auranki ki dawo to bazaku kasheni ba koma menene yanzu ki dakata mun na kashe wanann wutar kafin ta fasu idan yaso se na dawo kanki" Addah ta fad cikin tashin hankalin da muryarta ta kasa boyewa.
Cikin rashin fahimtar maganar Addahn Amirah tace
"Addah meya faru? Wane irin abun kunya kuma aka dakko miki badai bashi kika sake ciwo aka zo ana miki cin mutunchi ba?"
"Yo ba gara in ci bashi ba ko birsin ne a kaini da abinda wannan yar iskar yarinyar tajawo mun, ciki fa cikina haihuwa Ummi tayo har wata uku yanzu ina zaune ban sani ba.
To wallahi na gaya mata zubar dashi zamu tafi yanzu ayi dan bazata ja mun abinda za'a ringa zundena a garin Idan na wuce ba shi kuma shegen matsiyacin da yayi mata daga baya inyi qararaa tunda ai na raba shi da yata yaqi barinta seda ya dibga mata ciki tukunna" Addah ta fada cikin masifa se haki takeyi,
Amirah na jiyo kukan Ummi daga gefe tana cewa "ni wallahi baza'a cire ba, haka kawai ance mutuwa akeyi. Ki kyaleni ai Jawad din ya yarda idan na haihu zamuyi aure"
"Sedai ki auri ubanki, na gaya miki indai ina raye bazaki auri wannan matsiyacin ba wallahi" Addah ta zabura tayi kanta, can ta wullar da wayar ma da alama ta manta da cewa waya takeyi.
Zugudi Amirah tayi da waya a hannu cikin tashin hankali, ciki dai cikin shege Ummi ta yi to yaushe hakan ta faru? Zama tayi akan gado ta rafka tagumi radadin da takeji a kunnen ma ya tafi saboda jin sabon tashin hankali yanzu me Alhajin su zece idan yaji wannan maganar ta tabbatar da sedai Allah ya tsare amma da wuya auran Addah be mutu ba a dalilin wannan abun amma.
Ummi ta cuce su koda yake ba Ummi ba Addah zatace ta cuci Ummi tunda babu yanda batayi akan ta barta ta auri wanda take so ba amma ta kafe cewar bazata aureshi ba saboda bashida komai, shegun da take yawan ambatarsu dashi gashi yanzu ya tabbata ai seta shirya goya shegen jika.
Wanann maganar ce ta kashe wutar abinda ya faru da safe, haka ta wuni jiki a sabule batayi musu girki ba daman yaran suna dawowa gidan Ma'u suka wuce shima Bashir daya dawo yaganta a yanda ya fita ya barta kwafa kawai yayi ya sake wanka ya fice be kuma dawo gidan ba se bayan data kwanta.
ASMA'U
Da safe ganin harna shirya yara basu shigo yasa nayi tunanin sun koma cin abinci a gidan su kenan, toh itama Amna ta huta, a tsatstsaye na karya dan ina sauri mukayi sallama da Amnah ina fitowa na gansu cirko cirko a qofar gidansu fuskar Aliyu dana kalla ta tabbatar mun wani abu ya faru.
A gabansu na tsaya da mota na sauke glass, dukkan su suka gaishe ni na tambaye su lafiya Jafar na shirin magana Aliyu ya galla masa harara yace mun babu komai. Sena tabe baki nace "toh yayi, ina Abbin naku kuke tsaye anan kun kusa makara fa" ina rufe baki na hango an bude qofar, nasan Bashir ne dan haka nayi musu sallama kawai na wuce haka nan bana son haduwa dashi kuma.
Gurin qarfe goma ina zaune a office wayata tayi qara, ta true caller naga sunan me kiran YUSUF IBRAHIM WUNTI ina gani na gane Yusuf ne dan haka na daga wayar na kara a kunnena tareda yin sallama.
"Barka da rana Hajia" Yusuf ya fada daga daya bangaren sena amsa da cewa
"Barka dai Excellency"
"Ashe baki manta sunan ba" ya fada yana dariya sena mayar masa da amsa da cewa
"Haba dai ya za'ayi na manta, waya sani ma ko sunan ya tabbata yanzu dan Majalissar Jaha ne kai ko na taraiyya?"
"Haba Hajjaju ai tuni muka tsallake nan, sanata nake meci a yanzu kuma Gomna me jiran gado in Allah ya yarda" Yusuf ya fada, sena bude ido da mamaki kamar yana kallona nace
"Dagaske amma babu labari ko a gurin Alaqiyya ban taba jiba ita da take yar garinku, toh Allah ya tabbatar da Alkahiri kace na kusa zama qanwar Gomna".
"Toh ai baki taba neman koda labari na kinga bazaki sani ba, duk kuma sanda zanje gida se muyi sabani ace kinso kin tafi shiyasa amma yanzu da Allah yayi zamu sake haduwa kinga a arha na ganki a hanya, ya gida ya yarana na shigo Lagos ya kamata nazo na gansu ki sanarwa da Oga kar nazo yayi mun rotse"
Yanda ya fadi rotsen seda nayi dariya nace "ba abinda zeyi maka ai yasan kai Yayana ne ko, ba damuwa toh yaushe zaka shigo?"
"Injiwa ta ya za'ayi ya yarda da wannan nima bazan fara shigar masa gida ba a waje zan tsaya ki turo mun yarana na gansu kar naje mun sha haduwa ma ban san su bane ko da yake bayanda za'ayi naga jininki na kasa ganewa, ina jin ko a taron Arfa naga wanda ya shafeki sena gane shi wallahi
Zan zo gobe da yamma, idan babu damuwa zan sa a kawo takwarar ki anjima kafin nazo kin san an kawota gurin Hajia to ban samu na shiga Bauchi ba ita kuma ta saka rigima se an kawota gurina, inaga na saka a kawota nan din dan idan aka kaita Abuja ma bani da lokaci acan saboda aiki"
"Ok ba damuwa a kawota, ba tare zasu zo da mamanta ba?" Na tambayeshi, a maimakon ya amsa mun se yace
"Shikenan se goben In Allah ya kaimu kiyi saving Number ta nasan yanzu ma qila sa'a naci kika daga tunda baki da ita"
"Ai naga sunan a true caller na gane kaine, Allah ya kaimu goben a gaida Madam" daga haka mukayi sallama.
Dana tashi a hanya naga wani boutique da suke siyarda rigunan yara masu kyau, na tuna gobe ne fa Graduation partyn su Amna jibi kuma suyi prom kuma Faridah bata da kayan da zata saka goben dan haka na tsaya a gurin na siya mata riga me kyau, har na gama na tuno da za'a kawo mun wata yarinyar dukda bani da tabbacin ze bar mana ita ne ta kwana a nan nace bari na siya mata.
A hoto dana ganta dai nasan bazata wuce tsahon Abdallah ba amma dan na tabbatar sena kira wayar Yusuf amma line busy
Text yayi mun cewar yana busy akwai wani abune?
Sena mayar masa da cewa menene tsahon Takwara da size din takalminta ba'a dauki lokaci ba ya turomun kuwa na siya mata kalar ta Faridan da takalmi harda su Ribbon dan naga tana da gashi kafin na wuce gida.
Ina zuwa na tarar dasu sunyi kaca kaca da gidan na kuwa hausu da Fada akan su gyara na wuce dakina ina shiga Jafar ya biyo ni a baya tas ya kwashe abinda ya faru dazu ya gaya mun.
Sosai raina ya baci akan abin, wane irin rashin hankali ne ze saka Aliyu ya daki Matar Babansa da ko bata aure shi ba matsayin uwa take a gurinsa cikin bacin rai nace ya kiramin shi na hadasu su biyun tunda sune manya nayi musu tatas nace kuma idan ya koma ya bata haquri sannan na kira sauran na tara su gaba daya na sake ja musu kunne akan duk wanda na sake jin ya mata ko kallon Banza ne se ransa yayi bala'in baci, haka na wuce daki na barsu Aliyu ya cika kamar ze fashe har na tafi na koma na sake masa warning akan karya kuskura ya taba Jafar dan nasan qarshe se ya huce haushin gayamun da yayi akansa.
Ina Wanka najiyo wayata na qara, da yaje na kammala sena dauro towel na fito kafin na daga ta katse sega wani kiran ya sake shigowa.
Yusuf ne, ina dagawa muka gaisa yace
"Gata can a waje sunzo amma taqi fitowa daga mota, dan Allah ko zakije ki lallaba ta idan kuma taqi su wuto da ita kawai nan bansan ya zanyi da ita bane meeting mukeyi nasan zan iya kai qarfe biyu ma kafin na gama".
"Zama ta yarda in sha Allah bari naje na gani" na fada kafin na kashe wayar. Dogon Hijab har qasa na zura na saka takalmi na fito har sannan yaran suna zaune suna kallo, Abdallah na ganin na fita ya biyoni, a qofar gida naga motoci guda biyu masu numfashi da wasu qarti su biyu a gaban daya daga cikin motar.
Number Yusuf na sake dialing tana shiga ya katse se naga wayar daya daga cikin qattin tayi qara ya daga da sauri kafin ya juyo inda muke se gashi da dan gudunsa ya taho gurin.
Cikin girmamawa kamar ze durqusamun ya gaisheni cikin harshen turanci kafin ya nunamun motar da take a rufe yace tana ciki.
Gaban motar na qarasa na kwankwasa super tint windown motar, kusan minti daya aka sauke shi wani ni'imtaccen qamshin yan gayu ya daki hancina har seda na lumshe ido kafin na bude fuskata dauke da murmushi na kalli cikin motar mukayi arba da wata farar mata irin fara fat din nan dan duk farina se na ganni na zama wata kala a gabanta siririya me dogon gashi da ta barshi a bude, a yanayinta ma zan iya kiranta da bauturiya ko kuma dai ruwa biyu amma ba hausa ko Fulani bace wannan.
Qara fadada fara'ata nayi, dan naga yanayin yarinyar Yusuf a fuskar ta dan haka na tsammaci itace matarsa, cikin harshen turanci na miqa mata gaisuwa dan bana tunanin wanann zataji hausa, ta amsamun a wani yatsine har seda abin ya sosamun rai nan da nan kuwa nima na datse fara'ar dan ban son wulaqanci a rayuwata.
Cikin yauqi da iyayi tace mun "kece Asma'u?"
Sena daga mata kai kawai ina kallonta ta waiwaya daya bangaren da bana hango wanda yake zaune tace
"Sweetheart kije ga Namesake dinki nan zaki zauna a gurinta, ki zama yarinyar kirki kinji"
Cikin muryar yara da kanaji kasan yaron ma sangartacce ne Yarinyar ta fara mana tana cewa
"Ni bazan je ba gurin Dady na zanje"
"Dadynki bashi da lokacin ki na gaya miki kece kike ganin yana sonki amma baya sonki sam, idan ba haka ba ya za'ayi ki taho tundaga United State amma ya kasa zuwa ya tare ki sema yace a kaiki gurin wata stranger ki zauna hmm" Matar ta fadawa yarinyar seka rantse da wata babba Sa'arta takeyi ni kuwa ina daga gefe ina kallon ikon Allah.
Wannan wace irin uwa ce me qoqarin turawa yarta wata aqida da zata sa ta tsani mahaifinta?
Ganin dramar bazat qare ba ya saka na zagaya daya barin da take, badan kar Yusuf yaga rashin kirki na bama qyale ta zanyi su tafi amma bansan dalilin sa na cewa a kawota ba tunda ga uwarta amma yanzun ma sau daya zan lallabata idan bata yarda ba su sauka lafiya.
Qofar na bude da murmushi na na miqa mata hannu seta dakata daga bubbuga qafar da takeyi ta zuba mun ido
"Muje ko kinga dare yayi Momy tana so ta tafi gobe da safe se na kaiki gurin Dady da kaina" na fada cikin lallashi, seta kalleni ta kalli uwarta data wani tabe baki ta