Showing 159001 words to 162000 words out of 177840 words

Chapter 54 - FITAR TSIRO COMPLETE HAUSA NOVEL BY RUFAIDA UMAR

11 Jul 2024

79162

suna haɗa idanu da darawa duka lokaci guda.

Maama ta girgiza kai ita ma tana dariya.

"To yanzu kan autar tawa za ki dawo?"

"Auta fa kika ce Maama? Ni dai a'a, muna jira ki kawo mana..."

Pillow ta jefa mata ba shiri Zaituna ta yi shiru tana ƙunshe dariyarta. Maama ta miƙe ta na fadin.

"Bari na sa yanzu a maida ki inda kika fito, ba za ki zo ki takura mana ba."

Nan ta bi bayanta tana roƙon ta yi hakuri. 

"Allah Sarki Anti Zaituna, wallahi ina mata sha'awar samun miji mai nagarta da zai riƙe mana ita hannu bibbiyu."

Faɗin Haulatu kenan tana bin bayan Maama da Zaituna da kallo cikin murmushi. Radiya ma ta ce

"In sha Allahu za ta samu. Ita yanda na kula, ta fi kaunar aure a ƙasarnan, ba ta son ɗan can."

"Mu ɗin ta ke ƙauna, tana son zuri'arta ne ina ga shi ne babban dalilinta." Haulatu ta ba ta amsa.

***
A kwana a tashi...
A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah, har aka wayi gari sauran bai fi sati uku a sha bikin Sadauki da Haulatu ba.
  An fiddo ankon sisters daban da kuma na iyaye. Haulatu ba ta da wasu ƙawaye sai ko wasu abokan karatunta uku da suke mutunci sosai a makaranta, Fauziyya, Rumanatu da Sadiya. Sai ko aminanta kuma ƴan uwa Safina da Radiya, wannan yasa su biyar ɗin suka haɗe kai suka fidda ankonsu daban wanda za su saka ran dinnerparty da Sadauki ya ce zai shirya. Su biyar din kadai suka san da zaman ankon gudun ƙananan magana sai ko Zaituna da Maama wadanda ake yi a gabansu. Don Zaituna ma takanas ta dawo zama wurin Maama saboda ƙanwarta.

A yau ta kama Alhamis, ranar ce kuma za ta tattara ta koma gida. Maama ta yi mata iyakar yin ta, ta kuma kai ta wajen ƙawarta ƴar Senegal dake aure a Katsina ta mata nata gyaran har na tsawon sati biyu, jikin Haulatu har wani jaja-jaja yake ban da uban ƙamshi da ke tashi a jikinta. Ita kanta kuma daga yanayinta ta fahimci ba ƙaramin sauyi take ji ba, magunguna ne kala-kala an ba ta ta sha. Ta ci na ci ta kuma shanye romo.

Rabonta da su saka juna a idanunsu da Angon nata an fi sati biyu. Tun yana zuwa Maama na korarsa ta hana su ga juna har ya yi fushi ko ya zo gidan ba ya neman ya ganta. Ƙarshe ma ganin dagaske Maama take sai ya bar zuwa. Takaicinsa bai ƙaru ba sai da ya ga ko videocall ya kira ba ta so sam ba ta ɗagawa. Wannan abu ya sanya shi yin fushin da har ya yi tafiya Dubai bai mata sallama ba. Ita kuwa Haulatu jin da ta yi ya yi tafiya ranta ya yi mugun zafi, toh mene ne laifinta don ta bi huɗubar Maama? Ta dauka duka ana yi ne don ya ƙara musu shaƙuwa da juna.

Ko a yau da take faman haɗa kayanta na komawa babban gida sam fuskarta babu walwala. Damuwar rashin ji daga Sadaukinta yana cin ranta, gaba daya komai ya fita a kanta. A gaban Maama dakyar ta ke dannewa ta saki jiki a dinga hira. Sadauki bai taɓa nunawa Maama komai ba koda a waya hakan yasa ba ta fahimta ba. Zaituna ce ta shigo dakin tana amsa wayar Mamanta wacce za su taso daga Malaysia a gobe. Har ta kammala wayar Haulatu ba ta dube ta ba tana zaune gefen gadon riƙe da siket da take shirin ninkewa ta lula duniyar tunani.

Ganin kamar hankalinta ba ya wurin ya sa Zaituna kai hannunta saman nata wanda ya fargar da ita da sauri. Suna haɗa idanu sai ta sauke ajiyar zuciya gami da saurin miƙewa ta cigaba da ninkin kayan.

"Sis, kin bani tsoro fa. Har kin gama kallon?"

Fadin Haulatu ba tare da ta dubi fuskarta ba don ba ta so ta ga hawayen da ke kokarin zubo mata sai dai ina ta makaro, Zaituna ta riƙo hannunta ta zaunar a gefen gadon. Daidai sadda Haulatu ta share hawayen fuskarta.

"Meke faruwa ne? Har yanzu ba ku shirya ba?"

Tambayar da Zaitunar ta yi ya sanya ta dube ta da mamaki. Ɗan murmushi ta yi ta jinjina kai.

"Yes, na san ba kwa gaisawa da Yaya Sadauki, na san kun yi faɗa. Maama ta sha tambayata ko ina ganin kuna waya a ɗaki? Nakan amsa mata da eh don kawai na taya ki ɓoyon abin da kike gudun ta sani kar ranta ya ɓaci. Amma ni na sha ganinki kina hawaye da daddare. Me ya yi zafi har haka tsakaninku?"

Sai ta samu damar fayyace damuwarta, nan da nan ta labartawa Zaituna komai. Shiru ta yi tana sauraronta har ta kai aya kafin ta jefa mata tambaya.

"Kuma da ya yi fushin, ke ma sai ki ka bar yi masa magana? Ko kuwa kin kira shi?"

"Idan fa na kira ko ɗagawa ba ya yi tun ma kan ya tafi. Sannan ko text na yi ba ya ban amsa. Shi ne na watsar da shi nima."

Harararta Zaituna ta yi.

"Kin watsar da shi amma ai ga shi kina cutuwa. Ni dama ina ganin yanda Maama ke hana Yaya Sadauki ganinki na san ba zai haifar da ɗa mai ido ba. Ni ban ga wani amfaninsa ba."

Sai kawai ta miƙe tana ta faɗin bari ta sanar da Maama, ganin dagaske ta kama hanyar fita daga ɗakin ya sa Haulatu saurin miƙewa ta jawo ta.

"Aa Sis, don Allah kar mu yi haka. Wannan tsakaninmu ne, komai zai wuce. Kin ji?"

"Haka ki ke so ku ci gaba da zama babu mai kula wani a cikinku? Kinsan irin da matsalar hakan kan haifar?"

Haulatu ta girgiza kai tana dauke ruwan hawayenta.

Maama wacce ke kokarin shigowa ɗakin sai ta fasa ta juya, ta ji komai dake faruwa, dama zuwan da ta yi don ta kawowa Haulatun wata jarka da ta bari a cikin firij na tsumi. Komawa ta yi ta ajiye jarkar saman teburin dake tsakar falon ta zauna. Wato Sadauki abinda ya aikata kenan? To kada dai ace ta yi babban kuskure na hukuncin da ta yanke a kansu? Ita ta yi ne don a gaba ya ƙara jin matsuwa da son ganin matar tasa har ma da sabuwar ƙauna, ba wai don ya nisanta kansa daga gareta ba har haka. Ajiyar zuciya ya saki, gobe ne zai dawo daga Dubai, dama ya je tare da wasu abokan kasuwancinsa ne. Bari za ta yi ya dawo sannan ta yi mishi magana.

Ba ta kyale Haulatu haka ba sai da ta kira ta tare da Zaituna, rarrashinta ta yi gami da nunamata ainahin manufarta a kai. A karshe ta ce ta kwantar da hankalinta, ta yi hakuri kar ta neme shi tunda ya nuna ba zai saurare ta ba, ta bari har zuwa goben idan ya dawo daga tafiya. Sosai kuma sai ta samu nutsuwa da zantukan Maaman, ita da kanta ta kai su gida. Kowa ya ci karo da Haulatu ya ga yanda ta koma sai ya kama baki ya tanka kyawun da ta yi. Wai kamar ita ce ta yi rayuwar Malaysia din. Ita dai addu'ar kambun baka take yi a zuciya. Hajja ta washe haƙora.

"Dakyau Hauleta, Masha Allahu la kuwwata illah billahi. Ke ki dinga lahaula gudun baki kin ji ko? Kar ki yi wa kowa alkunya duk wanda bai ba ki yiwa kanki."

Mutan dakin suka saka dariya don tunda aka ga motar Maama, mutanen gidan aka yo caa zuwa wajen Hajja ganim fuskar Amarya. Har da masu gulmar son gani wane irin gyara ne Maamar ta ke mata da aka wani dauke ta daga gidan zuwa can. Fahima dake zaune a falon ko ci kanku ba ta ce ba. Sai ma ta miƙe ta yi sama abinta ba tare da kowa ya kula ba. Umma kuwa ba ta ce komai ba ban da murmushi, kwallar da suka cicciko mata a idanu ta share a faƙaice, a ƙasan ranta kuwa hamdala take yi ga Allah da ya sauya musu rayuwa daga wahala zuwa jin dadi. Fatanta a yanzu Allah ya nunamata auren ɗiyarta, ya sa a yi komai lafiya a kammala. Har Haulatu ta zo ta rungume ta ba ta bar kauda kai ba, Hajja na mata faɗa kan ta rage wannan jin nauyin ita ba ta son abu na mutan da. Ita ko Haulatu kai ta dora a cinyar Umman tana fidda hawaye masu zafi karshe ta fashe da kuka sosai, Umma ma ta shiga nata hawayen tana kallon gefe. Kowa da dalilinsa na kukan, ita Haulatu ga murnar wannan rana na tahowa da take tabbacin burin Ummanta ya kusa cika ga kuma na sauyin Sadauki da ke damunta koyaushe, ita kuwa Umma, baya kawai take tunawa tana cigaba da godewa Allah a ƙasan ranta. Nan aka shiga ban baki
Maama na janye Haulatun.

"Haba Na'imatu, ya za ki biyewa wannan a dinga wani koke-koke ana abin farin ciki da murna. To maza maida mayafinki mu koma gidana."

Jin haka ta shiga share fuskarta, baki a kumbure ta ce

"Na daina Maama." Aka yi dariya.

Sai da kowa ya watse sannan Radiya da Safina wacce ta zo gidan da zummar sai bayan biki, kuma babu inda ta yada zango sai ɓangaren Hajja, suka haɗu suka ƙulle a ɗaki. Hira suka shiga yi, Safina na labarta musu diramar da aka yi a daren jiya tsakanin Haj Hadiza, Fahima da kuma su Hajja.

"Wai fa Hajiya kuka sosai ta zo muna zaune ta shiga rerawa Hajja akan don Allah ta yafe mata. Hajja ba ta ko kalle ta ba nake fadamaki, shi ne ta koma ga Umma. Umma ce ta ce mata komai ya wuce. Dakyar dai Hajja ta saurari Hajiya ta ƙare da yi mata nasiha. Fahima ma har da neman gafara bayan Hajiya ta tirsasa ta. Ni dai jikina na bani tuban muzuru Fahima ta yi, amma Hajiyarta dai na ga alamar dagaske take ko ma dai ba duka ta sauya ba, kuka fa sosai har da su majina. Amma kuma ita ma kun san me?"

"Sai kin faɗa." Fadin Radiya da Haulatu har suna haɗa baki.

"Uhum, babanta ne zai haɗa Fahima aure da ɗan yayansa. A karshe dai Hajiya ke roƙon Hajja akan ta taimaka ta yiwa su Baba Alhaji magana su saka baki kar a yiwa yarinyarta auren dole. Hajja ta dinga yi mata faɗa akan ita babu abin da za ta ce, gwara ma a yi hakan ko Fahima za ta nutsu. A karshe Umma ce ta kashe wutar ta lallaɓa Hajja, dakyar dai ta ce a hakura zuwa bayan bikin Haulatu sai a yi maganar. Hajiya na ta ƙorafin wai yaron na shaye shaye, amma baban ya dage sai an yi, idan ya so tunda ita mace ce za ta iya juya shi ta maido shi hanyar tsira, ku ji fa?"

Girgiza kai Haulatu ta yi cike da takaici.

"Abin nan yana ci min tuwo a ƙwarya, sai ki ga namiji na tata duniyanci amma a dage mace wai sai ta aure shi a haka, amma da ace ita macen ke yin wadannan miyagun ayyukan da ta zama abar zagi da ƙyamata. Har ga Allah na tausayamata, ina addu'ar kar Allah ya tabbatar da wannan abin."

"Amin Haulatu, ni kaina ta ban tausayi, ba ku ga ma yanda ta dinga kuka ba daga baya, ba ta ji labarin haɗin auren ba sai da Hajiya ke faɗawa su Hajja. Ita dai Hajiya haka ta yiwa su Hajjar sallama ta tafi wai dama ta zo kawo Fahima ne don ba za ta yarda a yi mata aure da mashayi ba."

Murmushin takaici Haulatu ta yi, duniya kenan. Yau kuma Fahima ce ake son aurawa mashayi. Dole Hajiyarta ta fita hayyacinta.

"Allah ya magance mata." Abin da kawai ta ce kenan suka amsa da amin kafin su shiga hirarrakinsu. Daurewa kawai ta ke yi tana biye musu, ko kusa ba ta ba su labarin rikicin da suke ciki ba, hakanan ta ji tana son ɓoye sirrinta da Yayan nata. Zaituna ma don dai ta riga ta ɗago ta ne amma da ba abin da za ta ce.

***
Washegari misalin ƙarfe biyu da mintoci na rana, ana zaune ana hira a falon Hajja, Zaituna ta fito ciki shirinta na zuwa gyaran gashi. Don tace kitso take son yi da biki, wanken kan za ta a ranar. Mamanta ba su iso ba sai dare.

"To ke kadai babu ɗan rakiya?" Faɗin Umma kenan, Haulatu ta yi caraf ta miƙe zaune daga kishingiɗar da ta yi.

"Umma ko na raka ta?"

"Ina?" Fadin Hajja da Umma lokaci guda. Jin yadda suka haɗe baki kamar ta faɗi wani abin gudun sai suka ma ba ta dariya, Hajjah ta ce.

"Kin ga ki yi shiru da bakinki, so ki ke yau Zakiyya ta mana dirar mikiya. Koda dai, Sadaukin Alhaji uban ƴan kishi sai ya wanke ni ba shiri. Babu inda za ki je."

"Toh Hajja ita kaɗai za ta tafi? Ga Safina na makaranta. Sis ki saka baki please." Ta ƙarashe tana narke fuska kamar ta yi kuka.

Murmushi Zaituna ta yi.

"Aa fa, babu ruwana. Dama ya lafiyar kura? Bari na tafi kawai, zan leƙa can wurin Momi Nuratu sai na ja Zuhra ta min rakiya."

"Shikenan kuwa. Hakan ma ya fi. Sai kun dawo." Hajja ta amsa. Babu wanda ya yi maganar Fahima sakamakon matsalarta da ake kokarin magancewa don Baba Alhaji ya yi waya da mahaifinta ya nemi alfarma akan ya zo yana son ganinsa.

Ta juya tana ɗagawa Haulatun yatsunta uku tana mata dariyar mugunta. Haulatu ta kauda kai kawai gami da komawa ta kwanta. Ta sani yau Sadaukinta zai dawo, tun safe take baza idanu da kunnuwa ko za ta ji labarin ya shigo Katsina daga Kano amma shiru. Hankalinta gaba daya yana kansa ta kasa sukuni duk kuwa da ba maganar ke haɗa su ba.

***
Zaituna na fitowa ba ta wani yi nisa ba, tana takunta cike da nutsuwa cikin shigar doguwar rigar abaya maroon da ya karɓi fatarta sosai, ranar a yau ta buɗe ba kaɗan ba, don haka sai ta ke tafiyar a hankali. Ɗagowar da za ta yi ta hangi Khaleefa na takowa ya fito daga ɓangaren Baba Dakta, sanye cikin shadda sky blue sai ko hula a kansa. Ya yi tsaf abinsa cikin shigar juma'a. Bisa al'adarsa duk rana ta juma'a ba ya komawa gida sai ya shigo gaida iyayensa. A hankali ta sauke idanunta daga gareshi ganin bai bar kallonta ba.

"Barka da juma'a Abu Affan, fatan an yini lafiya?"

Ya sauke ajiyar zuciya, tun sadda ta zo garin ba su ƙara haɗuwa ba sai yau. Zai iya cewa kwanakin nan tana ransa, ya kuma kasa cire tunaninta a kwakwalwarsa, Hafsat ba ta ko sakaya sunansa, kai tsaye Khaleefa ta ke ce mishi amma ba ta ambaton sunansa na yanka. Sai dai yana son girmamawa, bai dai taɓa hana ta faɗin abin da ta yi niyya ba.

"Lafiya. Ya su Hajja?"

Da murmushin jin dadin ya amsa mata ta kara kallonsa ta ce.

"Lafiyarsu kalau."

Ga mamakinta murmushi ya yi mata, baki ta saki tana kallonsa. Za ta iya rantsuwa bai taɓa yi mata murmushi ba sai dai ta hango yana yi ga wasu.

"Masha Allah. Fita za ki yi?"

Tambayar ta ƙara lula ta cikin duniyar farin ciki, ita kadai ta san meke cin zuciyarta kwanakin nan sai dai ba ta son maimaita tarihi dalili kenan da yasa ta ke kwaɓar kanta tana kuma ƙaryata kanta da gangan.

"Eh, zan je saloon. Zuhra zan kira ta yi min rakiya."

Ya soma tafiya yana amsa mata.

"Ok. Allah ya tsare. A dawo lafiya."

Daga haka ya wuce ta zuwa sashen Hajja, ita kuwa ta amsa da amin da godiya tana mai binsa da kallo har ya gifta ta, kowannensu ya shaƙi ƙamshin turaren ɗan uwansa, Zaituna ta sauke ajiyar zuciya ta ɗan waiga ta dube shi sannan ta juya ta cigaba da tafiya har a lokacin ba ta bar murmusawa ba ga kuma gefe guda da mamaki ya cika ta. Wai Yaya Khaleefa ke mata murmushi?

***
Misalin ƙarfe bakwai na yammaci, Sadauki ya shigo garin Katsina. Mu'az wanda ya je ɗauko shi, shi ke tuƙi yayinda shi kuma ke bin garin da kallo yana ji a ransa babu abin da ya fi kewa a ciki kamar Haulatu. Ƴan kwanakin da ya yi a ƙasar waje, ya samu ya yi haske sai ɗan rama kaɗan wanda rashin ji da ganin masoyiyar tasa suka haifar. Babu wani abu da ya yi mishi dadi a tafiyar idan ka cire hotunanta da yake kallo ya ke jin ɗan sanyi a ruhinsa. Ya yanke zai je har gidan Maama, idan ta kama zai kai gwuiwoyinsa ƙasa akan kawai ta bar shi ya yi tozali da Haulatu, ta bar shi ya ji koda muryarta ne har ta yi mishi murmushin nan mai wanke zuciyarsa.

"Gidan Maama za ka kai ni."

Mu'az ya ji maganar kamar daga sama don ya ma fidda ran za su yi wata hira da Sadaukin tunda gaba daya ba su yi wata magana mai tsawo ba, ya kuma kula kamar akwai abin da ke damunsa. Sai dai maganar da ya yi ya ankarar da shi damuwar don haka ya yi murmushi.

"Idan dai Haulatun Hajja ka ke son gani, tana cikin gida. Ta dawo jiya."

Ya ɗan ji nauyi amma ya basar.

"Akwai kayan da zan so na kai wa Maama, amma muje kawai zuwa gobe sai na je."

Shi dai Mu'az toh kawai yace yana murmushi, wai shi za'a yiwa wayo kamar wani ƙaramin yaro.

Madadin su wuce ɓangarensu, sai ya ce ya tsaya a nan parking space na babban gidan. Ya ce Mu'az ya wuce masa da kayan can ɓangarensu shi zai je ga Baba Alhaji. Mu'az nan ma toh ne na shi, ya yi gaba, Sadauki ko kai tsaye ya nufi ɓangaren Hajja, ya sani shi mai laifi ne ya kuma shirya karɓar kowane hukunci daga Bebin tasa.

***
Fitowarta kenan daga kicin, sanye da tshirt fara da siket da bai matse ta ba pink. Sai ko ɗan ƙaramin ɗankwali pink da ta rufe gashinta. Ƙafarta sanye da safa, don Maama ta ce duk inda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login