Showing 165001 words to 168000 words out of 260321 words

Chapter 56 - WATA KISHIYAR (ALKAHIRI CE KO SHARRI) COMPLETE HAUSA NOVEL

27 Dec 2024

42709

dauke kai gefe, kai na gyada mata alamar tabbatar wa se kuwa gashi ta zuri qafafunta sena dagata na fito da ita daga motar ashe ma afili batafi girman Yan biyu ba.

Qato daya ne ya bude boot ya ciro mata akwatinta ta yangayu me shegen kyau ga wata qatuwar Teddy da tayi girmanta ma ya wuce da kayan bakin qofa ya ajiye, a taqaice nayiwa matar sallama na juya seta dakatar dani, ta bude jakarta ta zaro wata farar takarda ta miqo mun, da rashin fahimta na kalleta se tace

"List na abubuwan da Sweetheart take ci ne"
"Ikon Allah" na fada a fili na sa hannu na karbi takardar na shige gida ina jujjuyata a hannuna, muna shiga muka tarar suna kallon wani cartoon na Bluey ne sunan sa kome ta kuwa dage ta kwala sunan a kunnenan babu shiri na ajiye ta ta wuce da gudu cikin palour, ganin sun cikia ko ina kan kujerun bata tsaya ba ta dane Cinyar Aliyu da yake kujerar data fi saiti da Tv tayi zamanta.

Se kawai muka tsaya muna kallonta, ita kuwa ba abinda ya shafeta dariyarta takeyi da alamar tana son abinda take kallon.

"Mami wacece wanna" Aliyu ya fada yana sauke ta daga jikinsa amma taqi saukar, se nayi murmushi nace "sabuwar qanwa kuka samu tazo mana weekend, gobe Babanta zezo zaku ganshi" na wuce ciki na barsu.

Akan Mirror na ajiye takardar ina mamakin wannan wace irin mata Yusuf shi kuwa ya aura ko a ina ya samota se Allah.

Seda na gama shiryawa tsaf na kalli agogo nasan lokacin sun fara shirin tafiya dan haka na fito, ina sako qafata ido na ya sauka akan Yar Amana tana zaune tayi daidai tana cin wainar fulawa da Manja da alama yanzu sukayita farar rigar jikinta tayi kaca kaca ta canza kala.

"Na bani ni Asma'u me kuka bata haka" na fada ina qarasawa gurin da sauri, seta dago tana yar dariyar yarinta cikin turancinta da kana ji kasan rainon America ce tace

"Mami da dadi amma akwai yaji"
"Waya ce ku bata Amna me yasa baku tambayebi ba kafin ku bata" na fada ina janye farantin se kawai naga yarinya ta fara birgima kamar me hawa bori, Amna na dariya tace

"Wallahi Mami ban san ma sanda suka shirya ba Jafar ne yayi musu gashi can ma yana soya sauran a Kitchen"
"Kun kyauta, idan cikin yar mutane ya baci se kusan yanda zakuyi da ita ai" na fada ina akiye mata kwanon na koma na dauko wayata na shiga kiran Babanta.

To a takardar fa wasu lissafin abincinsu can na turawa yan gayu aka rubuta sunzo sun hadata da fulawa da manja, saurin fa da nayi kenan na fita ko oat ne na saka su hada mata tasha dan banida tarkacen dana ga an rubuta a takardar.

Nayi Sa'a kira daya ta shiga ya daga yana cewa
"Badai yar rigimar taqi zama ba"

"Wa ai gata can muan shigowa ma ta shiga sabgarta, Mamanta ce ta bani list na abincin da take ci, todai in gaya maka ina daki kafin na fito su Jafar suka dura mata wainar fulawa da yaji na dauke na hanata ci ta farayi mun bori shiyasa na kiraka kar muje cikinta ya birkice ga dare yayi" na fada masa.

Dariya sosai yayi yana cewa "Ma'u kenan sarkin ci ai indai taga abinci setaci ko wanne iri ne, ki manta da wata takadda na rasa me yake damun Intee Allah yasa dai batayi miki halin nata na wulaqanci ba"

"Aa ba komai gaisawa kawai mukayi ta tafi, to shikenan ba matsala kenan mu bata duk abinda muke ci" na sake tambayarsa

"Ki bata komai, dambu fura tuwan dawa ba abinda Hajia bata dura mata a Bauchi tun bata kai haka ba me kuma ya sameta tsabar matsala irin ta uwarta ce kawai" ya sake fada, se nace masa

"Allah ya rufa Asiri, goben da wuri zaka shigo dan zamu fita, zamuje Graduation din su Amna qarfe goma"

"Kai masha Allah har Amna ta gama secondary school dagaske dai tsufa ya fara kama mu, ba damuwa a wacce makaranta ne idan na samu dama sena shigo nima"

Sunan makarantar na gaya masa mukayi sallama, ina jiyo ihun Ma'u takwara na fita naga meya faru na tarar wai su Faridah ne zasu tafi ta kama qafar Jafar ta riqe da gani dai dashi aka qulla abota se tsalle take tana ihun bazasu tafi ko kuma seta bisu, kamo ta nayi ina rarrashi amma ina qara zillewa take yi, qarshe dakyar na samu ta haqura shima seda nace Faridah ta zauna ta kwana suka zille sauran suka tafi na saka Amna tayi mata wanka suka kwanta a raina ina Addu'ar Allah sa kar Bashir yace zeyi tashin hankali a daren nan cikin Sa'a kuwa har muka kwanta shiru.

WASHE GARI

M&Z FASHION DESINGNERS
INA MATA YAN KWALISA
KU GARZAYO M&Z
FASHION DESNGNERS DAN SAMUN IN GANTATTUN KAYA MASU AMINCI.
IRINSU
ZANNIWAN GADO
TROW PILLOWS NA ZAMANI
TUM TUM
BABY SET
TOILET SET
KITCHEN SET
LABULAYE DA SAURAN KAYAN KWALLIYAR GIDA.
HARMA DA ATAMFOFI DA KAYAN KITCHEN AKAN FARASHII ME RAHUSA
KU NEMEMU AKAN LAMBAR WAYA 07064870087.08127423783.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR πŸ₯°πŸ‘Ή
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 48



WASHE GARI


Washe garin ranar da wuri muka shirya saboda su basayin African time irin namu na yan Arewa. Sosai nayi kwalliya da Doguwar rigar Lace baqi me Golden din zare na yafa mayafina a kafada na saka coge nida kaina na yaba kwalliyata dan na fito cas dani.

Da muka fito zamu tafi Anty se tsokanata take wai taga alamar fa Zawarcin nan me lasisi nakeΒ  zuba to dai nayi a hankali kar na sa maza suringa karo a hanya a garin kallo na.

Bashir ne ya tafi da yara mazan a motar sa harda Amirah suka tafi, daman bamu hadu ba a bakin Amnah naji cewar da Amiran aka tafi nayi murmushi kawai a raina ni kadai nasan tsiyar da zan qulla mata tunda nidai ban gayyaceta ba ai, A motata muka tafi tareda Anty da yammatan harda sabuwar yata da tasha kwalliya dan tun dare na gyara musu gashin su ita da Farida sunyi kyau sosai cikin rigar jiya kamar wasu Yaya da qanwa haka muka rankaya muka tafi.

Sanda muka isa lokacin an fara shiga dakin taron, sallama Amnah ta mana ta wuce gurin Yan ajinsu ni kuma na tsaya dakko Get pass dan suna motata tun ranar da aka kai mana ban cire su ba nasan su Bashir ma basu shiga tunda dole su jira pass din, murmushi nayi sanda na fito dasu na qirga.

Guda goma ne cif, daman guda hudu suke bawa ko wanne dalibi idan kana son qari seka siya dan haka na qara guda shida ya zama teburi daya muka kama kenan, nida yarana banda Amnah mu bakwai se Anty ta takwas ga Bashir tara ragowar daya kuma daman na siyane kawai dan teburin me Goma ne to yanzu ga sabuwar yar da nayi shi kenan mun cike shi.

Haka kawai naji dariya ta kama ni sanda na hango Amirah yanda taci uwar kwalliya kai ka rantse wata dinner auren qawarta zata tafi se wani karairaya take a gefen Bashir hannunta cikin nasa, wani ikon Allah se banji komai a raina ba illah ma dariya data bani kawai dan a yanda take abun kana gani kasan irin da gayyar nan take dan ta bata mun bata san ko a kwalar rigata ba.
Mijin nata ma da da na dauka na dora akai yanzu na sauke nima na huta.

Seda na qara gyara fuskata tsaf kafin na kulle motar na fito ina gyara zaman gyalena a kafada daya, cikin takun yauqi da yanga na qarasa inda su Bashir suke ina jin yanda idon mutane yayi mun caa a raina na shiga karanta 'A'uthubikalimatillahi tammat min kulli shaydanin wa hammatin wa min kulli aynin lammati' saboda mugun ido haka na qarasa inda suke kallo daya nayiwa Bashir daya watso mun idanunsa da suka fara rinewa da bacin rai nan take na dauke kaina ina murmushin qeta.

A saitinsa na tsaya fuskata dauke da murmushi na gaishe shi, be amsa ba se matsowa da yayi bayan ya saki hannun Amirah da tunda ta ganni ta shaqa tayi fam se wani harare harare takeyi kuma dai baze wuce tsabar hassada da baqin cikin gani na bane ya saka. A daidai kunnena ya tsaya idonsa akan fuskata yace

"Meye kike yi haka Ma'u baki kalli kanki a mudubi ba da zaki fito a haka cikin wannan kwalliyar? Jifa yanda maza suke kallonki dan Allah ki koma nasan bazaki rasa Hijab ko Abaya a mota ba ki saka".

Wata siririyar dariya nayi kafin nayi qasa nima da murya yanda shi kadai ze ji abinda na fada nace masa

"Ai daman saboda mazan su kalleni nayi, ko ka manta a kasuwa nake yanzu ne?"
Ina fadar haka na janye daga kusa dashi ina ji ya na kira sunana amma nayi kamar ma banji ba, katinan hannuna na fara bawa yaran da akwai table Number dan haka sukayi gaba, na miqawa Anty nata na miqawa Bashir daya sannan na juya ina cewa Anty

"Muje toh, Baban Ali seka shigo koh" nayi gaba abuna dan ban nuna nasan da wanzuwar wata halitta ma a kusa dashi ba, hannuna ya riqo da sauri na waiwaya na watsa masa wani mugun kallo da ni kaina bansan na iya shi ba, se yayi saurin sakina yana cewa

"Yi haquri amma dan Allah kije ki.."
"Karka sake mun haka, da mutunchi na kazo kana kamani a gaban mutane bana so, sannan baka da hurumin da zaka gaya mun abinda zanyi yanzu ko wanda zan bari ka gane" na fada ina qara daure fuska.

Ina kallo ya hadiye wani abu qut kafin ya marairaice fuska ya sake cewa

"Nace kiyi haquri ai, naga kati daya kika bani ina na Amirah?"

Juyawa nayi na kalli Amiran da ya ce se numfarfashi takeyi kamar wadda zata haihu na maida idona kansa nace masa

"Na iya wadanda aka gayyata kenan, bama buqatar qarin gayyar sodi" ina gama fada na bi bayan Anty da ta dade dayin gaba daman.

Bansan yanda suka qare ba, munfi kusan minti sha biyar da shiga kafin na hango su sun shigo Amirah na bayansa fuskar nan kamar ka tsira mata Tsinke ta fashe tsabar yanda ta kumbura, acan kejerun yan regular naga ya sama mata sit ta zauna, ya dan duqa da alama magana yake gaya mata kafin a fusace naga ya taho inda muke zaune.

Na zata masifa ze zo yayi na qara tamke fuska ta tsaf se naga yana zuwa yaja kujerar da tayi saura ya zauna ya gaida Anty ta amsa masa sama sama nidai na mayar da hankali kan cultural dance da akeyi ina jin yanda idon Bashir yake kaina amma naqi kallon barin da yake.

Wayata dake ajiye akan teburin ce ta dauki qara, yanda kasan shi aka kira ya bi wayar da kallo na kai hannu na dauka, Yusuf ne da nayiwa saving da Abban Takwara, saboda qarar kida banajinsa dan haka na tashi nayi tacan baya gurin inda kujerun su Amirah yake, ta kusa da ita na wuce ina giftawa naji ta saki tsaki ban kulata ba na wuce na amsa wayata.

Gaya mun yayi yana waje nace ya jirani gani nan zuwa, na sake zuwa na wuceta dan banida lokacin da zan tsaya ina kula wannan yarinyar. Seda na koma sit dina, jakata na bude na ciro ragowar kati daya dan Ma'u Jafar ne ya dagata da yake ta sangarta ta lankwashe a jikinsa yanda kasan wata yar Yaye dan haka basu karbi katin taba muna shiga ya bani na saka a jaka.

Ina kallon yanda Bashir ya bini da kallo ganin na ciro wani katin daga jaka, se na juya na cewa Anty ina zuwa na wuce ta saitin Bashir ya shaqi qamshij da nakeyi kuwa kafin ya ajiye numfashi na wuce shi ina juya mazaunan da Allah ya hore mun shi kuwa Ya bini da kallo da baki a sake har na qulewa ganinsa.

A qofar gurin naci karo da Yusuf, wani dace shaddar jikinsa yanda kasan tare muka siya da kayan jikina sunyi bala'in dacewa.

Cikin mutuntaka muka gaisa da wani dana gansu tare babban mutum ne sosai wai shima Sanata ne akwai yaransa biyu a yan Graduation din, ba'a ma karbi katinan mu ba muka shiga tareda Yusuf din kai tsaye teburin da muke zaune na wuce gaba yana bina a baya.

BASHIR
Tunda yaga Asma'u a gurin gaba daya ta sake kwance masa notin kai. Kwalliyar ta tayi bala'in tafiya da imaninsa ga wani kishinta daya taso masa Ganin yanda maza suke binta da kallo.

Tana bashi katin nan da ta juya haka ya rakata da ido gani yake kamar qara mata quruciya akayi dirin jikinta ya sake fitowa, yana can aikin kallonta tsakin da Amirah tayi ne ya dawo dashi hayyacinsa se ya kalleta sanda take cewa

"Yanzu kana kallo ta tafi bayan kaji abinda tace wato nice ma gayyar sodi ko kuma kayi shiru baka ce komai ba"

"To so kikeyi na kamata da kokawa nace seta baki ko kuma nawa zan baki? Daman ai ba gayyatarki ki akayi ba gayyar sodin kika zo.

Kinga ki kama kanki wallahi karki sake kice zakiyi mun shirme a gurin nan zan bata miki rai" Bashir ya fada cikin bacin rai, wallahi da a Gombe nema tafiyarsa zeyi ya barta idan yaso ta koma gida dan dai kawai nan bata san hanyaΒ  bane.

Amirah data shaqa iya wuya, dakyar ta danne bacin ranta tace
"To yanzu a waje zaka barni ka shiga ciki kenan" ta fada kamar zatayi kuka

"Seki koma mota ki zauna dan dai ni ban san a inda zan samo miki kati ba kuma nan ba irin taron da kika saba zuwa bane ko ba'a gayyace kuba ku shiga su komai a tsare sukeyinsa" Bashir ya fada yana hararar ta, se kawai ta saka masa kuka tana cewa

"Da kasan wulaqanci zaka mun idan nazo tun a gida se kace bazaka dani ba amma yanzu kace na tafi mota bayan ga katuna can a hannunta harda wasu daban ta gayyato se nice baza'a bani ba"

Tsaki Bashir yayi ganin tana neman tara masa Jama'a dan har an fara kallon su yace mata yana zuwa ya tafi Gurin securities din bakin gate.

Seda yaci wuya dakyar ya samo mata regular card shi kansa dubu goma aka siyar masa, daya bata a maimakon ta gode seta hau sabon qorafi wai ba irin nasu bane dan ko a kala katin ya banbanta.

Banza ya mata suka shiga ya rakata kujerarta se raba ido take ganin Jama'a kala kala yanzu da wannan shagalin za'a mata buqulun zuwa tab, Allah ya kaimu Na Aliyu wannan ai dan mijinta ne itama dole tana teburin gaba tunda yanzu ance mata gayyar sodi.

Hakata zauna wani mugun kishi ga kyashi da hassadar Ma'u na dukanta. Duk abinda ta gani a jikinta ji takeyi dama itace, simple lace me Azabar kyau ga zobuna da awarwaron gwal suma qira mara hayaniya sun qara fito da kwalliyar ta sosai qarin baqin cikinta yanda Bashir ya kasa dena kallon Ma'un ba daban ba da se tace su tafi kawai amma ina setaga kwal uwar daka sannan idan sun koma gida se ayi uwar da za'ayi.

BASHIR
Kwarewa yayi da ruwan da yake sha a daidai sanda Ma'u da Yusuf suka ratso dakin taron kamar wasu shaqiqan masoya fuskokinsu dauke da murmushi. Ba Bashir kadai ba, da yawa mutane seda suka bisu da kallo haka suka qarasa har teburin Yusuf ya daga Ma'u qarama data fasa ihun murnar ganinsa ya zauna a gurin suna fuskantar juna da Bashir.

Fuska a sake ya miqawa Bashir da yayi suman zaune hannu dukda can qasan zuciyarsa bazeyi qarya ba daurewa kawai yayi amma sosai yake Adawa da Bashir din daya rabashi da macen da yake so sama da kowace mace a rayuwarsa.

Ya wargaza masa mafarkin shimfida rayuwar aure me ciki da aminci da qauna qarshe ya barshi da gantalewa da zama macen da bata dauki aure a bakin komai ba.

Malam Bashir kuwa bin hannun Yusuf yayi dake daure da wani shegen Agogon diamond a tsintiyar hannunsa, kai Cufflinks dinsa kadai abin kallo ne wani irin tuquqin baqij ciki da kishi suka taso suka shaqe masa wuya kawai ya mayar da kai gefe ba tareda ya karbi musabahar ba, ko a jikin Yusuf ya maida hannun gurin su Aliyu duk suka gaisa yana tambayar su sunayensu dan ko shine Bashir din akan Mace kamar Ma'u zeyi abinda yafi haka shi yama ga qoqarin sa daya zauna teburi daya dashi ai

Gaisuwa me kyau sukayi da Anty Halima nan da nan suka shiga hira kamar sun san juna dan shima akwai faran faran da mutane halinsu yazo daya dukda da ita da gayya ta qara sakewa suke hirar saboda ta turawa Bashir takaici se gashi kuwa Hira ta barke tsakanin Yusuf da sauran Yaran Ma'u qarama na qara maimaita masa sunayen su se dariya suke mata dan bata iya fada ba ya kalli Asma'u yace

"Gaskiya kin iya bida yara kiga yanda yarinyar nan ta sake lokaci daya anya bazan bar miki ita ba kuwa"

"Ai na yara kadai ba har manyan in gaya maka ta iya tafi dasu ta kowacce hanya me sauqi ko me daci, ka bar mana ita kawai mun samu qarin ya" Anty ta fada tana dariya ta gefe kuma tana hararar Bashir da ya kumbura dan har kamar yafi Amirah kumbura yanzu.

Shigowar yan Graduation ce ta dakatar dasu daga hirar, nan da nan aka shiga gabatar da abinda aka je yi, an raba musu kyututtuka sosai Amna ta samu lambobin Yabo dan ita ta lashe Best Student ta shekarar aka kira Iyayenta, Ma'u na miqewa Bashir shima ya tashi daga kan stage ta hango Amna na tsalle tana nuna mata bayanta tana waiwayawa se ganin Alhaji Qarami tayi tareda Matarsa ta biyu da daya daga cikin Yaransa Abdullahi da suke cewa Baffa.

A tsakiyar Mu nida da Bashir Amnan ta tsaya akayi mana hoto se wani washe baki yake shi ala dole ga Baban Amnah, ganin Alhaji Qarami da Yah Muslim da shima bamu san da zuwan sa ba sun qaraso gurin se Bashir ya dan matsa yana shafa kai amma Alhajin ya sake mayar dashi gefen Amnan su kuma suka tsaya daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login