Showing 3001 words to 6000 words out of 157517 words
Madina ta na raye, gashi Allah yayi haɗuwarmu da tsatsonta kafin ita, amma wannan miji nata Allah yayi mugu wallahi sai ya san ya taɓo ƴar asali!”
Hanci ta fyace ta cigaba “Garba, Umaru, Usmanu, Gadanga, Muhammadu da kai Yusufu don Allah a ƙara ƙaimi wurin sanar da jama'a da kuma jami'ai har Allah yasa Madina ta dawo gare ni”.
Kowa jimami yake yi kuma jikin kow yayi sanyi sai dai ganin halin da Hajjaty ke shirin saka kanta yasa suka ɗan kawar da damuwarsu duk da cewa yanayinsu dama saisaitacce ne tunda sun samu tabbacin Madinar na raye.
Daddy wanda duk cikinsu yafi zafi ya ce “Tabbas wannan miji na Madina ya cutar da ruhikanmu, Wallahi sai ya san ya taɓo jinin ABATCHA, sai ya san ya taɓo ƴar Babban gida!”
Dafa shi Alhaji Baba yayi shima yana ƙoƙarin kawar da tasa damuwar
“Ya isa haka Umaru, ka kwantar da hankalinka yanzu abu mai muhimmanci shine kau haɗa kai ku bada himma a nemo Madina, shi kuma mijin daga baya ma san yadda zamu yi da shi.
Shawarar da Alhaji Baba ya basu kowa yayi na'am da ita, nan Alhaji Babba ya murmusa ya ce “Yaki yarinyar kirki, zo jikin babban uba ko?” cike da matsananciyar kunyarsu ta taho garesa, rungume ta yayi sannan ya sumbaci kanta kafin ya ce “Photocopyn Madina, Allah yayi Miki albarka Zahra'u.” da “Amin” Zahrar ta amsa kafin ta nufi sauran jama'ar da ke Parlourn suma ta kwashi albarka. Kasancewar lokacin sallah ya ƙarato daga nan aka rufe ɗan ƙaramin zaman da Addu'a, nan mazan suka fice zuwa mosque da ke cikin estate ɗin.
Ko da suka fita Hajjaty da fara'a ta ƙara rungume Zahrar, tsawon wasu daƙiƙu kafin ta sake ta tana tsura mata ido. Cikin ranta tana ƙara tausayawa rayuwar da ahalinta da Kuma bar soyuwarta Madina tayi, sai kawai ta yi murmushi cike da son kawar da damuwarta ta ce “Muje can ɗaki na kiyi Salla Zahrah, idan Laraba ta zo ta kwaso Miki kayanki” Kan Zahrah ƙasa ta ce “To Mama” Hararar wasa Hajjaty tayi mata tana riƙe da hannunta tace “ki ƙira ni Hajjaty kamar yadda kowa cikin estate ɗin nan ke kira na, kinji?”
“Eh Hajjaty ” ta bata amsa har lokacin bata sake ba.
Sallarta ta maghrib ta gabatar shimfiɗa ɗaya da Hajjaty, zuciyarsu tana ƙara kusantuwa da juna, bayan sunyi Sallar Hajjaty ta fara ɗauke Zahrah da zance, tun tana bata amsa a kunyace har dai ta sake suna Hira, ko da Alhaji Baba ya dawo, babban Parlourn sa suka wuce kamar yadda Hajjaty ke yi koyaushe. A nan dai Zahra ta saki jiki da ƴan kakannin nata da suka fara mantar da ita duniyar ta hanyar ɗumbun kulawa da so da suke nuna mata cikin sa'o'i ƙalilan.
Wannan kenan.
Lokacin Isha da yayi ne Alhaji Baba ya fita daga gidan zuwa Masjid tare da rakiyar Daddy. Su Zahra a nan suka yi sallar su kowa ya nuna godiyar sa ga Ubangiji, nan suka yi addu'a Allah ya bayyana Mama. Ko sallayar basu naɗe ba Maid ɗin Hajjaty, Laraba, ta shigo hannunta ɗauke da wani dogon tray wanda ke shaƙe da kuloli shaƙe da. Kuma jugs.
Tana gama jerawa ta fice, few minutes ta dawo da wasu kulolin ta jera, ta zo fita Hajjaty ta dakatar da ita “Laraba, in kin fita ki ɗauko kayan zahra ki mayar da su can ɗaki na”
Cike da girmamawa Laraba ta amsa mata da faɗin “To Hajiya, yanzu ma”. Daga haka ta fice.
Tsawon wasu daƙiƙu, misalin 7:23pm suka yi sallama zuwa parlourn, saɓanin fitarsu ɗazu su biyu, wannan karan tare da wasu samari kyawawa guda huɗu, Daddy kuma baya cikinsu. Da sallama suka shigo fuska sake. Alhaji Baba zama yayi a kan kujerarsa su kuma suka zauna ƙasa kamar yadda Zahrah da Hajjaty ke zaune.
Cikin samarin ne ɗaya ya kalli Hajjaty fuska sake yace “Barka da dare Hajjaty”
Suma sauran suka gaishe ta, kamar yadda yanayin fuskarsu yake haka ta amsa musu tana murmushi “Lafiya ƙalau yaran nan” sai kuma ta haɗe gida kamar ba ita ce ke cikin fara'a daƙiƙu kaɗan da suka gabata ba.
“Duk nayi fushi da ku, tsawon jiya shiru shiru babu wanda ya leƙo cikinku, ƴar gaisuwar safiyar nan ma babu wanda ya leƙo saboda kun maida Ni mutuniyar banza” su dai kallon Hajjatyn kawai suke suna kwaɓe fuskokinsu ba tare da sun katse ta ba.
“Amma iyayen ku da ke da daraja ai kun shiga kun gaida su ko?”
Gaban Hajjatyn suka dawo tare da durƙusawa ƙasa, fuskar tausayi suka yi cikin haɗin baki suka ce “Haba tsohuwa mai ran ƙarfe, uwar gida sarautar mata a gidan tsoho mai ran ƙarfe, ki yi wa ƴan jikokin ki haƙuri ba zasu kara ba.”
Ɗan sakin fuakarta kaɗan tayi ta ce “Ai yau ba zan yi haƙuri ba, nasan da yarin kirkin nan Mahiru na nan da ban shaƙi takaicin ku ba, shi kafin ya gaida iyayensa sai yazo ya duba lafiya ta, Allah sarki mahiru.”
Ƙara kwaɓe fuska suka yi kamar zasu yi kuka, kamar haɗin baki kuma suka kama kunnuwansu suna faɗin “Ayi mana afuwa Hajjatyn mu”. Dariya sosai Hajjaty tayi, su dai da mamaki suke kallonta though sun San halinta, lokaci ɗaya in ta birkice kamar ba zata dawo dai-dai ba, sai kuma kuga ta dawo unexpected. Shiru Hajjatyn tayi tana kallonsu tana murmushi ta ce “Shikenan yaran kirki, kun ci albarkacin yau ina cikin farin ciki na haƙura” fuska sake ta yadda zaka fahimci ainihin farin cikin da suka yi da jin zancenta suka ce “Mun gode Hajjaty tamu abar ƙaunarmu”
Alhaji Baba da ke kallonsu sosai suka burge shi, yana ƙara alfahari da jikokinsa saboda ɗa'a da biyayya da suke da shi, sai kuma ya kai duban sa ga Zahrah wacce kanta ke ƙasa tun shigowar samarin, ganin she's uncomfortable yasa ya buɗe baki zai yi magana sai Muryar ɗaya daga cikin samarin ta katse masa hnazari.
“Hajjaty farin cikin menene wannan ya ƙwacemu daga fushinki mu taya ki celebrating?”
Kallonta ta mayar ga zaharh da ke gabanta, sai kuma ta jawo ta jikinta, su ma a lokacin idanuwansu ya kai kanta, sai dai sun yi mamakin ganin ƴar matashiyar budurwa tare da Hajjaty.
Hajjaty ta ɗago kan Zahrah tana dubanta, ba tare da t kallesu ba ta ce “Albarkacin jika ta daga gudan jini na Madina”
Da mamaki suka kalleta, in basu manta ba kullum sai Hajjaty tayi magana kan Madina da take cewa ɗiyarta ce auta da ta ɓata tsawon wasu shekaru. Ganin rashin fahimta shimfiɗe kan fuskarsu yasa Hajjaty tayi gyaran murya tana faɗin “Ɗiyar Madina ne yau Allah ya kawo ta cikin ahalin nan, Zahra'u” ɗagowa Zaharah tayi tana duban Hajjaty, har lokacin idonta bai kuskura ya kai kan samarin ba. “Kinga ga yayunki nan, ku kuma ga Zahrah ƙanwarku, gobe zaku ƙara saninta, in kun fita ma ku sanar da sauran ƴaƴan akwai taro gobe”.
A tsorace Zahrah ta dube su sai kuma ta sunkuyar da kai saboda kwarjin da suka yi mata, ga kuma kyau da Allah yayi musu kamar me. “Ina yinin ku” ta faɗa cikin rawar murya. Tare suka amsa da lafiya, mai surutun cikinsu ne ya ce “Sannu Zahrah, muna matuƙar farin ciki da dawowarki cikin ƴan uwanki, fatan zaki karɓe mu hannu bibbiyu, mu dai nan muna farin ciki da zuwanki, ɗago ki kalle mu matsayin ƴan uwa na farko da kika fara gani” ya Idasa cikin sigar zolaya.
Ɗagowa tayi ganin basu nuna wani ƙyama gare ta ba kamar yadda da tayi zato.
Cikin sakin fuska yace “Suna na Auwab..” “Ni kuma Aufa...” Ni kuma Tajuddeen” sai kuma Ni “Faruq” murmushi tayi tace “Na gane fuskokin ku, sunayenku masu daɗi” cike da zolaya Ya Auwab ya ce “Ke fa bamu san naki sunan ba”
“Zahrah” ta basu amsa tana murmushi. Ta matuƙar burge su, ga ta kyakkyawa son kowa, ko maƙiyi ba ya kushe ba, ita ma bata ɓangaren tunanin kirkinsu take tana addu'ar Allah dai yasa sauran family members ɗin su kasance haka.
Ƴar hira suka fara janta da shi saboda ta ɗan ƙara sakewa da su, ganin sun ware kansu yasa Hajjaty faɗin “Ku tashi kuyi dinner Ku bar min jika, daga zuwan ku kuna shirin ƙwace min ita!”
Ya Aufa ya ce “Kai Hajjaty ki bar mu mu gana da ƴar uwarmu mana”
Danƙwalo ta kai masa ta ce “Ungo nan!, kai Auwabu ka kiyaye Ni, ku tashi nan ayi dinner.”
Gabaɗayansu miƙewa suka yi zuwa dining ɗin kowa ya nemi wuri ya zauna, ita dai Zahrah sai rarraba ido take tana ganin ikon Allah, Hajjaty da kanta ta samar mata waje daga nan ta fara serving nasu, ta can ƙasan idon Zahrah ke dubanta tana kula da yadda take komai.
Tunda suka fara cin abincin shiru ya wanzu, ƙarar spoons da ke arangama da plates kawai kake ji. She's not comfortable eating with them shiyasa tana cin kaɗan ta dakata, tatar kallon Ya Taj tayi ganin shima ya ajiye spoon ya yago tissue ya goge baki yasa ita ma tayi kamar yadda yayi.
Hajjaty ta dube ta ta ce “Zahrah ya bakya ci” a hankali don bata son sauran suji bare su ce sai ta ci tace “Naci, har na ƙishi”
“kin sha abun shan ne?” Hajjaty ta ƙara tambayarta “A'a Hajjaty” Hajjaty da kanta ta tsiyaya mata zoɓon tasha.
Bayan sun gama ci nan aka ci gaba da hira, tuni Zahrah ta gama sakin jiki da su, meanwhile Ya Faruq ya tura musu saƙon Hajjaty na meeting gobe. Da misalin tara saura su Ya Taj suka yi sallama suka wuce, Hajjaty ma ta ce Zahrah ta taso su kwanta. Sai da suka yi wanka tare da alwala suka yi shafa'i da witri. Hajjaty na zaune kan sallayar ta ta ce ma Zahrah ta je ta kwanta, babu musu ta haye makeken gadon Hajjaty, ita kuma Hajjaty sai da ta gama laziminta ita ma ta nemi wurin bacci.
Safiya mai albarka Zahrah and Hajjaty.
Fatann rayuwar farin ciki tare da Abatcha family.
_Sallar Shafa'i da Witri salloli ne da manzon Allah (S.A.W) ya bayyana cewa: « gara a baka damar yin Shafa'i da Witri akan a baka duniya da duk abinda yake cikin ta» , shiyasa manzon Allah kullum yana yin Shafa'i da Witri koda yana halin tafiya yana yin su.
Karanta Sunanut Tirmiziy, Hadisi na 425._
_Zaku samu cikakken bayani kan yadda ake yin ta a channel ɗina_
★★★★★★★★★★★★
_Me kuke tunani game da rayuwar wanan ahali?, me ake aikatawa a babban gidan nan ne?, shin kuna ganin rayuwar Zahrah ta samu Salama kenan?, ina Mama ne? Ko da gaske ta mutu?, Amsoshinku na ɗaure da alƙalamin Diamond Bhatool 💎, Diamond Bhatool 💎 taku ce!👍😍_
*Vote, comment, react and share Fisabilillah!*
*Vote, comment, react and share Fisabilillah!*
[13/10, 12:12 p.m.] 💎Diamond Bhatool 💎:
*Typing 📲*
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family 🏠)_
★TAKUN ƘARSHE★
[Labari/Rubutawa]
*Fadimatu Adamu Hassan*💎
*A.k.A Diamond Bhatool*
*(Famanté)*
Wattpad: @diamond_bhatool
Arewabooks: @diamondbhatool
_Ƙirƙirarren labari mai cike da ƴan'uwantaka, gwagwarmayar rayuwa, makirci, mugunta, hassada, munafurci, rashin tausayi da kuma dauwamammiyar soyayya maras iyaka_
_Creative work of love vs. societal expectations., family bonds and loyalty, Identity and self-acceptance, Hypocrisy and jealousy's destructive power._
*Masu Neman labarin daga farko, kuyi following channel ɗina.**
*Chapter 2: People only managed to smile, nobody know how they're really hurting deep down*
*PAGE* 0️⃣3️⃣
_Sadaukarwa gare ku mutanen channel ɗina *Diamond Bhatool's library*, ina godiya da ƙaunar ku gare ni._
_Ban manta da ke ba Maryam Muhammad, ƙauna ta ta musamman, ina godiya ƙwarai
*1:00 midnight*
*Unknown location but a black wilderness*
Cikin ƙasurgumin baƙin dajin wanda tsabar duhunsa ko tafin hannayenka baka iya gani, duhun wannan daji ya wuce misali, ya wuce siffantawa ga tunanin mai karatu, amma zan iya cewa duhu ne da ba lallai bil'adama ya taɓa cin karo da kwatankwacinsa ba.
Cikin ƙankanin lokaci kuma kamar tsafi sai ga haske ya bayyana kamar safiya irin rana ta fara hudowa. Kamar ƙiftawar ido sai hasken ya ɗauke wurin ya koma kamar dai dare, amma akwai haske though bai wadata ba amma mutum kan iya ganin tafin hannunsa. Kamar daga sama kuma wani irin mummunan sauti maras daɗin amo da sauraro ya fara cika jejin, a hankali kuma sautin na ƙara kusantowa i zuwa tsakiyar wani fili wanda ke ɗauke da bishiyoyi biyu a jere, ƙatuwar bishiyar kuka ne sai kuma ta tsamiya a gefenta wacce ke da duhu kamar wani kurmi.
Tsawon wasu daƙiƙu wasu halittu da zasu kai kimanin Goma sha biyar suka bayyana, ko kaɗan basu da daɗin kallo, siffarsu tayi kama da ta goggon biri saboda gashin da ya lulluɓe fatarsu. Tsarin kama ma dai basu da maraba da goggon biri sai dai haƙwarensu zaƙo-zaƙo ne baƙaƙa da su har abun tsoro. Daga cikin waɗannan halittu wanda suke bisa tsari, wani yafi wani girma, haka wani ya fi wani. Babban cikinsu ne ya zauna can nesa da da sauran waɗanda suke hallare a wuri ɗaya, hakan zai ƙara tabbatar maka da cewa shi ɗin na musamman ne.
Wani irin sauti mai rikitar da tunanin bil'adama ne ya fara fitowa yayin da waɗannan halittu suka miƙe tsaye suna jujjuyawa kamar wanda suka shiga filin rawa. Can kuma sai ga wata walƙiya mai mugun gaske da ta haska illahirin dajin. Lokaci ɗaya waɗannan halittu suka nutsu, wasu baƙaƙen kujeru da ba zaka iya tantance da ƙarfe ko roba aka yi su ba suka bayyana a bayan kowa, nan suka zauna damas yayin da wannan halitta ɗaya dake gefe wata narkekiyar kujera ta iso bayanta, ita ma zama tayi, nan dai halittun suka fara wani kuka wanda zamu iya siffanta shi da Yaren da suke yi. Can bayan wasu daƙiƙu shiru ya wanzu.
Kwatsam!, babu zato ba tsammani wannan shugaban da ba zamu iya tantance jinsinsa ba ya fara magana irin ta mutane, abun al'ajabi ma a wurin cikin harshen Hausa. Muryar dai irin ta mutane ce amma tana fitar da wani amo na musamman wanda ke bada sauti bibbiyu kamar dai echo.
“Jinjina ga Gutsirito dodon tsafi! Jinjina ga Gutsirito dodon tsafi! Jinjina ga Gutsirito dodon tsafi!!!”
A tare su ma suka amsa da “Jinjina! Jinjina!”.
Shiru suka yi sannan shugaban ya ɗaura da faɗin “Ba komai ya tara mu a wannan waje ba sai don wata muhimmiyar sanarwa da nake son kai wa gare ku a matsayi na ta uwargijiyarku!”
“Jinjina! Jinjina!!!” suka amsa mata cikin haɗin baki tare da ɗaga hannayensu masu ɗauke da Zara Zaran faratu masu kama da duwatsu baƙaƙe ƙirin da su.
“Akwai wata masifa da ke tunkaro wannan ƙungiya ta Devil Klans 👿, Wanda idan muka yi sake zamu iya rasa dama da ta rage mana, ƙarfin tsafi da muke da shi a duniya zai raunana, zamu rasa ikon mu! Kai mu kanmu in wannan masifa muka barta ta iso akwai tashin hankali! Don kuwa sauran ƙungiyoyi zasu yi ta kawo mana farmaki yayin da mu kuma bamu da ƙarfin kare kan mu, ku sani in dai bamu tsayar da ita ba to kowa zai yi galaba a kan Devil Klans 👿!”
Surutunsu ne sama sama ke ɗan tashi yayin da shugaba wacce ta ambaci kanta da uwargijiya tayi tsit tana jira ta ji daga gare su.
Ganin lokaci na ƙure musu gashi babu wanda ya faɗi wani abu yasa ta buga sandar da ke hannunta a ƙasa, wani irin sauti da sandar ta bayar tare da fidda tartsatsin wuta yasa dukkansu yin shiru. Magana ta fara tana faɗin “Ina jira daga gare ku, Ɓurum me zaka ce?” ta idasa tana nuna wanda ke a farko ta ɓangaren hagu.
Ƙasa yayi da kai sannan ya sauƙo tare da sujjada a gabanta kana ya ɗago, cike da girmamawa ya ce “Uwargijiya ki ƙara mana haske a kai, wace irin masifa ce haka ke tunkarar tawagar mu?”
Ba tare da ta kalle shi ba tana mai ɗaura jafarta kan ɗaya ta ce “Ɓurum yayi abunda ya dace! Dodon tsafi yana alfari da kai” ta faɗa tana ɗaura hannunta kan goshi.
“To bari nayi muku filla filla, ɗazu na gana da Shastuna Aminiya ta wacce ita ma shahararriya ce a duniyar tsafi shine take sanar da Ni cewa haske na ya fara disashewa! Idan nayi wasa kuma kungiyar mu na shirin halaka!.
A tsorace na koma gida bisa mayafin tsafi kai tsaye fada ta da ta kasance ta sirri na shiga, ina buɗe madubin tsafi a nan na tabbatar, akwai wasu haske guda biyu da ke shirin tunkaro mu, sai dai kuma duk hanyar da zan bi na gano jinsin waɗannan haske ya faskara, abun da dai na gano shine ɗaya na ƙarfafan ɗaya ne, kuma waɗannan ruhi biyu suna gab da ƙarasowa gaban mu, idan bamu dakatar da su ba kuma za'a samu matsala, ya kamata tun wuri mu toshe duk wata hanya da zata sada mu da su, mu rufe kowacce kafa da zata basu damar tunƙarar baƙin daji. Dodon tsafi na a tare da mu!” ta ƙarasa tana ɗaga murya wacce sautin ta ke fita kusan takwas takwas from every direction.
“Ye! Dodon tsafi na a tare da mu!”
Suka haɗa baki suna bata amsa. Cike da jarumta ɗaya daga cikinsu tace “Tabbas dole mu tsinkayo wannan ruhika guda biyu sannan mu datse gudirinsu ga Devil Klans 👿 cikin ikon Gutsirito dodon tsafi!, amma kafin nan, ya ke uwargijiya!” sai ya yi sujjada gabanta ya tashi “Ki bamu dama mu mu bincika daga nan sai a san yadda za'a ɓullowa al'amarin. Gobe in an fito meeting sai kowa ya faɗi ya yake tunanin zamu yi, in so samu ne ma a ce kowa yayi matsanancin bincike mu gano waɗannan ruhika biyu kafin mu ɗau mataki kan su!”
Cike da gamsuwa uwargija ta furta “Dodon tsafi ya ƙara kasancewa tare da kai Muƙal! Ka cika magajin Devil Klans 👿, Ka ƙara ƙaimi wajen ƙara gina kanka, dodon tsafi zai