Showing 180001 words to 183000 words out of 210924 words

Chapter 61 - ZUBAIDA COMPLETE HAUSA NOVEL

EYSHAAT   

30 Aug 2024

22920

yayi yana kallon sa ba tareda ya iya furta koda kalma ba..

***************

*Fadah*

"Yau ta kasance babban rana ga d'aukacin wann masarauta, rana ce wacce ta shafe bak'in tarihin da ya auku shekaru 26 da suka wuce, rana ce wacce ta kafa d'inbin tarihi..

"Sanda Jalal ya saka k'afar sa ta dama da niyyan shiga gidan, hawaye ne ya shiga gangaro masa, bai tab'a tunanin rana irin wann zata zo ba...
"Tun daga waje ake zube masu ana mik'a gaisuwa, ga fadawan da suka soma hangosa daga waje, zubewa kawai suke cike da mamaki sunai masa fadanci, wann fuska tasa ko ba'a fad'a ba Ahali Lamid'o ne, d'aya ne daga cikin iyalan Sarki Lamido na uku mai rasuwa..

"Gaba d'aya Jalal ji yayi zai iya zubewa a k'asa sabida yanda yake ji a jikinsa, yau gashi nan, a gidan su kuma mahaifar sa... Shattima ya lura da hakan yayi saurin rik'e sa, duk bafajen da ya gaishe su, Shattima ne ke k'ok'arin amsa su...

"Sanda suka saka k'afar su a babban gwani, wato babban parlorn Mai Marataba Sarki Aliyu Mu'allayid'i Lamid'o na goma sha uku.... Allahu akbar gaba d'aya mik'ewa fadah tayi, su Waziri, su Hakimi, su Ajiya, kai gaba d'aya king makers manya manyan sarakunan gargajiya mik'ewa sukayi, tabbas wann Lamid'o ne ya bayyana, hawaye ya shiga bin fuskar Baba Waziri sanda ya hangi Shattima da Jalal suna takowa...


"Mai Martaba ya kasa daina murmushi jin dad'i da yake, yau ga Modibbo ya dawo mahaifar sa, yau Allah Ya cika masa burin sa.
"A yayinda hankulan mutane yayi kan Su Jalal a lokacin Mai Martaba ya zame ya kalli alk'ibla ya gabatar da sujudusshukri ga Rabbil Izza Sarkin da babu kamar sa Mai Mulkin sama da k'asa...

"Baba Waziri yana ganin Mai Martaba yayi haka, ya tabbata wann shakka babu Lamid'o ne, kk'arasawa yayi yana hawaye kafin ya rungume Jalal yana fad'in" Allahu Akbar Lamid'o ka dawo gidan ku...

"Wann furuci na Baba Waziri ya kuma karkata hankulan jama'an fadah dake cikin parlorn, nan kaji Fadah ta amsa lokaci guda, kan kace Me, Sank'ira ya soma shlela a cikin fadah cewa Lamid'o Modibbo ya dawo gida...


Sameena ce
[9:03PM, 2/6/2018] โ€ช+234 809 781 2439โ€ฌ: ๐ŸŒ˜๐ŸŒ˜๐ŸŒ˜๐ŸŒ˜ *ZUBAIDAH*

91


*ยฉSameena Aleeyou...โœ๐Ÿพ*

_๐ŸŒˆKWA_



*Dedicated To All Victims Of Rape...*





"Cikin Ummi gaba d'aya ya d'uri ruwa, k'irjinta sai dukan tara tara yake. Lamid'o a gidan nan... Kai kodai ba daidai taji ba..
"Jakadiya ta kuma rusunawa murya na rawa ta maimaita mata sak'on Mai Martaba.
"Zufa ya shiga keto ma Ummi ta ko ina, wayyo Allahn ta bata tab'a nadaman abubuwan da tayi a rayuwar ta kamar yau ba.. Ina ma bata bari ya kashe Suhaima ba, ina ma bata jefar da Lamid'o ba, kaicon ta, ina zata kai wann tarin danasanin... "Tsawa ta daka wa Jakadiya ta shiga zagaye katafaren d'akin nata tana mai Zullumin fita, don kuwa k'iris ya rage k'irjinta bai tarwatse ba..


"Hannun Madaki Zahida ta rik'e tana goge mata hawayen ta tana murmushi kafin taci gaba da fad'in" Ya dawo, ya dawo Madaki, Modibbo ya dawo gare mu..
"Tsohuwa Madaki kallon Zahida kawai take ba tareda ta fahimci komai ba, k'arasawa tayi ta d'au hoton sa dake ajiye saman Chase of drawers ta shiga shafawa tana fad'in" Shekaru ashirin da shida kenan rabon mu dashi, shekaru ashirin da shida kenn da b'acewar sa, anya kuwa Fatima kinji da kyau....
"Zahidah ta kuma rik'o hannun ta hawaye na Bin idanun ta amma murmushi take kafin tace " Mai Babban d'aki naji da kyau, shiyasa ma Abbah ya turo a tafi da ke cikin fadah ki gansa.... Zaki sake ganin jikan ki da a kullum kike kwana kike tashi dashi....

"Shattima ya k'araso yana murmushi yake kallon Zahidah kafin ya rik'o hannun Madaki guda yace " Muje Mai Babban d'aki, muje kiga Modibbon ki...

"Madaki ta d'ago ta kalle su su duka biyu hawaye na neman b'alle mata suka soma tafiya a tare, Shattima na rik'e da hannun ta na dama yayinda Zahidah ke rik'e da hannun ta na hagu...
"A haka Khalifa ya hange su, zuciyar sa ta shiga masa zogi, tausayin kansa ya cika masa zuciya, wann wani irin al'amari ne, Modibbo ya dawo masarautar nan wanda hakan na nufin babu shi babu sarauta, snn Zahida bazata tab'a son sa ba, tuni tayi nisa da soyayyar wanin sa, mahaifin sa ya dawo daga jinya babu baki babu k'afafu, meyasa rayuwa ta kasance haka.... Kasa komawa cikin Fadah yayi ya nufi hanyar fita...

"Shafa fuskan sa take hawaye na gangaro mata, yayinda shima hawayen ne ke bin k'uncin sa, Kuka sosai ya b'arke ma Dattijiuwa Madaki, rungume ta Jalal yayi ba tareda ya iya furta koda kalma ba...
"Zahida ta kuma damk'e hannun Zubaidah tana jin har ranta take k'aunar ta...
"Madaki ta soma maganganu cikin harshen fillanci tana godiya ma Allah.
"Allah sarki hak'ik'a yau rana ce wacce bazata tab'a shafewa ba a tarihin masarautar...

"Ba zallan Fadah kawai ba harta garin gaba d'aya labari ya d'auka, long lost son d'in Mai Martaba ya dawo..
"Wann labari ya haifar da farin ciki ma d'aukacin mutanen garin..

"Gaba d'aya Dattijuwa Madaki ta kasa sakin jikan nata, haka ta rik'e hannayen su k'amk'am shida Zubaidah,.


"Baba Ciroma zaune saman wheelchair d'insa, ya sami kariya sosai a k'ashin bayar sa, snn sun masa lahani wajen sauraren magana da maidawa, a tak'aice dai likita yace zai d'au lokaci watak'ila mai tsawo kafin ya warke watak'ila kuma Ya iya warkewa a 'yan kwanakin nan, abin dai na Allah ne sai yanda ya gudanar da Al'amran sa..
"A b'angaren Ummi kuwa hakan ba k'aramin dad'i ya mata ba, Kai Allah ma yasa ya tabbata a haka, tunda hakan na nufin rufuwar asirin ta.
"Ummi harda hawayen ta sanda ta k'arasa ta rungumi Jalal, wanda mutane sun zata na farin ciki ne, amma kuwa ita kanta batasan hawayen Me take ba, walau na bak'in ciki ne ko kuwa na tsoro da fargaban abinda ka iya zuwa yazo....
"Harta Zubaidah saida Ummi ta rungume ta tana mai nuna farin ciki..
"Baba Ciroma kuwa kallon ta kurum yake babu halin magana.
"Sai kalaman yabo da godiya Ummi ke jero ma Annah, haka kurum Annah taji matar bata kwanta mata ba, kaman tana da b'oyauyyen Al'amari k'ulle cikin zuciyar ta...


"Masauk'i me kyau Mai Martaba yasa aka bawa su Annah, gefen Jalal da Zubaidah daban wani ratsentttsen sashe, basu shige ciki ba a cewar Mai Martaba sai zuwa gobe idan anyi bikin basa sarautar Yarima had'i da gabatar dasu a fadah a matsayin mata da miji kafin su shige sashen su cikin salama...

"Sanda Jalal da Shattima suka fito ya salam zo kaga yanda fadawa da masu sarautar ke kwasan gaisuwa had'i da fadanci..
"Gaba d'aya sai jin kansa yake uncomfortable.


*************

"Har Labib ya fito Salim Ya k'walla masa kira, tsayuwa yayi yana kallon sa kafin yace " What, ka gama shawarin ne, you lucky ban tafi ba, now d'auko mana car keys d'inka ka gani..

"Salim Ya kalle sa kafin yace " Ban gane na d'auko car keys d'ina ba, me kake nufi...

"Labib yayi gajeren tsaki kafin yace " Garage d'in Emeka zamuje mu saida ta mu k'ara kud'in guziri....

"Zaro ido waje Salim yayi kafin yace " You're crazy, this is ridiculous, man ka min maganar da hankali zai kama, motar tawa, Benz d'in nawa kake magana a saida a garejin Emeka wanda baifi ya taya mana dubu d'ari ba, kai ya gama k'ok'ari ya taya 200k... Motar over 7mlln.

"Tsaki Labib yayi kafin yace " You know what Salim you really wasting my Time, idan bazakayi tafiyar nan ba fine, da kake maganar Benz dinka miliyan bakwai ni nawa ride d'in miliyan nawa ne, ina ce na sayar sann da kud'in nasa a mana booking Ship, idan ma ka bar motar ka a nan ne toh wllhi k'arshe Alh Kasim ne zai biya bashin mutane da ita ko kuma Kawun ka Munir ya d'auka yayi gaba dashi don na tabbata eventually he's gonna betray Kasim Dasuki....
"So Dude if you ready for the escape ka d'auko car keys d'inka idan kuma ba haka ba, ka nemo 1mlln wanda za'a saya Captains dasu.....

"Idanun Salim suka ciko da k'walla, cikin sauri ya koma cikin gida ya bud'e bedroom d'insa, ya d'au keys d'in dake ajiye saman side drawer.
"Kallo ya tsaya yake bin d'akin dashi sanda ya tsaya a k'ofa hannun sa rik'e da handle, ya tuna duk wann luxury life d'in da yake ciki bashida wani option bayan ya fice ya rabu da ita, he never experienced financial hardships before, what ever he wants he got it...... But now, things are gonna change, ...... Muryar Labib yaji yana k'walla masa kira, cikin sauri ya soma sauk'owa daga stirs d'in gudu gudu....
"Yana fitowa ya danna security luck 4matic E350 d'insa ta bud'u, Labib ya murmusa kafin ya bud'e backseat ya jefa luggage d'insu, ya zagayo frontseat ya bud'e ya shige....

***************

"Washe gari ta kama Juma'a rana ce wacce aka gabatar da Yarima Modibbo da iyalan sa a matsayin ahalin gidan sarki. Hawan dubur sosai aka gabatar, tun safe ake gudanar da Dabur, lokacin sallan Juma'a tanayi suka sauk'a daga dawakan suka nufi babban masallaci don gabatar da nasu sallan.
"Abbah yana lura da yanyin Jalal, k'arshe dai kafin su fice ya tsida Shattima yace " Abdullah a koya wa Modibbo Al'adu da d'abi'un cikin gida..
"Cike da rusunawa Shattima ya amsawa Mai Martaba..

"Yau rana ce ta bikin murna, tambura sun bugu a wann rana, algaita sun kad'u,.

"Da yamma kuwa Mai Martaba yayi kiran iyalan sa gaba d'aya cikin fadah, wasu kujeru na alfarma masu kyaun gaske jera ma Jalal da Zubaidah, Ummi da Annah su suka rufa masu alkyabba, na Jalal fari k'al harda rawanin sa yayinda na Zubaidah ya kasance golden colour, Masha Allah kurum mutane ke fad'i..... Take kaji algaitu sun ci gaba da tashi..

"Marok'a nayi fadawa nayi, Allah Ya baka gidan ku, AAllah ya ja zamanin Yarima. D'an sarki jikan Sarki, D'an na gada kafi d'an na koya, gaban salamun baya salamun.... Baiwar Allah Allah Ya baki, Allah yaja zamanin matar d'an sarki, kin shigo ahalin alkhairi.. Allah Ya azurta ku da zuri'an alkhairi....
"Ire iren Kirari da aketa yi knn a cikin fadah.
"Dukda Jalal bai saba da hidimar sarauta ba, but for sure he feels something yaji wani abu a jikin sa. Tabbas ya yarda jinin sarautar na yawo a cikin jikin sa...


"Bayan an tashi daga wajen sahsen Ummi aka wuce da Zubaidah, wani abin mamaki har gyaran amarya su wasu dangin turarruka da kayan ci masu gyara Mace Ummi ta bawa Zubaidah, idanun Annah dai na kansu, sai ta yarda da ingancin abin kafin ta bari Zubaidah taci ko tayi amfani dashi, sosai Zahidah taji dad'in yanda Ummi ke nan nan da Zubaidah, kai kowa ma abin ya birge sa ga wad'an da suka santa shekarun baya sun sha mamakin canzawar ta, koda shike ba abin mamaki bane tunda a da can baya akwai k'uruciya a tattare da ita, ba kaman yanzu da girma yazo mata ba ta kuma samun hankali...

"Umman Shattima dai karyar goronta kawai take tana tab'e baki don kuwa sam bata yarda da kirkin da Fulani Kilishi ke yi ba....


"Da misalin k'arfe 8:30 na dare aka shigar dasu parlorn Mai Martaba na cikin gida Don lokacin ya tashi daga fadar sa, wato babban gwani...

"Ummi sai nan nan dasu take wanda hakan ya faranta ran Mai Martaba sosai, wasu alkyabban aka kuma rufa masu Ummi ta feshe su da turare kafin Abbah yayi masu nasiha mai ratsa zuciyar Mai saurare. Had'i da sanya masu albarka, daga nan sashen Madaki aka wuce dasu itama ta sanya masu albarka...

"Annah, Umman Shattima , Ummi da kuma Maman Kahifah matar Baba Ciroma sune sukayi rakiya ma Zubaidah zuwa sashen ta, tun daga waje bayi ne sukayi layi suna jiran isowar uwar gijiyan tasu...

"Wow Masha Allah, wann gida ya amsa sunan sa, komai yaji yayi kyau sai Allah son barka..
"Bayan kowa ya watse Annah ta kuma yima Zubaidah nasiha sosai kafin ta mata sallama ta shige sashen ta itama...

"Tana zaune saman katafaren Royal bed d'in wanda ya dace da hamshak'in d'akin, kanta har lokacin yana rufe cikin Alkyabba, a hankali ta yaye alkyabban ta shiga bin d'akin da kallo. K'walla suka ciko idanun ta, a hankali ta saki wani sassanyar murmushi zuciyar ta cike da gode ma ubangijin ta,...


"Tun daga k'ofan sashen nasu ya hangi bayi sai kai komo suke, masu saka turaren wuta na yi masu shigar da warmers na abinci na yi, " D'an juyowa yayi ya kalli Shattima kafin yace " What's all this for...??

"Shattima ya murmusa kafin yace " What do you expect,...

"Jalal ya d'an girgiza kai kafin yace " I had to put up with hargajiya things amma wad'an nan kuyangin sunyi yawa a nan, gaskiya ni bana son tak'ura...

"Shattima dariya ya soma har yana rik'e ciki kafin yace " Zan so naga zamanin naka sarautar inaga fadar kawai ta 'yan boko zata koma, za'ayi watsi da d'abi'u da Al'adun mu na gargajiya...

"Jalal ya d'an tab'e baki kafin yace " You're not helping you know...
"Kaga kasan yanda za'ayi a rage wad'an nan matan a nan, don ni gaskiya tak'urani zasuyi..

"Shattima ya k'unshe dariyar sa kafin yace " Wai kai meye naka na damuwa, naga dai ba akan ka zasu zauna ba snn kaga can... Yayi masa nuni da gefe wasu d'akuna kana yaci gaba da fad'in" Can shine d'akunan su, ba cikin gidan ka zasu kwana ba balle su tsare maka wani abu... Idan ka gansu gari ya waye ne, idan gimbiya tace bata buk'atan su bazasu shigo ba har sai gimbiya ta aiki yardajejjiyan tayi kiran su, idan buk'atan hakan ta taso, ka fahimta...


"Tab'e baki Jalal yayi daidai sanda suke shiga cikin kataparen parlorn wanda ya sha ado da kayan kwalliya na alfarma.

"Kuyangin nan suna ganin su suka zube k'asa suna kwasan gaisuwa, daga nan ficewa sukayi baki d'ayan su...

"Shattima ya d'an kalli Jalal yace " See.
"Bai wani zauna ba shima ya fice yayi tafiyar sa, waya mak'ale a kunnen sa da alama da sahibar tasa Zahida yake wayar.....

"Ya d'an jima a parlor yana bincike site d'in company d'in su don yanzu gaba d'aya zama busy Man ya kama sa, don ma Allah Ya taimake sa akwai Shattima, lallai yaga k'ok'arin Shattima da yake running company d'in...
"Daga bisani mik'ewa yayi ya haura sama.....

"D'akin dake a center ya soma shiga, shakka babu wann shine d'akin sa, bathroom ya fad'a ya sakar ma kansa shower had'i da d'auro alwala kafin ya fito ya shirya tsaf cikin silk jallabiya, fara k'al, sai k'amshi ne kurum ke tashi a jikin sa... Daga nan fitowa yayi ya nufi d'akin Zubaidah.



"Tana nan zaune wajen ta jiyo mostin tab'a handle da sauri ta kuma rufe fuskar ta heart d'in ta na beating fast sai kace ba Ya Jay d'inta data saba dashi ba haka taji...


"Da sallama saman bakin sa cikin tattausar muryar sa ya turo k'ofar ya shigo..
"Murmushi kawai yake yana kallon ta yanda tayi zaune tsakiyar gadon irin dai yanda amare ke yi...

"K'arasowa yayi ya zauna gefen ta, kafin Ya tambaye ta taci abinci, gyad'a masa kai tayi alamun eh...


"Jalal ya murmusa kafin yace " Baby mu biyu ne fah, only the two of us, ki bud'e bakin ki ki min magana, Ya Jay d'ink ne fah...


"Shiru bata kulasa ba, murmusawa Ya kuma yi gamida kai hannun sa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login