Showing 144001 words to 147000 words out of 177840 words

Chapter 49 - FITAR TSIRO COMPLETE HAUSA NOVEL BY RUFAIDA UMAR

11 Jul 2024

79148

da ita, don kanta ta sauko ta ɗiba."

Baba Saude tuni ta fice tana fadin ai ba za'a shiga tsakaninta da Haulatu ba. Yanzu za ta kai mata. Umma dai girgiza kai ta yi. Sadauki jin an zo inda yake so ne ya sanya shi yin magana.

"Wani abu ne ya samu wayar?"

Ɗan taɓe baki Umma ta yi.

"Uhum, wai fashewa ta yi ta tsage, jiya tsautsayi ta ɗan zameta faɗo daga bene amma ba ta ji ciwo ba, bakin ne kawai ya ɗan kumbura. To shi ne ta kashe wayar wai ba za ta ƙara aiki da ita ba."

Duk sai ya ji babu dadi, ashe baiwar Allah abin da ya faru gareta kenan?

"Ayya, Allah ya ƙara ya kiyayewa."

Umma ta amsa da amin. Daga nan ya yiwa Umman sallama ta ce ya gaida su Momi Nuratu, ya amsa sannan ya fice.
Wurgi take da duk abin da ta samu a ɗakin nata kamar wata mahaukaciya, yi take tana ihu da kuka, Maminta na aikin rarrashi da nuna mata wannan sam ba zai zame musu mafita ba.
Ganin abin ba na ƙare bane ta riƙe tsintsiyoyin duka hannunta biyu.

"Kina hauka ne?! Wannan abu da ki ke yi an fadamaki shi zai haifar da ɗa mai ido? A tunaninki zai sa ki samu Sadauki?"

Jannat ta fisge hannuwanta.

"Ni Mami ki rabu da ni! Wannan banzar Bokanyar ta yaudare mu ta ci amanarmu kawai! Babu wani abu da ya yi tasiri akan Yaya Sadauki, ko kallon salama ban samu daga gareshi ba, bai ɗauke ni a bakin komai ba sai wulaƙantacciyar ƙanwarsa!"

Mamin Khaleefa ranta ya ɓaci. Tun sadda Jannat ta kira Bokanyarsu da banza ta ji kamar ta kifamata mari don ta tabbata aljanun Bokanyar suna ji kamar yanda ta taɓa shaida musu cewa ita ko ba ta wuri aka ambace ta, aljanunta na kwaso mata komai. Daƙyar ta iya danne fushinta ta ce

"Ya isa haka, kar ki ƙara magana, idan ya san wata bai san wata ba."

Jannat ta juyawa Uwar ƙeya, ta gaji da gafara Sa ba ta ga ƙaho ba. Ta fi yarda da abinda ta yanke a zuciyarta, wato tunkarar Baba Alhaji ta cire kunya ta ce masa tana son Yaya Sadauki. Ta gwammace ta yi haka da dai ace tana kallo ya auri wata ƴar bariki Haulatu ya kyaleta. Mamin har ta gama surutanta a yanda Jannat ta dauka, ba ta ko kalle ta ba har ta gaji ta fice sakamakon wayarta da ya hau ringing kuma sunan Khaleefa ne. Tana ɗauka yake sanar da ita Hafsat matarsa ta haihu suna asibiti an samu ƴa mace. Dama Annur ɗin tun soma laulayinta ya ke nan a gidan Mamin, nan ta shiga faɗa wai don me bai kira ya sanar da wuri ba ya bar ta ita ɗaya a asibiti. Sai da ya sanar da ita ai Hajiyar Hafsat din na nan sannan ta sauko. Ɗakin Jannat ta dawo fuskarta a sake.

"Hafsat ta yi, an samu ɗiya mace. Shirya muje asibi..."

"Ni babu inda zan je." Ta amsa kai tsaye fuskarnan kamar hadarin kaji. Madadin Mamin ta ji zafinta sai kawai ta share da fadin.

"Dama na san yanayin nan da kike ciki ba lallai ki iya zuwa ba. Ki huta idan kina buƙatar wani abun sai ki yiwa Indo magana ta girka maki. Kinsan Hajiya Shukra ba mutunci ne da ita ba, yanzun za ta ce ba a kula da ƴar ta ba, bari na yi sauri na tafi."

Ko ci kanki Jannat ba ta ce ba.

***
Radiya da Safina zaune sun yi wa Haulatu  ƙuri da idanu ita kuwa sai ja musu rai ta ke. Sun fi minti ashirin da zuwa dakin amma daga bari ta yi shirin bacci sai bari ta shafa mai a kanta yana mata ƙaiƙaiyi. Gajiya suka yi Safina ta fisgo hannunta har murfin man gashin na faɗuwa, ta kuwa yi dariya.

"Don Allah mene ne haka? Ke daɗina da ke idan kin ga ana son jin labari akwai jan rai. Kin ce mana Yaya Sadauki ya maki wasu maganganu da bikin Maama amma kin ɓige da wanka yanzu kuma shafa mai na tsirfa."

Ta ƙara murmusawa. Umma ba sa nan sun tafi asibiti ganin matar Khaleefa da ta haihu don haka su kaɗai ne a saman ke budurinsu. Ganin sun mata ca ya sanya ta saurin zuwa ta zauna tana ɗaga hannuwanta alamun saranda.

"Na ji kar ku cinye ni ɗanya." Nan ta shiga ba su labarin duka abin da ya faru, tun soma labarin suke washe haƙora har ta kai aya. Ai kamar jira suke yi suka ruƙunƙumeta suna ihu da dariya. Safina ta mike tsaye har da rawa da juyi.

"Kai kai! Ba zan iya misalta maki farin cikin da nake ciki ba Haulat, ke kuwa don Allah me ya cije ki da har yanzu ki ka kasa sanar da shi kin amince ta waya? Au, mts, ashe ba wayar." Faɗin Radiya kenan, Safina wacce ta dawo ta zauna ta ƙara sakin wata dariya kafin ta ce.

"O'o, kai, Alhamdulillah. Ke har na hango idanun Fahima da Anti Jannat, ai ni nasan babbar magana ce wannan lamarin zai jawo, sai mun toshe kunnuwanmu duk abin da za'a ce a yi ta faɗi, ni nasan dai iyayenmu za su rungumi lamarin nan da hannu bibbiyu."

"Ki na batun su Fahima, ai idanun Yaya Zaid na fi kaunar na gani, hum, ya yiwa kansa." Radiya ta faɗi, nan Safina ta riƙe haɓa.

"Au, to ai na ma manta, ni Yaya Mu'az ma kamar dai shi na kula ko shiga harkarki ba ya yi, ya biyewa Momi ta raba zumuntarku. Tunda dai ai ko babu aure akwai zumuntar."

Haulatu ta taɓe baki.

"Su suka sani, ni a farko na ji ciwon yanke alaƙar zumuntar amma yanzu ko a jikina tunda dai ai shi yana da hankali kuma ya yi karatu a addinance ya san hukuncin yanke zumunci."

Nan suka rufe babin nan, suka yi ta zuzuta yanda Haulatu da Sadauki suka dace ita kuwa sai murmushi ta ke bugawa. Su ne har goman dare su na hira don ma sa'ar da suka ci washegari ya kama Asabar babu makaranta, Haulatu ma babu lesson saboda malamar tasu ta yi tafiya. Ga kuma Safina da ke shirin barin gidan a gobe za ta koma hannun iyayenta. Haka suka yi kamar kar a rabu a wannan daren.

***
Tun wayewar garin Asabar ta ke cike da damuwar rashin waya, ba don komai ba sai a ranar ne za ta ba Yaya Sadauki amsarsa, babu damar ta yi yanda ya buƙata. Wayar Umma kuwa ba ta so ta yi amfani da shi, ita sam ba ta yanke sanar da Umman yanzu ba duk kuwa da irin yanda sam ba ta mata ɓoyon komai nata. Tsoron yadda za ta karɓi zancen ne ya sa ta zaɓi rufemata a yanzu. Koda ta sauko zuwa ƙasan, ta iske suna karyawa, ta ƙara gaida Hajja da Umma karo na biyu bayan wanda ta yi da Asubahi, zamanta ke da wuya ta soma haɗa shayi kawai sai gani ta yi Hajja ta ajiye mata kwalin waya a gabanta. Idanu waje ta dubi wayar kafin ta sa hannu ta ɗauka. Samsung A24 ce. Ta ɗago kai ta dubi Hajja da wani irin wangale baki na jin dadi ta ce.

"Hajja, waya ki ka siya min?"

Hajja na dariya ta amsa.

"Ina dai niyya aka riga ni. Yayanki ne ya aiko yau da safe ya ce a baki. An chaja maki ita tun jiya, har layin waya ya saka, kinga sai ki haɗa da tsohon layinki idan kina so."

"Wane Yayan?" Ta tambaya cikin son sani, don ta ƙudurce idan har Yaya Mu'az ne wannan karon ba za ta karɓa ba.

"Sadaukin Alhaji." Umma ta amsa mata da murmushi a nata fuskar ita ma. Ko kaɗan ba ta kawo komai a rai ba, kawai dai ta kula jininsu ya haɗu.

Ita ko Haulatu ai tuni ta yi suman zaune don jin wani sanyi da dadi. Kenan da Umma ta ce mishi ba ta da waya tuni ya saka a rai zai siyamata? Ko da dai gani ya kori ji tunda ga ta ga wayar a hannu, ta ciro ta a kwali ta jujjuya, silver colour ce, ta ganta a kunne.

"Ki ajiye wayar hakanan ki karya mana." Fadin Umma tana kallonta.

Ba shiri ta ajiye kuwa, tana kammalawa kuwa ta tattara gurin ta kai komai kicin sannan ta kwashi jiki za ta koma sama don kiran su Safina a waya ta ƙara jin muryar Umma.

"Ki dai kira shi ki masa godiya." Hajja kuwa fadi take.

"Ni dama dai wannan son da wancan mara aikin yi ke maki, Sadaukin Alhaji ne ke yi, ai da na ji dadi."

Haulatu dake amsawa Umma da toh, ta dubi Hajja jin abin da ta ce kafin ta ɗan kalli Umma wacce ba ta ce uffan ba sannan ko a yanayin fuskarta ba za ka fahimci komai ba don haka sai ta yi saurin juyawa ta haye abin ta. Hajja kuwa murmushi kawai ta yi ba ta ce uffan ba.

***
Ya kalli fuskar wayarsa ta fi a ƙirga, ya fito ya yi kewayen, shi ne har ɓangaren Baba Dakta da Baba Alhaji daniyyar gaida su, ya ci karo da Safina wacce za ta wuce da yamma, ya tambayi ƙawarta? Tana danne dariyar ƙin maida amsar da Haulatu ta ce ba za ta yi da wuri ba sai ya ƙosa ta amsa.

"Ba ta shigo ba duka yau."

Sadauki ya haɗiyi miyau mai ɗaci, ba ya son tunaninsa ya cigaba da ba sa cewa ba ta sonsa ne. Ya yi shiru ya na sauraron Baba Alhaji na yi jan Safina da tsokana wai ta zauna kawai babu inda za ta koma. Ita kuwa tana fadin ya yi hakuri. A karshe ya mata nasiha sannan ya tambayi ƙawayenta? Safina sai da ta ɗan kalli Sadauki da idanunsa ke kan waya amma kuma hankalinsa na ga amsar da za ta bayar sannan ta maida kai ga Baba Alhaji.

"Tare zamu je da su. Za su yimin rakiya."

Jin haka Sadauki ya ɗago kai amma bai ce uffan ba.

"Toh shi Gali yana nan?"

"Eh amma babu mai a motar ya ce."

Ɗan gyaran murya Sadauki ya yi.

"Bari na kai su kawai, dama zan je asibiti ganin Baby."

Yana nufin jaririyar da aka haifawa Khaleefa. Safina ta yi godiya ta miƙe ta fita tana danne dariyarta, ba za ta faɗawa Haulatu wanda zai kai su ba gudun kar ta ce ta fasa ta ce tana jin kunya. Riba dai biyu, za su je su ga baby wacce a hoton waya kawai suka gan ta da aka turo whatsapp group dinsu na zuri'a.

***
Biyar da mintuna na yamma, Safina ta kammala duka zagayenta na yiwa kowa a gidan sallama, duk inda ta shiga sai ta fito da wata kyautar, hatta Umma sai da ta bata turmin atamfa. Haka ta dinga fitar da hawaye kamar kada ta tafi duk da dai cikin garin katsina ne amma sabo ake wa kuka.

Haulatu cikin doguwar baƙar abaya mai kwlaliyar duwatsu, leɓɓanta sun sace daga kumburin da suka yi sai dai ɗan taruwar jini kaɗan da ake gani daga ƙasa. Idanunta ya ɗan yi ja saboda kukan kewar Safina da suka yi ita da Radiya. Hajja ta dinga yi musu faɗa don ita ba ta son kuka, fadi take ai ba mutuwa Safinar za ta yi ba, duk sadda aka so haduwa za'a ga junan.

Koda suka fito su Najeeb dake tahowa daga wurin motar Sadauki inda suka kai kayan Safinar aka sa a boot, suka yi turus suka dube su.

"To super glue, wai kewar Safinar ce ta saka ku kuka? Hahaha! Taɓ! Ni kuwa na yi me toh? Me dafamin indomie idan na ji yunwar dare za ta tafi?"

Haidar ya kai masa bugu.

"Au abin da za ka ce kenan ko? Sorry Feenah, muna kaunarki, ai ba a rabu ba, kina can ma za ki dinga ganinmu. Ba mu gama jin kewar Maama ba ke ma kin tattara za ki gudu ki bar mu ko? Ai shikenan."

Hon ɗin da Sadauki ya yi ne ya sanya su tuna wanda aka bari da jira.

"Oh, kai ba ruwana sai anjima. Boss ya ƙosa ku tafi. Sai mun yi waya."

Haulatu ta dubi motar Sadauki kafin ta dubi su Najeeb da har sun ɗan soma takawa.

"A'a, ban gane ba? Ba za ku je ba? Kuma ki ka cemin Gali ne zai kai mu?" Ta ƙarashe tana kallon Safina.

"Mu je Haulatu, motar ce kawai ta Yaya Sadauki, yana jira ne a kai mu a dawo zai fita."

Kasancewar tuni su Najeeb sun yi gaba sai ta yarda, bayan ta bude gidan gaba ta sanya kai ta juyo tana kokarin rufe murfin da fadin.

"Malam Gali ina..."

Sauran zancen ya maƙale mata a fatar baki ganin wanda ta yi ido huɗu da shi. Sai ta ga kamar ya ƙara haske don fuskarnan ta yi fayau. Nan kuwa damuwa ce don har wata ƴar rama kaɗan ya yi. Sai ta ga ya yi mata kwarjini ta kauda kai ta gaishe shi, ya amsa mata yana sauke ajiyar zuciya. Su Radiya ma gaida shi suka ƙara yi ya amsa, jin duka sun rufe ƙofofin ya sa itama rufe na ɓangarenta amma tsabar sanyin da jikinta ya yi bai ma rufu sosai ba. Madadin ya ce ta ƙara rufewa sai kawai ya cire seatbelt dinsa ya fita a motar duk suka zubamasa idani don a tunaninsu ko mantuwa ce ya yi, Haulatu kuwa kallonsa take ganin ya zagayo ya buɗe murfin motarta sai da gabanta ya fadi don a tunaninta ko laifi ta mishi zai sauke ta a motar, sai ta ga ya ƙara rufewa dakyau sannan ya zagaya, har wani ajiyar zuciya ta saki, su Safina da Radiya ko kallon juna suka yi da murmushi. 

Madadin ya fara kai su gidan Dakta Hashim, sai ya soma yin asibitin. Ita dai Haulatu babu um balle um um, kallon wayar da ya siyomata take yi, ga kunyar ko godiya ba ta masa ba, shi kuwa a hankali yake bin waƙar da ke tashi kaɗan kaɗan na harshen larabci. Yana tsayawa ya dube ta.

"Ku shigo muje, na san ba ku zo ganin baby ba ko?"

"Eh Yaya." Safina da Radiya suka amsa, ya bude murfi ya fito su ma duka suka fito ya rufe. Gaba ya yi su na binsa a baya yana waya, lambar ɗakin aka fadamasa ɓangaren VIP ya tafi. Haulatu sai kallon wurin tame, an ƙara gyara a asibitin kamar ba nan ta taɓa zuwa ba. Tun ganin da ta yiwa Nusaiba a tsaye tana amsa waya a ƙofar ɗakin ta gane Momin Mu'az na ciki. Nusaiba da sauri ta cire wayar a kunne ta gaishe da Sadauki ya amsa ba tare da ya kalle ta ba ya juya ga su Haulatu.

"Ku soma shiga." 

Safina dake a gaba ta murɗa ta shiga da sallama aka amsa, Mamin Khaleefa ce sai Momin Mu'az da wasu yan uwan Hafsat din ciki har da mahaifiyarta Hajiya Shukrah. Ganin Haulatu ya sa sauyi ƙarara ya bayyana a fuskokin Mami da Momin Mu'az. Haulatu dai ta gaishe su yanda ƴan uwanta suka yi, masu amsawa sun amsa idan ka dauke su biyun. Sai a sannan Sadauki ya shiga shi ma. Ganinsu tare ya baƙantawa Mamin Khaleefa, wato can ga ƴarta na sumbatu a kansa, shi kuwa yana nan ya zama direban Haulatu. Sun dai amsa gaisuwarsa da yaƙen dole, Hajiya Shukrah ce ta sakarmasa sosai don mutuminta ne, sadda Khaleefa ke yayin zuwa gidanta tare suke zuwa. Aka miƙo masa jaririyar mai kama da Khaleefa sak, karɓa ya yi ya shiga yi mata addu'a. Haulatu ƙasa-ƙasa take satar kallonsa ganin yadda bebi ya yi kyau a hannunsa, har wani murmushi ta ɗan yi. Ba zato kuma ya ɗago kai suka haɗa idanu, shi ma murmushin ya yi mata sannan ya miƙa mata bebin. Wannan abu duka a kan idanun iyayen nasu biyu dake adawa da su, ransu ya mugun ɓaci amma suka danne. Momin Mu'az ke tambayar Safina dagaske guduwa za ta yi daga babban gida, dariya kawai ta yi. Ba su wani jima ba suka yi musu sallama suka fice. Kasancewar Sadauki ya riga su ficewa ne ya sa Safina fadin.

"Ku, ni kadai na kula da hararar da su Mami ke bugawa Haulatu?"

"Wallahi ina shirin magana ki ka rigaye ni Feenah. Hum, ai na ga abin mamaki. Can dai ta matse musu, in sha Allahu na gaba dai ya yi gaba." Fadin Radiya.

"In sha Allahu." Safina ta amsa. Ita ko uwar gayyar ba ta ce uffan ba don dama ai hakan ba baƙonta ne daga wajensu ba.

A gidan su Safina ma ya bar su bayan ya shiga an gaisa ya ce zai je ya dawo, sai wurin bayan sallar isha'i sannan ya dawo, nan din ma an tafi da kewa amma wannan karon ba su yi kukan ba. Suna isa gida bayan ya yi parking Radiya ta bude ta fita, ba ta ma tsaya jiran  Haulatu ba don ta san maganar tsakaninsu ne.

Kafin ya ce komai ta riga shi.

"Yaya nagode Allah ya ƙara buɗi. Wayar ta yi kyau sosai."

Abin da ta ce kenan. Ta ji sadda ya sauke ajiyar zuciya.

"Nevermind, yiwa kai ne. Kin fa son amsar da nake son ji please. Na ce maki duk abin da ki ka yanke zan yi ƙoƙarin mara maki baya a kai koda zan cutu."

Yanayin da ya ƙarasa zancen sai ta ji ya karyarmata da zuciya, ya kuma ba ta tausayi. Ta buɗe motar ta sauke ƙafafunta a waje, tana kallon waje ta ɗan waigo kaɗan idanunsa a kan gefen fuskarta da ya ga alamar murmushi ta ke, ta soma magana. 

"In sha Allahu Yaya ba za ka taɓa cutuwa ba idan daga gare ni ce. Amsarka ita ce eh, na yarda na amince da kai. Ina roƙon Allah ya tabbatarmana da dukkan alheri a tsakaninmu."

Ta na kai wa nan ta fice da sauri ta rufe motar, ba ta ko kalle shi ba ta cigaba da tafiyarta, shi kuwa Sadauki hamdala ya shiga yi na nuna jin dadi da godiya ga Allah da ya amsa roƙonsa. Kalamanta suka cigaba da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login