Showing 1 words to 3000 words out of 210924 words
HADA DOCUMNTS BY
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND ENGLISH NOVELS
@ WASAPP 08066360176
πππ ZUBAIDAHπππ
01
*Β©Sameena Aleeyou...βπΎ*
_πQueen Samy Novels Forum....ππ_
*Dedicated to all Victims of Rape, never give up, fight for your right, this is not something to be ashamed of your self. Make the guilty ones feel ashamed of themselves* ππΎππΎππΎππΎππΎ
"Garin Dukku jihar Gombe, gari ne wanda akasarin mutanen dake zaune wajen fulbe ne, ma'ana fulani ne. Ni Sameena tafe nake cikin garin ina bin tsarin garin da kallo yayinda zuciyata ta cika da nishad'i. Can na hangi wata matashiyar budurwa wacce ak'alla bazata gaza shekaru goma sha shida 16 a duniya ba. Daga yanayin halittarta zaka fahimci cewa bafulatana ce ta usul. Bata da matsanancin tsayi snn bata a layin gajeru, farinta irin mai d'auke idon nan ne don saida ta matso kusa sosai na fahimci hakan. Yanayin suturan dake jikinta zai tabbatar maka iyayenta talakawa ne sosai. Silipas din dake k'afufunta kuwa duk ya b'ule yaji jiki.
"Sauri take tamkar mai shirin tashi sama, yanayin tsoro da firgici da ya wanzu a fuskarta zai tabbatar maka cikin matsanancin tashin hankali take. Kaman ta zunduma a guje haka take tafiyar, Yar da d'an karan dake hannunta tayi ta soma sassarfa hadi da gudu gudu sakamakon jiyo muryar dake sata firgici koda a mafarkinta ne tana k'walla mata kira har waje ake jiyowa,. *ZUBAIDAH! ZUBAIDAH, ZUBAIDAH!!!
"Ni kuwa Queen Samy nace " Bari na bi wann yarinya na rubuto wa d'inbin masoyana labarinta mai cikeda tausayi, Al'ajabi da kuma ban mamaki had'i da darrusa masu girgiza zukata.
"Dan ubanki sai yanzu kika daman dawowa daga karuwancin naki? Macen dake tsaye tsakar gidan rik 'e da guga ta fad ' tana watsa wa Zubaida mugun kallo me nuni da cewa zaki yaba wa aya zak'inta.
"Bakinta na rawa take fad 'in Yaya Hadiza wllhi ban sami Yayan a kasuwa bane shine na k'arasa bakin tasha..... Ai bata gama cewa tasaha ba Yaya Hadiza ta jefa mata gugan dake hannunta ji kake tum ya fad 'I a tsakar kanta.
"Durk'usawa Zubaidah tayi tana rik'e da tsakar kanta hawaye na zuba bisa k'uncinta.
Hadiza ta k'araso gamida mak'urota tana fad'in" Dan ubanki ni na aikeki bakin tasha, wani munafurcin ne ya kaiki bakin tasha, auho kice mun karuwanci kika tafi, shegiya Me suffan mayu da aljanai. Rankwashin da ta sake mata a tsakar ka yasa Zubaidah sakin k'ara sabida azaban dataji.
"Hadiza ta shiga janta a k'asa tana fad'in" Au kuka ma zakiyi shegiya munafuka saikace wacce na bugeki toh bari kiga na tapkeki sosai sai kiyi mai dalili.
"Duk kukan da Zubaidah take tana rok 'on Hadiza tayi hak 'uri ko gizau bata fasa jibgangta ba kaman Allah ne ya aikota.
"Inna Furera mak'ociyarsu ce ta shigo a guje don ceton Zubaidah dama mak'ota sun saba shigowa kawo mata d'auki, tunda Hadiza ta tsefe ido taci mutuncinsu tsaf suka daina, saiko Inna Furera ce kawai bata fasa ba.
"Da sauri tayi tsalle ta kwace Itacen da Hadiza ke jibgan Zubaidah dashi, dama Jadiza irin ingarman matan nanne.
"Ta shige tsakani tana fad'in" Haba, haba Hadiza, anya kina kuwa tuna mutuwa, kullum sai ki kama wann 'yar marainiya kita jibga ke ko tsoron kamuwar Allah bakya yi. Cewar Inna Furera .
"Galala take Kallon Inna Fure kafin ta gyara tsayuwa ta soma fad'in" Fure! Fure!! Fure!!? Billahilazim hawainiyarki ta kiyayi ramata, banda munafunci irin taki ina ruwanki da ita, ci kike bata ko sha, cikin biyu babu d'aya. Toh wllhi wllhi ki fice a idanu na.
"Inna Fure tai murmushin takaici kafin tace " Lokaci ne, da zaran lokacin da Zubaidah zata sami kulawata yazo zata samu kuma ke baki isa kiyi komai ba.
"Shewa Hadiza ta kwashe dashi kafin tace " Ai dama nasan wajen munafukin wann d'an naki me matse yaran mutane a lungu take zuwa, bacin haka babu abinda zai kaita bakin tasha, Toh wllhi idan ni Hadiza ina numfashi Zubaidah bazata auri Ummaru dreban tanka ba. Ke na tak'sita maki zance Zubaidaha bazata tan's aure a rayuwarta ba, makarantar data samu na bari tayi ya isheta, amma aure kam saidai tayitaji k'annen bayanta suna tafiya d'akin miji amma banda ita, tunda dama sa 'anninta Sun k'are k'annenma sun kusa k'arewa. Ta juyo ta narkawa Zubaidah da har lokacin kukan zuci take hawaye na bin k'umcinta tace " Ke kuma bak'ar munafuka ki tashi ki min wanke wanke kafin ki d'aura sanwa don yau islamiyar ma ba zuwanta zakiyi ba. Daga haka ta wuce d'aki fuuu kamar me shirin tashi sama.
"Inna Fure ta girgiza kai ta k'arasa ga Zibaidah wacce ke faman mik'ewa da k'yar sabida raunin da Hadiza taji mata da itace, tsugunawa Inna Fure tayi tausayin yarinyar ya cika zuciyarta, a hankali tasa hannu ta goge k'wallan da ya zubo mata. Hannu tasa ta shiga sunce d'aurin da Hadiza tai ma Zubaidah da igiyan guga.
"Suna had'a ido Zubaida taji wani sabon kuka na shirin kufce mata, ........
[1/23, 22:07] βͺ+234 803 619 0581β¬: πππZUBAIDAHπππ
02
*Β©Sameena Aleeyou... βπΎ*
_Queen Samy Novels Forum.... ππ_
*Dedicated to all victims of rape, never keep silence, keep fighting for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves*ππΎππΎππΎππΎ
"Murya na rawa Zubaidah take fad 'in" Inna meyasa iyayenmu suka mutu suka barni dagani sai yaya na, meyasa Yaya na ya kasance haka, meyasa bai zama kaman ko wani d'an Adam ba...... " Tausayin kalamanta sun cika zuciyar Inna Fure, a hankali ta kwance bakin zaninta ta goge wa Zubaidah hawayen dake kwaranya a fuskarta. Hannayenta ta rik 'e suna fuskantar juna kafin ta soma fad 'in" Zubaidah kar ki bijire wa ubangijin ki, kar ki bari shedan ya rinjayi zuciyarki, har yake kawo maki ire iren wad'an nan tunani. Mutuwa dole ce kan ko wani mahaluk'i, snn kasancewar yayanki cikin mutane marrasa k'oshin lafiyan k'wak'walwa jarabawace daga Allah, wanda kema jarabawar ya shafeki. Shi kansa Habibu baijin dadin abinda Hadiza ke maki, amma babu yanda ya iya, bazai iya k'watan 'yancin kansa ba balle naki daga hannun Hadiza, hak'uri shine zakici gaba da yi.
"Goge hawayen tayi kafin ta furta a hankali " Kenan shikenan ni bazan tab'a jin dad'in rayuwa ba kenn, bazan rayu kaman yanda ko wani d'an adam yake rayuwa cikin 'yanci ba. ...."Kasa jure saurarenta Inna Fure tayi sabida tausayi, mik 'ewa tayi kafin tace "Tashi ki soma ayyukanki kafin ta fito ta sameki. Jiki a sanyaye Zubaidah ta mik 'e daidai lokacin " Kamalu d'an Yaya Hadiza ya fito cikin shirin tafiya islamiya fuskarsa da alamun bacci ya tashi, yaro d'an shekaru bakwai a duniya. Rungume Zubaidah ya k'araso yayi yana mata magiyan ta shirya su tafi islamiya, itama rungumesa tayi tana k'k'arin lalumo k'aryar da zata shata masa, don tasan yau kam babu ita babu islamiya. Inna Fure ta fice tana sak'sak'en lamarin Zubaidah a zuciyarta.
"Kamalu ya lura da hawayen dake bisa fuskan Zubaidah, Ya kalli gwiwar hannunta yaga jini, shiru yayi kaman bazaice komai ba kafin yace " Na sani yauma Umma tace ta dakeki ta hanaki zuwa makaranta ko Anty. Kame kame Zubaidah ta soma yi don yaron akwaishi da wayo da kaifin basira, daidai nan Yaya Habibu yayi sallama ya shigo cikin yanayin tafiyarsa na sokaye _Phsycos_ da maganansu.
Kamalu ne kawai ya tafi ya masa oyoyo Zubaidah kam wucewa tayi bakin rijiya don taran ruwan wanke wanke, tabbas tasan Yaya Habibu ya ganta a haka toh fah haka zai wuni yana kuka.
"Inna Fure tana shiga gida ta tarar da Umar dawowarsa kenan. Koda ya gaisheta sama sama ta amsa, Umar ya lura da yanayinta, don ko tambayarsa ko yaci abinci batayi ba, kaman yanda take a kullum. don haka zama yayi bisa gefen tabarman da take zaune " Sadda murya yayi kafin yace Innata meke faruwa ya tambaya yana kallon Inna Fure. Sauk 'e ajiyan zuciya tayi kafin ta soma fad'in" Umar shin da gaske kake son Zubaidah.
"Kallon mamaki yayiwa mahaifiyar tasa kafin yace "Haba Inna wann wace irin tambaya ne, Kowa ya sani duk fad 'in garin nan Zubaidah kadai nake so, nake burin mallaka, bansan meyasa Zubaidah tak'i barina na kai tambaya gidansu ba. Don wllhi Inna na k'agu na rabata da wann muguwar matan yayan nata.
"Inna ta sauk 'e ajiyan zuciya kafin tace " A gaskiya Hadiza bata da imani Ummaru....... "Ganin yanayinta yasa mik 'ewa zuciyarsa na bugawa yake fad'in" Inna ki fad 'a mun me tayi mata, ta kuma dukanta kaman yanda ta saba ko..
"Gjrgiza kai Inna ta soma tana fad'in a'a Umar don Allah ka zauna, zauna nace ba dukanta tayi ba, kawai dai so nake ayi maganar aurenku, da zaran malam ya dawo zan masa batun insha Allah, take farin ciki ya mamaye zuciyarsa nan ya shagala da zancen......Inna ta bisa da ido yanda yake murna kaman an masa alk'awarin hajji, gwara da ta kawo masa wnn zancen don tasan kalan zuciyar d'anta yanzu sai yaje yayi ma Hadiza kaca kaca.
**********************
*Abuja, Maitama*
"Wasu tagwayen gidaje na hango masu d'an karen kyau, exactly babu abinda ya raba da na gefe, komai iri guda. Wadan nan gidaje gidajen Yaya ne da kuma k'ani, Alhaji Kasim Dasuki shine Babba, yayinda Alhj Jamil Dasuki shine k'ani. Alhj Kasim da k'aninsa sunyi kaurin suna wajen hold'an kasuwanci ta yanda k'asashen duniya da dama suke hold'a dasu, tareda shahararriyar Company dinsu mai suna *Dasuki Holders*, Ko wannensu Allah Ya albarkacesa da yaro namiji k'wara dad'd'daya,.
SALIM KASIM DASUKI, da kuma LABIB KASIM DASUKI, tsakanin Salim da Labib shekara gudane cal, haka nan yaran suka taso cikin sangarci da rashin tarbiya, saboda so da iyayensu ke nuna masu, wanda a nasu tunanin gata ne. Babu mai taba masu 'Ya'ya Ya zauna lafiya sai sun ga k'arshensa, musamman Alhj Kasim shi yafi k'aninsa bak'in zuciya, wani sa'in Alhj Jamil dinne ke nusar dashi hanya. Haka zai balbalesa tsaf da masifa, uwa uba WA'azin da Alhj Jamil ke masa kan su guje dukiyar haramun cikin kasuwamcinsu, wann dalili Ya soma sakawa Alhj Kasim tsanar Dan'uwarsa har yake tunanin tabbas zasu iya samun sab'ani koma takaisu ga raba dukiyarasu.
[1/23, 22:07] βͺ+234 803 619 0581β¬: πππ»ZUBAIDAHππ»π
03
*Β©Sameena Aleeyou...βπΎ*
_Queen Samy Novels Forum..ππ_
*Dedicated to all victims of rape, never keep silence, fight for your right,... This is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselves ππΎππΎππΎππΎ*
"Salim ne kwance saman coach a bakin pool dake a cikin gidansu, da gani daga ruwan ya fito don daga shi sai gajeren wando. Idonsa manne da bak'in sunshade ya k'ura wa rana ido, gefe dashi k'aramar table ne wanda wayoyinsa ne da kuma Chapman akai.
"A hankali ya kai hannunsa kan table din gamida daukar d'aya daga cikin wayoyin nasa nan ya shiga dialling lambar budurwarsa KAUSAR wacce ake batun saka masu rana. Sosai suke hiran soyayya daga ji kasan suna tsananin son junansu.
"Daga can bayansa yanda Labeeb ke tsaye ya k'urawa cousin d'in nasa ido, shakka babu su duka biyu sunyi tarayya wajen son mace guda, zuciyarsa yaci gaba da tafarfasa, da sauri ya juya ba tareda yayiwa d'an uwan nasa magana ba.
"KAUSAR TAHIR MARAFA, shine asalin sunanta, mahaifin Kausar abokin kasuwancin iyayen Labeeb da Salim ne, musamman Mahaifin Salim Alhj Kasim Dasuki, Shima Alhj Tahir Marafa dan asalin garin Dukku ne, Kausar basu jima da dawowa Nigeria ba daga k'asar Holland dalilin dawowarsu ma sabida neman muk'akin kujeran Shugaban k'asa da mahifinta zai fara ne, farkon dawowarsu sabo mai tsanani ya shiga tsakaninta da Labeeb a lokacin Salim yana can Scotland yana k'arasa wani course dinsa shi, koda Salim ya dawo Labeeb shi yayi masa introducing Kausar, tunda Kausar da Salim suka k'yalla ido akan juna soyayya mai tsanani ta shige tsakaninsu, toh fah run daga wann lokaci Labeeb ya rasa sukuni, a ganinsa cin amana ce wnn k'wace Salim yayi masa.
"Iyayensu gaba d'aya sunyi farin cikin wann Al'amari tun basu hadasu ba gashi sun hada kansu, babu kaman Alhj Kasim Dasuki wanda dama shi Money hungry, baya rab'an mutum sai zai sami alkhairi. Dukda tarin dukiyar da yake dashi baya hanasa hangar na wani. Yasan muddin tilon d'ansa Salim ya auri tilon 'yar Alhj Marafa wataran zasu mallaki gaba d'aya dukiyar Alhj Marafa.
"JALAL! Na'am Anna ya amsa gamida ajiye takalmimsa da yake faman gogewa, fitowa yayi ya tarar da Annah zaune tana stincen wake
. Kallonsa tayi yanda ya shirya tsaf cikin kaya masu kyau da tsada kaman wani d'an hamshak'i.
"Jalal ina zaka, Jalal farin saurayi dogo mai cikar zati kyakkyawa ya murmusa kafin yace "Annah birthday d'in abokinmu TARIQ zamuje su Salim suna waje suna jira na.
"Fuskar Annah tamau dama tasan zancen bazai wuce haka ba, tasha raba Jalal dasu Salim amma baya ji, yak'i yarda ya tsaya a matsayinsa na talaka bashi da aiki kullum sai k'ok'arin had'a kansa da sangartattun yaran masu kud'i musamman su Labeeb.
"Gyaran murya Annah tayi kafin ta soma fad 'in" Jalal har yaushe zan maka magana kaji, ka sani kai maraya ne kuma talaka, idan baka tashi ka tsaya ma rayuwarka ba babu wanda zai maka, kai kullum bakada aiki se biyewa su Salim ko, toh ka sani su sunada masu masu, sunada gatansu kaifah, baka dashi , tunda ka gama jami 'a ka'ki neman aiki ka tsaya kana biye masu, yau kune wancan club din gobe wancan, kune bin 'yanmata kune shaye shaye...... "Jalal yayi saurin d'ago kai yana kallon Annah, haba Annah shaye shaye fah kikace nasan dai su Salim suna yi amma ni banayi, ina dai da 'yammata banyi musu ba amma wllhi bana shan komai tunda kika hanani....... "Rufe mun baki Annah, ta dakatar dashi kafin taci gaba da fad'in" Da da kakeyi na maka uzuri don na d'auka yarinta ne zaka daina amma yanzu na gane shashanci ne kawai ke damunka, shekaranka 25 ace bakasan abu me kyau ba toh wllhi ka kiyayeni..... "Sallaman Labeeb ya katsesu.
"Gaisar da Annah Labeeb yayi, ta amsa masa babu yabo babu fallasa, kafin ya d'an daki kafad 'un Jalal yace Guy let's get going.. Jalal ya mike yana satan kallon Annah kafin yace Annah sai mun dawo, kallo tabisu dashi har suka fice, girgiza kai tayi kafin tace bazan fasa maka addu'an shiriya ba.
Sameena ce ππΎ
[1/23, 22:07] βͺ+234 803 619 0581β¬: πππ»ZUBAIDAHππ»π
04
*Β©Sameena Aleeyou..βπΎ*
_Queen Samy Novels Forum... ππ_
*Dedicated to all Victims of rape, never keep silence. Fight for your right, this is not something to be ashamed of your self, let the guilty ones feel ashamed of themselvesππΎππΎππΎππΎ*
"JALAL, abokin su Saleem ne wanda tun tasowarsu tare suka taso, Jalal maraya ne wanda bashida kowa sai mahaifiyarsa Annah, Annah tayi komai a rayuwarta don ganin ta inganta rayuwar Jalal tun yana yaro, kama daga karatunsa har zuwa girmansa, haka nan ya tashi ba tareda yasan mahaifinsa ba, don Annah ta sanar dashi cewa mahaifinsa ya rasu tun yana k'arami. Annah ta jima tana yiwa matar Alhj Kasim aiki wato mahaifiyar Salim, tun wani lokaci da suka zauna a Gombe, tun yaran gaba d'aya suna k'anana, Annah ita ta rainesu gaba d'aya, Salim Labeeb da kuma Jalal d'inta, wann dalili yasa lokacin da zasu komo Abuja suka taho tareda ita don tun a lokacin bata da miji ya rasu. Ta zauna da d'anta a nan BQ din gidan Alhj Kasim.
"Tunda yaran suka taso iyayen ke k'ok'arin rabasu da Jalal, suna nuna masu cewa shi ba daidai dasu bane, babu yanda basuyi ba don ganin sun rabasu amma abu yaci tura dole suka hak 'ura suka k'yalesu, amma ko kid'an babu wani abu na arziki da suke masa.
"Shi kuwa Jalal babban abun da ke masa dad'i shine yanda emmata da samaruka yaran masu kud'u suke zaton shima DASUKI'S ne, ma'ana shima dan familyn Dasuki ne, ko ina tare dasu Salim suke zuwa party shisha spot da dai sauransu. Allah ya masa kyaun hallita gabba d'aya yafisu kyau 'yanmata suna rubibinsa shiko na ja masu class kaman wani d'an hamshak"i ko kad'an bakace Jalal ya had'a jini da talaka ba...wann kenan.
*Gombe, Dukku*
"Huci take kaman wata kububuwa tana watsawa malam Habu mahaifin Umar da abokinsa malam Tanko harara, Malam Habu suka saki baki suna kallon ikon Allah sanda Yaya Habibu ya mik'e ya rusuna gaban Hadiza yana tambayanga shin ta amince a karb 'I