Showing 168001 words to 171000 words out of 226732 words

Chapter 57 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12464

Inna ba ta sanyamusu kenan, duk zuwansu dama gargadi ne sosai da jan kunne ta ke musu akan kar su sake su yi yunkurin tonamata asiri.

Modibbo wanda ya kasance ɗa na bakwai a wurin Inna, kusan shi ne babban mugun da ya fi kowa tsanar yaran Yakumbo. Ya sha kama su a makaranta ya jibga ya kuma kwace abincin da Hajjo ta girkamusu. Gori na uwa da uba bai fasa yi musu ba.

"Wai meye amfanin riƙon da ake musu anan? Tunda suna tutiyar dangin uwarsu masu arziki ne, ki tattara ki maida su mana!"

Modibbo ya fadi a zafafe. Yar uwarsa kuma Yayarsa Adda Salma ta karɓe.

"Ashe ka gane, ni wallahi haushinsu nake ji,wannan Aminar ma kyanta ya yi yawa, ko makaranta muka je sai a yi ta wani zuwa ana daukarta. Ji nake kamar na shaƙeta na huta. Da zan samu reza na tsaga fuskar ma zai fi."

Sauran suka yi dariya har Inna Idan ka cire Karime da Adamu wadanda su kadai suka fita zarra akan sauran, basu taɓa nuna kiyayya ga Amina da Aminu ba. 

"Allah ne Ya ba ta kyan, kuma ai..."

Buge bakinta Modibbo ya yi da ƙarfi.

"Dama ke da Adamu ina kula da yanda ku ke shishshigewa yarannan! Marasa zuciya da kishin uwa!"

***
Da wannan irin kiyayyar Amina da Aminu suka taso, boko dai basu isa su je ba sai yaran Inna, islamiyya kadai suke zuwa. A wannan rayuwar, Waziri ya fadi ya mutu, kasancewar mahaifiyar Yakumbo ta jima da rasuwa ne yasa babu wanda ya kara waiwayarsu balle ya maida hankali wurin kula da su daga Mubi. Yar uwar Yakumbo tilo, Zahida, ita kuwa tana aure a Saudiyya. Kafin ta shigo gari akan jima sosai.

Shekaru suka ja a wannan halin, Aminu ya yi saukar littatafai da dama na addini. Mutum ne mai matukar kokari da saurin daukar karatu. Lokaci ɗaya kuma ya bazama neman ilimi a garuruwa daban-daban. Inna ko a jikinta, don a ganinta ba wani ci gaba da zai samu face ya ƙare a almajiranci. A sannan babbar ɗiyarta Hansatu, ta kammala karatunta a fannin shari'a a jami'ar Adamawa. Yayinda Salma ta karancifannin Kasuwanci. Duk an musu aure a sannan.
   Modibbo yana ajin karshe inda shima dai yake karantar fannin Kasuwanci. Adamu da Karime su ne a babbar Sakandire sai Hadiza, Safiya, Tahir a karamar Sakandire,  Maimuna Autar Inna a firamare.

A islamiyya ba su taɓuka abin a zo a gani, gwara ma Karime, tana da kokari sosai don ta yi sauka.

  Yaran Amarya Hajjo hudu, suma duka suna karatu.

Bayan tafiyar Aminu almajiranci da watanni biyar sai ga Hajiya Zahida da yaranta daga Saudiyya. Sun dawo kenan sakamakon sauyin wurin  aiki da mijinta ya samu zuwa Adamawa. An saukeshi daga Ambasada. Kai tsaye wurin ƴaƴan yar uwata ta soma zuwa. Ranar da ta je ta tarar da Inna na jibgar Amina da sunan wai ta tsaya sauraron bare wanda kwata kwata ma ba jinin Fulani ba ne. Da biyu Innar ta yi hakan ganin yaron mahaifinsa mai kudi ne, sunan zuri'arsu ba ɓoyayye ba nema ƙasar. Ya ganta ne a hanyar dawowarta daga islamiyya.

Wannan tashin hankalin da Hajiya Zahida ta tarar yasa ta rantse ko sama da ƙasa za ta haɗe sai ta tafi da Amina. Kaca-kaca suka rabu da Inna, a karshe ta ci nasarar dauke Amina tana kukan rashin sanin inda Aminu ya tafi.

Da wannan suka wuce Mubi, sosai ta nunamusu ɓacin ranta akan yanda suka yi halin ko in kula da yaran Yakumbo, hatta aiken da takan yo a kai musu ba ya riskarsu.

Da wannan bakin cikin ta zauna, sati na cika ta tattara yaranta har Amina suka wuce sabon gidansu a cikin Yola.

Wannan ne dalilin ingantuwar rayuwar Amina wacce gaba daya yaran ke kiranta Dada. Babban ɗan mijin Hajiya Zahida  (ɗan Uwargidansa da ta rasu, riƙonsa ya koma hannun Zahida) Naziru, tunda ya dora ido a kan Amina ya ji nan duniya ita yake so da aure.

  Sosai abin ya yiwa Hajiya Zahida dadi, hakanan shima mijinta bai ƙi ba. A yan uwan mahaifiyarsa ba wanda ya nuna kiyayyar abin ko don irin rikon da Hajiya Zahida ta mishi, ba jimawa kuwa aka sha bikinsu. Amina ta yi kukan rashin dan uwanta a kusa, haka ta hakura ta fawwalawa Allah suka tare a gidan Naziru wanda babu nisa sosai da gidan Hajiya Zahida.

***
  Bayan shekaru masu dama, Dada ta haifi yaranta uku duk mata, tana da cikin na hudu ne ba zato ba tsammani Naziru mijinta ya ɗaukesu sai gidan Hajiya Zahida. Wanda ta gani ne ya sanya ta zuwa a guje ta rungumeshi sai kuka, tana yi shima yi yake. Ta ɗago ta dubi wata mace fara ƙal da ita kyakkyawa, a gefenta wasu kyawawan yara ne su biyu da zasu girmi yaranta, komai nasu iri daya. Haka kawai jikinta ya bata wannan iyalin Aminu ne. Ta rungume matar kafin ta rungumi yaran tana cike da farin ciki.

Sai bayan an zauna an nutsu ne ya ke basu labarin inda ya je.

Ashe bayan tafiyarsa da tawagar almajirai ba inda suka yada zango sai Maiduguri, ya fada hannun wani Malami kuma barebari cikakke, Malam Banakura. Mutum mai sanin daraja da ƙimar almajiransa. Aminu bai ɓoyemishi komai dangane da Asalinsa ba. Tausayi da kaunar Aminu suka shiga Malam. Ya rikeshi tamkar ɗan cikinsa, duk da tarin Almajiran Malam, Allah bai ba shi haihuwa ba. Kuma matsalar daga gareshi ne. Uwargidansa Yakura, mace ce mai halin Dattako, ta rike yaran yan uwa da dama ta kuma aurar da su. Yara biyu kadai suka rage a hannunta sannan, Zahra da Yusha'u.

  Zuwan Aminu sai ta haɗa da shi ta rikesu duk kuwa da cewar ya girmi Zahra nesa ba kusa ba. Sai dai zai iya sa'an Yusha'u.

Haka suka rayu har suka kara girma, noma da kiwo shi ne sana'ar Malam bayan koyarwa, Aminu ya tsunduma wurin taimakawa Malam.  A hankali kuma Allah Ya sanyawa abin albarka. Koda shekarun aure suka kai, Malam ya fahimci irin soyayyar dake tsakanin Zahra da Aminu, bai yi ƙasa a gwuiwa ba ya auramasa ita da iznin iyayenta. Mahaifinta buzu ne kuma Maigadi, mahaifiyarta ce ƙanwa ga Yakura matar Malam. Kyakkyawar mace mai gashi har ƙugu, yarinya mai yawan ibada da kunya.

  Zamansu ya yi albarka sosai, sai da suka shekara kafin ta samu cikin ƴan biyu. Ta sha wuya sosai kafin ta haifesu. Sai da ƴan biyu suka shekara goma cif a duniya, Malam ya rasu bayan fama da rashin lafiya. Sosai ya gargadi Aminu kamar koyaushe akan ya je ya nuna iyalinsa a gida. Wanna tasa ana yin arba'in na Malam, shima hankalinsa ya yi gidan.

Shi ne zuwan da ya yi a yanzun, Dada ta ci kuka ta kuma yi korafin nisanta kansa da ya yi da ita har ba ya tunanin halin da ta shiga. Hakuri sosai ya ba ta, ɗan uwa rabin jiki, nan da nan kuma ta mance da komai. Ya nemi labarin abubuwan da suka faru bayansa, anan yake jin labarin mutuwar Inna bayan ta yi fama da jinya. Addu'a kawai ya yi mata tsoron Allah na ƙara shigarsa. Nan yake jin auren da Modibbo ya yi da kuma zaman da ya koma yi a Kano inda yake kasuwanci, sai Adda Salma da mijinta ya koma Gombe. Sauran yan uwa kuwa suna nan a Yola, Karime ma ta yi aure hakanan Adamu.  A yaran Amarya Hajjo ma, autanta ne kaɗai bai kai ga yin aure ba sannan. 

Washegari suka dunguma zuwa dangin mahaifinsu.

Sun samu tarba ta ban mamaki a wurin yan uwan mahaifinsu wannan ya kara tabbatar musu cewa dama can shakkar Inna ce ta sanya ake baya-baya da su, ko dai kuma don yanzun Dada na auren mai kudi ne shima kuma Aminu ya samu rufin asiri daidai gwargwado ne don har gidajen gona da dabbobi yana da su? Oho, ba su da masaniya.

Aminu bai yi ƙasa a gwuiwa ba sai da ya je gida yayyunsa mata duka idan ka cire Adda Salma da ke Gombe. Ya yi mamakin ganin yanda har sannan babu ɗigon kaunarsu a cikin idanuwansu, asalima sai da suka goranta masa na auren Bare a cikinsu don dukkansu auren gida akai musu.

"Kai da Amina kun fita zakkah! Gwara ita, ta auri Fulani kai kuwa bayinmu ka je ka kwaso mana. Har abada ba zamu taɓa daukarki daya a cikinmu ba. Tsana yanzu aka fara."

Wannan shi ne munanan kalaman da Gwaggo Hansatu ta watsawa Zahra da har ya sanyata hawaye.
Karime ce dai ta rasa inda za ta sanyasu don farin ciki. Ta rungume HASSAN DA HUSSEIN cike da murna da jin dadi har da kukanta.

Haka aka rabu cikin aminci, suka dunguma zuwa Mubi. Nana ba laifi an musu tarba.

Aminu bai ƙasa a gwuiwa ba sai da ya shirya zuwa Kano sada zumunci da Modibbo. Ya tarar da matansa biyu, Hajja Fatuma da Amarya. Tun shigowarsu ya dinga watsamusu banzan kallo yana gyara zaman malun-malun. Ba haka ya so ganin Aminu ba, so ya yi rayuwarsa ta lalace yanda rigar jikinsa ma zai gagareshi. Ya mishi tsanar da ko a inuwa ba ya son ganinsa sai rana. Da harshen fulatanci Aminu ya gaida shi.

"Gaisuwar ta mece ce? Ni waye a wurinka? Shekaru nawa ka tafi yawan maula, sai yanzun ne za ka je ka dawomana da SADAKAR YALLAH?"

Cikin dakiya Aminu ya amsa.

"Ba sadakar Yalla ba ce, sunanta Zahra. Matata ce."

Harara Aminu ya watsamata, ƴan biyu suka ƙara nanewa a jikinta suna bin wanda aka kira Yayan Babansu da kallon tsoro da tsana.
  "Bare ce! Yanda uwarka ta shigo gidanmu tana matsayin bare, kaima haka ka je ka kwasomana abin fadi da gori! Har abada wannan matar ba za ta zauna cikin zuri'armu ba. Sai yanzun ka tuna da mu ka kwaso jiki ka taho zumunci ko? Toh ni Muhammadu, ban sanka ba! Bani da wata alaƙa da kai, ƙafarka na ƙara gani a gidana Allah Ya isa. Duk abinda na yi maka kuma kai ka ja wa kanka. Ku kuma kuma kallona kamar Mayu!"

Ya maida akalar zancen kan Hassan da Hussein da suke kallonsa, duk da karancin shekarunsu, haka bai sa sun gaza fahimtar wasu abubuwan da yake faɗi ba don Hausa sak ya yi ko don ya baƙantawa Zahra.

Da wannan cin kashin da rashin mutuncin na Modibbo, Aminu ya tattara iyalinsa suka juya ko kwana ba su yi ba. A mota ya yi ta rarrashin Zahra da ban hakuri. Ita kuwa murmushin yaƙe ta yi kawai ta nuna ba komai tunda dai bai ɓoyemata alaƙarsu da su ba tun farko. Labarin komai na irin riƙon da ya samu a hannun uwarsu ta sani.

  Watansu daya suka yi shirin komawa, nan fa Dada ta rikice da kuka da rantsuwar ba ta yarda ba, a karshe ta dage ma sai dai a bar mata ƴan biyu ta riƙe, dabararta na yin hakan, don kawai su dawo da wuri a dinga ganinsu. Aminu ya rasa ya zai yi da yar uwarsa, ga mamakinsa Zahra da kanta ta riƙe hannun Hassan da Hussein ta damƙawa Dada tana murmushi.

"Yarana mallakinki ne Dada. Gasunan na bar miki su duniya da lahira."

Wannan abu har gobe Dada ba za ta mance shi ba, kuka sai ya koma dariya. Har tasha suka yi musu rakiya suka dawo. Abin mamaki Hassan da Hussein ko a jikinsu don sosai sun saba da Dada da iyalinta a ɗan zaman da suka yi tare.

***
Mummunan labarin hatsarin mota da rasuwar Aminu da Zahra ya riskesu. Wannan ya yi sanadin fitar cikin Dada, ta sume.

   [3/17, 9:18 AM] +234 703 629 0938: I just published "BABI NA HAMSIN DA BIYU" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1010093134?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=azuNeDf8BzRGeUbQ5hUohOGx2aTzO5EgG0sslypZUWd87KXOqPMoNqGJcWUIJ7lkGQPCJLaZwnIqw7s7g8N0NU%2BMfRV98U0i0%2BriYhHA5YJps5E19e%2B0H%2FQy%2Br8BBzme




🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

52)



Sosai mutuwar ta girgizasu, anan suka ƙara jinjina kudurar Ubangiji. Wato dai da yanzun har yan biyun za'a rasa shikenan babu tarihin Aminu da Zahra a doron ƙasa.

Allah Ya taimaka, Aminu ya bada kwatancen inda suke zaune a Maiduguri, da haka suka karasa bayan an sallaci gawar Aminu da Zahra an binnesu a nan cikin Yola.

Yakura ta ji mutuwarnan ba kaɗan ba, dama tana cikin takabar Malam. Hakanan iyayen Zahra su kansu mutuwar ta dake su. Sai da aka yi arba'in aka raba gadon ƴan biyu. Ba wanda ya hana Dada tahowa da Hassan  da Hussein.

***
  RAYUWAR ƳAN BIYUN

Rayuwa mai dadi suke yi a wurin Dada da mijinta, basu san matsalar rashin uwa ko uba ba. Kaunar da Dada ke yi musu har kusan matsala ta so ba ta da Naziru don gani yake kamar ba ta kula da yaransa irin yanda take rike da yan biyu. Wannan ne dalilinta na ɓoye son a zuciyarta. Makaranta mai kyau na masu gata suke zuwa don dama sun soma firamare, ci gaba kawai suka yi.

  Tafiya ta ci gaba da tafiya har ƴan biyu suka kammala firamare suka soma kokarin tafiya Sakandire. A sannan ne Dada ta danne zuciyarta ta shirya da yaranta kaf suka halarci bikin ƴar Modibbo a Kano. Yaran babu mai murna haka Dada ta yi ta lallaɓasu gami da nunamusu muhimmanci da ladan dake cikin sada zumunta.

Koda zuwansu suka sauka a gidan wani abokin Baba Naziru don yaran sun rantse baza su je kwana gidan Modibbo ba har da kukansu, anan ne Dada ta goyi bayansu, ita kadai ce ta karasa gidan dan uwannata  ta sauka dakin Amarya don duk ta fi mutan gidan kirki da dadin mu'amala. Ita ke yawan ba Dada hakuri akan yanda rayuwa ke tafiya. Hajja Fatuma ta yi bakin ciki da saukar Dada dakin Amarya ganin ita ce ke aurar da ɗiyarta.

  Ranar wuni direba ya kawo yaran Dada kaf. Basu samu matsala sosai ba don hidimar biki ta sanya ma ba wanda ya hadu da Modibbo sai dai a wurin yaran su Adda Salma da sauran yan uwa, sun sha hantara.

Sai da aka kammala bikin sannan Dada a karo na biyu ta kwashi yaran suka shiga bangaren Modibbo don su gaidashi su yi mishi sallama, wancan karon ya ganta sarai amma ko amsa gaisuwarta bai ba.

Modibbo zaune shi kadai a falonsa, ta samu damar shiga dalilin ranar girkin Amarya ne. Yana ganinsu ya daure fuska tamkar bai taɓa dariya ba.

"Ke har yanzu ba ki tafi ba?"

Dariya ta ɗan yi.

"Eh, amma gobe zan wuce. An yi biki, Allah Ya..."

"Dakata, ke har wani bakin alheri ne da ke? Ai ni kaf zuri'ata ba za ta ga rashin alheri ba. Tashi ki ficemin daga gida! Zaman ya isa hakanan, biki ya ƙare tunda kin zo gayyar soɗi ai sai ki tattara ku koma."

"Dada tashi mu tafi! Ba zamu kara dawowa ba! Na tsaneshi!"

Da sauri Dada ta kalli Hussein ta rufemasa baki, shi kuwa Modibbo ya mike ya zo ya fisgoshi.

"Kai! Dan iskan yaro, ni sa'anka ne? Haka aka koyamaka ka zageni?"

Ya bubbuge bakinsa kafin ya murɗe kunnensa, Hussein sai huci kawai amma kukan ma ya ƙi yi. Dada na hawaye yaran na tayata ta mike ta ja hannunsu ta fito ba ta kara magana ba.

Sosai ta gargadi yaran akan kar wanda ya fadawa Baba Naziru abinda ya faru, suna cike da ɓacin rai da jin haushin Modibbo wannan ta sa ba su amsamata ba. Ba ma kamar Hussein da ya ji duniya ya tsani mutumin.

***
  Tafiya na ci gaba da tafiya, yan biyu suka kammala Sakandire, a sannan sun zama matasa, Hassan na sanya farin  gilashi a sannan a dalilin matsalar ido da yake fama da shi. Wannan ne ya taimaka wurin bambance su.

Baba Naziru bai yi ƙasa a gwuiwa ba wurin nema wa kowannensu gurbin karatu a fannin da yake so, AlHassan ya samu fannin Accounting  a jami'ar Oxford, London. Yayinda Hussein ya tafi AUD a Dubai.

***
Tsakaninsu da Nijeriya sai an musu hutu.  A wani zuwan ƙarshe da Hussein yi hutu, don wani lokacin hutunsu kan bambanta da na Hassan. Hutu wanda daga shi kuma sai kammala karatunsu. Bisa tursasawar Dada ya ziyarci ƴan uwan Babansu. Sosai ya samu tarba a hannun Adamu da Karime kamar koyaushe, zuwa Kanon da Dada ta ƙaƙaba ya fi komai dagula lissafinsa.

"Nikam ba zan je ba." Cewar Hussein ransa a tsananin ɓace. Daƙuwa Dada ta mishi gami da harara, ya kauda kai.

"Duk rashin ƙaunar da zai nunamaka ai hannunka bai taɓa ruɓewa ka yanke ka yar ba. Mu mun san muhimmancin zumunci don haka dole ne ka je idan har na isa da kai."

Ganin yanda ta dage har da ɓata rai yasa shi lallaɓa ta ya kuma shirya tsaf ya bi motar kasuwa ya tafi har da tsaraba Dada ta shirya ya kai.

Tun a ƙofar gidan Kawun ya soma cin karo da samarin gidan, haɗe girar sama da ƙasa ya yi kamar bai taɓa dariya ba ya ƙarasa. Ciki-ciki ya yi musu sallama sai dai ba wanda ya yi yunkurin amsawa, wannan ya fi komai ƙular da shi. Wato don ubansu har sannan ba su ɗauke su wata tsiya ba. Ya yi kwafa ya karasa ciki. Ba laifi ya samu tarba daga Amarya sosai, ganin haka ya ƙi shiga ɓangaren Hajja Fatuma ya shantake har dai ta sanarmishi da shigowar Kawun daga kasuwa. Tsam ya miƙe ya nufi sashinsa. Yana zaune saman kujera ya shiga da sallama. Dubansa ya yi yana mai amsawa sai dai ganin ko waye ya karasa amsawar ciki-ciki. Hussein ya taɓe baki don dama ya shirya ganin fiye da hakan.

"Barka da yamma." Ya gaida shi a ladabce.

"Kai, me ya kawo ka gidana?"

Kallonsa ya yi kyam.

"Zumunci."

Kawu ya ji wutar tsanar Hussein ta ƙara ruruwa a ƙoƙon ransa, shekaru kusan bakwai rabon da ya tako gidansa, Alhassan kan shigo koda ba ya so.

"Na lura ba ka da kunya! To ko Aminu ubanka bai isa ba balle kai! Ni na fi ƙarfin tsagerancinku! Illar auren bare kenan...

"Ubana Aminu ya rasu, gidan da ya je ba wani da zai dawwama a duniya bai je ba. Gidan biyu ne, wuta da aljan. Don Allah Kawu ka yimin dukkan zagi, banda ambatar iyayena."

Miƙewa Kawu ya yi ma matukar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login