Showing 219001 words to 222000 words out of 226732 words
ma sauran mutane.
"Ka yi hakuri ɗana, ka yafemishi, idan ba ka yafe ba, da me zai ƙare ka? Me kake nema a duniya yanzu da Ubangiji bai maka ba? Babu shi, ka saka a ranka ba yanda ka iya, haka Allah Ya so ya jarabceka kuma Ya jarabta. Idan har na isa da kai, kuma har zuciyarka kana jin za ka iya yafewar, domin Allah muje ka fadi ya ji da bakinsa ka yafemasa."
Hussein wanda gaba daya jikinsa ya yi la'asar, ba shi da sauran kataɓus, miƙewa kawai ya yi suka fita tare da Dada zuwa sashinta. Ta ba Ramlatu umarnim biyo ta, hijab kawai ta sanya ta bisu a baya.
Kawu ya yi murnar sake ganin Husseini, da kansa ya mike jiki na rawa ya kasa gareshi ya rike hannunsa, kawai sai ya soma kokarin durkusawa yana kuka. Da sauri Hussein ya rike hannunsa ya ɗagoshi tsaye.
"Ya wuce Kawu, na yafemaka a bar zancen haka."
Ba wanda kalaman Hussein bai wa dadi ba, Ramlat ta gaishesu, itama dai gafararta Kawun ya nema, take kuma ta ce ba komai ya wuce.
Nan fa gida ya yi dadi amma Hussein bai wani sake sosai ba, sai da aka yi Magriba kafin su Kawu su wuce, Baffa Surajo ya ce lallai gobe duka a hadu a babban gida yana neman kowa da kowa. Ya bada umarnin a sanarwa wanda ba ya nan, na nesa kuwa a rabu da su. Da wannan komai ya wuce.
***
Washegari kuwa misalin karfe biyu, Baffa Surajo ya haɗa taron da kowa na zuri'ar Gidado dake a Adamawa ya hallara. Bayan addu'a da doguwar nasiha, ya ba Kawu damar neman afuwan yan uwansa. Nan Kawu ya ba kowa hakuri da kuma daukar alkawarin ba zai kara aikata ko makamancin hakan ba. Kowa ya ji dadin hakan kuwa, karshe kuma ya nemi alfarmar haɗa auren Taheer da Hafsat, nan take Dada ta ce ita ba ta da ja. Hussein zai yi magana ta harareshi, murmushi ya yi.
"Cewa zan yi an bayar." Maganar ta ba kowa dariya, Baffa Surajo ya yi mishi daƙuwa.
"Ai ba kai ke da alhakin bayarwar ba."
Bai ce uffan ba, Hafsat kuwa ai kamaran mata albishir da gidan aljanna.
***
MURFI....
[3/17, 9:18 AM] +234 703 629 0938: I just published "BABIN ƘARSHE" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1035704431?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=ahGlFX6GFRN4rYLxQybIWR9WrkgGWE36szhMfA7kRFxFwQXwS03Sgp8YSmnHzMO1lgoFTgL30%2Brf0xbkWKei5hlm6ZnndGuZExstbOwboUAs%2BBmTygvZgHsBmhnEg64g
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA* 🕯️
_Rufaida Umar_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
*BABIN ƘARSHE*
ADAMAWA
BAYAN WATANNI BIYAR..
Amarya Ramlat ta kara kyau da ƙiba sai dai ba irin mai munin nan ba. Sanye take cikin doguwar riga na leshi lemon green an mata dinkin bubu, ta fito daga motar yayinda Hafsat da Rasheeda suka yi gaba niƙi-niƙi da kaya, ita kuwa tare suka jera da Kausar rike da wasu ledojin. Dawowarsu kenan daga kasuwa, zuwa lokacin sun yi nisa da shiryen-shiryen bikin Hafsat har ma da Rasheeda wacce za ta auri ɗan Barrister Hansatu (Babbar Yayar su Kawu Modibbo), Mujaheed.
Tun da suka rubuta jarrabawar karshe kasancewar tare suke tafiya da Hafsat a karatu, sai Rasheeda ta tubure ta ƙi zaman Kano, ta dawo gidan Adamawa wajen Dada ta yi zamanta. Wannan abu ya yiwa Dada dadi, wai yau ta budi ido ta ga jinin Kawu Modibbo a gidanta, kuma da son ran mahaifin, sai ta ji inama ɗan uwanta baban su Hussein na raye ya ga ranar da ya dinga ce mata za ta zo in sha Allah, ashe kuwan tana tafe.
Hamida babbar ƴar Dada wacce aure ya lula da ita har Saudiyya, ta jima rabonta da ƙasar don ko Ramlat tsakaninsu sai dai ta waya ko kuma idan ta kira Hussein videocall suke gaisawa. Ta dube su da kulawa tana ba karamar ɗiyarta Mama.
"Sannunku da zuwa. Kun sha wunin kasuwa."
Suka yi murmushi lokacin da kowa ke kokarin zama.
"Wash!" Fadin Hafsat tana mai kwantar da kai jikin Dada. Ture ta Dada ta yi.
"To raguwa, ni matsa ki ban wuri. Gwara ma ki tattara ki bar gidannan ko na huta."
"Aa Dada, ina hutu ba kya ganin Auta? Faɗa dai ki ke yi."
Cewar Adda Zahra, mai bi wa Hamida, ita a Lagos ta ke da zama.
Aka yi dariya. Haka kuma aka shiga bude kaya ana ganin siyayyar da suka yi na abinda ya yi saura na tarkacen kayan girki har ma da sauran kayan kicin da ba'a siya ba. Sosai an yaba da kayan, sai da suka ci abinci kafin Ramlat ta koma sashinta. Wanka kawai ta yi don wani irin zafi ta ke ji, ta sanya kananun kaya riga da siket marasa nauyi kafin ta faɗa kicin. Lissafi ta shiga yi a ƙasan ranta, su Rafee'ah bai fi saura kwanaki shida su zo ba saboda biki. Ta ƙagu ta ga yaranta da kuma Aisha da babynsu. Ta shafi cikinta kaɗan tana murmushi, tana burin Allah Ya ba ta haihuwa ko don ta ga kalar farin cikin Hussein wanda yanzu koyaushe ba shi da zance sai na baby, baby. Haka dai Ramlat tana aiki tana tunane-tunanenta. Sai da ta yi nisa, sai ga Kausar ta shigo, itama kam ciki ne da ita wata uku. Sallama ta yi mata akan za ta tafi, har ƙofa ta yi mata rakiya.
"Kai aa ki koma hakanan, ga mijinki can na baro sashin Dada, idan ya ganki haka kin fito ai ni zai ɗorawa laifi."
Ramlat ta yi dariya, sai yanzun ta tuna da kalar suturar dake jikinta. Ko ba komai daga rigar mai hannun vest har siket din wanda yake dogo amma kamar roba, duk sun matse ta.
"Toh Maman Twins, Allah Ya saukeki lafiya. A gaidamin da Fatina sosai."
"Twins dai yana jikinki Madam, amma ba ni ba. Ki bar yimin wannan fatan. Fati kuma za ta ji sosai."
Ramlat abin ma ya ba ta dariya, tana mamakin yanda Kausar ke gudun twins. Ita kam da ace za ta samu tana son abinta. Anan dai suka rabu ta koma kan aikinta. Babu jimawa Gogan ya shigo. Ganin tana kicin kawai ya nufi ɓangarensa ya watsa ruwa. Duk tana ji, Allah Ya taimaka dama girkin ƙarashe ne don ta dafa markade ta kuma yi tafashen kazarta kafin su wuce kasuwa. Wannan yasa kawai miyar ta haɗa ta kuma dafa kuskus da ya sha karas da koren wake. Komai ta haɗa a gaggauce ta kawo falon ta jera saman ledar cin abinci.
Ƙamshinsa ya soma dukan ƙofofin hancinta, ta ɗaga kai ta kalleshi. Wando ne mai jikin cotton ya sanya sai farar tshirt mai gajeran hannu. Koyaushe Hussein ƙara kyau yake yi a idanunta, kullum ƙuruciyarsa ta ke gani. Har kullum idan zai fita daga gida hakanan sai ta ji wani kishi ya kamata. A kwanakin baya sai da ta kwashi takaici sadda wata Meena ta matsa mishi da kira, hankalinta bai kwanta ba sai da ya tabbatar mata babu komai tsakaninsu karshe ma ya rufe Meenar ta yanda babu damar da za ta ƙara kiransa. Da wannan ya samu hankalinta ya kwanta.
Har ya ƙaraso ta shagala ba ta ko lura ba sai da ya kai hannu ya shafi mafi soyuwa a wajensa. Ta dawo hayyacinta ta sauke ajiyar zuciya lokaci guda ta ɗan harareshi da wasa gami da murguda baki. Ya shafi lebbanta da yatsa hana murmushi.
"Ni kike wa haka? Tunanin me kike?"
"Ba komai."
Ya matso da ita jikinsa ya kwantar da kanta saman kirjinsa.
"Ko? Faɗamin gaskiya Malama."
Ta lumshe idanu tana shaƙar ƙamshinsa mai sanyamata nutsuwa.
"Dagaske fa ba komai. Tunaninka nake yi."
Ya sumbaci saman kanta yana murmushi.
"Uhum, faɗamin, me kike tunani alhalin ni ɗin naki ne."
Ta yi wani tattausan murmushi a hankali ta ɗago kai har hancinta na gogar sajensa. Suka dubi juna. Ya ja karan hancinta.
"Ko ba haka ba?"
"Hakane."
"To kin gani, me zai dameki?"
Ta jinjina kai kawai ta murmusa. Nan kuma ta zubamishi abincin, koda ta ce ta ci bai matsamata kan lallai sai ta ci ba.
Haka dai a kwanakin nan kusan kullum sai sun fita siyayya, sai da suka jera kwanaki uku, kafin Hussein ya murtuke ya ce abin ya ishe shi. A gaban Dada aka yi, suna zaune ne sai ga Waleeda cikin shiri ta dubi Ramlat.
"Adda Amal, muje ko?"
Ya haɗe fuska, ita kuwa Ramlat da ido ta nunamata Hussein alamar bai yarda ba. Waleeda ta dubeshi baki sake sai dai tuni ta haɗiye abinda ta yi niyyar faɗi dalilin kallon da ya yi mata. Dada ta dara.
"To kai Husseini banda abinka, ai fitar ta su ce, ɗinkinsu za su kai. Ka yi hakuri su je a auna su."
Ya mike zaune.
"Aa bari na aunata sai ita Waleedar ta kaiwa telan. Ba shikenan ba?"
Kunya ta kama Dada, ba ta kara uffan ba ta mike ta yi daki, Hussein dama ba yau ya saba ɓaram-ɓaramarsa ba. Ramlat da ta ji kamar ta nutse ta rasa bakin magana. Waleeda dake dariya ciki-ciki ta dubeshi kawai yayinda Hamida ta hau dariyarta sosai a fili don kusan sa'anni suke da ƴan biyu. Sai da ma ta faɗo duniya da watanni biyu aka haifesu.
"Me na ce ne?"
Ya furta yana neman ba'asi ganin Dada ta mike ta yi daki, su kuwa na falon na dariya.
"Au ba ka san me ka ce ba kenan? To ai Dada wuri ta ba ka idan ka auna matartaka sai ta dawo."
Ya taɓe baki yana yamutsa fuska.
"To meye a ciki? Dada dai ta so jin kunyarta ne. Idan muka haifamata jikoki ta daina. Tashi ita kuma wannan ta ɗauko abin awo."
Ramlat ta mishi wani irin kallo kamar ta yi kuka. Ya yi murmushi ya girgiza, kallon ya ji shi a dukkan wata gaɓa ta jikinsa. Miƙewa ya yi ya mata duban zan haɗu da ke kafin ya musu sallama ya fice wurin aiki, lokacin goma da ƴan mintuna.
"Dagaske dai mijinki bai bari ba. Ai shikenan, kawai ki ɗauko rigar da za ta yi maki daidai a yi amfani da ita."
Waleeda ta faɗi tana murmushi. Kafin Ramlat ta ce wani abu sai ga kiransa. Ta ɗaga da sallama.
"Kwalliya ta biya kuɗin sabulu, amma kallon da aka yimin yanzu idan na dawo zan zauna a yimin sau ɗari. Kuna iya tafiya, Allah Ya tsare. Drive carefully."
Daga haka ya katse kiran bai jira cewarta ba, ganin yanda ta ke zabga murmushi yasa Hamida kallonta.
"Ya bar ki kenan ko?"
Ta gyada kai, suka yi dariya. Mikewa ta yi ta koma bangarenta, mayafi kawai ta dauko sai jaka da mukullin mota ta rufe ko'ina. Koda ta dawo, Dada na zaune ta dawo falon. Sallama suka yi mata suka wuce. Wani tsadadden leshi da ya haura dubu ashirin, iyakarsu ne kawai, iyalan Dada, surukai da kuma ƴaƴa, ranar Dinnerparty zasu sanya. Sai atamfar da zaa sanya ranar wuni gaba daya dangi. Sai kuwa wata shadda ta Ramlatun da za ta sanya ranar ɗaurin aure.
***
Ana gobe za'a sanya Amare a lalle ne, ƴan Kano suka iso, dama iyalan Kawu Modibbo tun ana saura kwana uku suma dira. Ramlat ta rasa inda za ta sanya su Rafee'ah don murna. Ga yaranta, Affan ya zama babban mutum, ba kuka sai ma yawan sunkuyar da kai wai shi a dole mai kunya. Yaran sun yi wata irin ƙiba da kyau ga murjewa. Ta dauki Babyn Aisha, kyakkyawa da ita, sunan Mahaifiyar Hisham ta ci su na kiranta da Afnan. Kyau kam wane iyayenta.
"Ke kina ta cewa wasu sun yi kyau, kina kallon kanki kuwa a madubi Ramlat? Lallai aurennan ya karɓeki tubarakAllah."
Maman Twins ke maganar tana kallonta sosai. Nan fa sauran suka shiga tofa albarkacin bakinsu, ba wacce zuwanta ya ba ta mamaki sai Bilkisu don ita Hunainah ba ta zo ba saboda laulayin ciki na biyu da ta ke yi, ba ta jima da haihuwar ɗanta ba kafin ta kai ga yin wani tsarin iyalin sai ga ciki. Bilkisu kuwa wata uku kenan da dawowarta gidan Muniru, nan ma sai da ta sha baƙar wuyar rayuwa a gidansu, ta duba ta hango babu rayuwar da ta fi ta gidan mijinta dadi wannan yasa dakyar da siɗin goshi ta lallaɓa Muniru har ya sauko ya maidata ɗakinta. Tun komawarta musamman ganin su Yasmeen babu wani alamar wahala tattare da su, sai ta yi sanyi, ta kuma karɓi Hunainah hannu bibbiyu suka zauna lafiya.
Hussein sosai ya ke jan yaran a jiki, wani irin so da kaunarsu ya ke ji na musamman a ƙasan ransa har yake ji inama daga jikinsa suka fito. Ya yi amannar son da ya ke musu, ko mahaifinsu sai hakan. Ramlat kuwa banda murmushi ba abinda ta ke yi, ganinsu tare na karamata annashuwa. A ranar dai da kansa ya ce ta kwanta tare da yaran, ya tabbatar ta yi kewarsu.
Washegari aka shiga cikin biki, komai ya tafi cike da tsari. Ranar babu batun anko don kowa kayansa ya sanya, a rana ta biyu ne suka gudanar da yini da rana wanda kowaccensu ta sha ankon atamfa har su Aisha mutan Kano, don tun kafin su zo Ramlat ta aikamusu hoton ankon suka ɗinka.
Tun soma sabgar biki ba ta da wani lokacin kanta balle kuma na Hussein, hira ta ragu sosai a tsakaninsu. Sai dai ta kai mishi abinci, zaman da za ta yi wurinsa bai fi na mintoci ba. Wannan abu ya kai Hussein bango, gaba daya ma sai ya daina bari su haɗu. Da daddare idan ta leƙo, ya rufe kofar gam, da safe kuwa duk irin sammakonta ya fice daga gidan, waya kam ko ta kira bai ɗagawa. Text na duniya ba ya kulata, sam ya kasa yi mata uzurin tana da baƙi kuma su na hidimar biki. Wannan damuwar ta sa a ranta, shiyasa ko ranar da ta kama na dinnerparty, kasa wani kataɓus ta yi. Tana zaune tana kallon kowa na shiryawa, maganar duniya su Zulaihat da su Kausar sun mata akan ta tashi ta shirya amma ta ce sam ta fasa.
"Adda Amal kina cewa ba za ki je ba, ga Hamma Hussein can ya ci uban kwalliya ya fita, kuma wallahi idanun ƴanmatan nan kamar su tsiyaye tsabar kallonsa."
Jin abinda Falmata yar uwar su Hussein ta Maiduguri ta fadi, ai sai Ramlat ta mike tsaye ranta na susa. Nan aka kwashe da dariya, har itama ta murmusa.
"Kishi kumullon mata, ki zauna dai kar ki je. Wallahi sai dai ki ji ana wani labarin."
Ita dai Ramlat ba ta biyewa zancen Rafee'ah ba ta shiga bandaki bayan ta rage kayan jikinta, tana ji su na mata dariya. Wanka ta ƙara yi duka rabin hankalin na ga tunanin Hussein, abinka da zuciya, sai nan da nan ta ji itama ai ya mata laifi, ta ji ya bata haushi sosai. Kwafa ta yi tana ƙara cuɗa sabulu a jikinta, aikuwa ta ci alwashin itama ko kallo bai isheta ba a wurin taron. Ta fito ta shirya, da yawansu sun fice har su Rafee'ah da maman Twins. Aisha da Falmata da kuma Asma'u diyar Hajja Fatuma uwargidan Modibbo sai wata Hannatu itama daga Maiduguri, su ne kadai suka yi zaman jiran Ramlatun don su wuce a motarta.
Leshinta da suka yi anko kalar milk kai adon golden brown ya yi masifar sama a jikinta, ya sha aikin stones shi ta fiddo ta zura. Falmata ta yi mata make-up na fitar hayyaci, kasancewar kwalliyar zamani mai kama da na aljanu bai damu Ramlat ba don ba irinsa ta fi yi ba, sai ta fito ta yi wani azababben kyau. Daman su Rafee'ah yanda suka ga ta sauya fatarta ta kara kyau da sulɓi yasa suka dinga yi mata zargin mai ciki, ita kanta sauyawar na ba ta mamaki.
"Wallahi na fadamaki wani abu? Nidai ba ki taɓa kyau irin na yau ba, ko bikinki albarka."
Aisha ce ke maganar tana dariya, harararta Ramlat ta yi ta ja guntun tsaki ba ta ce komai ba, wannan duk abinda ta yi ɗanawa Hussein tarko ta ke son yi yanda zai yi dana sanin wannan fushin da ya ɗauka da ita. Har tunani take ko wa ya sanya a gaban mota suka tafi? Nan fa ranta ya ƙara sosuwa. Ta mike ta yafa mayafinta golden ta dauki purse dinta mai kyalli shima golden, turare mai sanyin ƙamshi ta fesa kafin ta zura takalminta da ya kasance mahaɗin purse din, ta dauki mukullin motarta. Kuɗin liki kam dama tuni sun tsufa a cikin ƴar jakar don tun safe suka bada aka yi masu chanji kowacce ta adana abinta.
"Muje." Ta basu umarni, duk suka fito ta rufe ko'ina na gidan. Su Ummi na sashen Dada da yara ana ta wasa don yanzu ba su fiye wani kewar uwartasu sosai ba balle su liƙe mata.
Tana tuƙin amma fuskar ba wawalar a zo a gani musamman da ta ga dagasken dai babu motar Hussein a farfajiyar gidan. Aisha ta karanceta tsaf, ta san kishi kawai ke cin ƴar uwarta don haka ta bar janta da hira ta maida akalar hiran ga su Falmata dake zaune a baya haka har suka isa ƙayataccen ɗakin taron na FARHAS Event Centre (Dan Adam).
Farfajiyar wurin sai ɗaiɗaikun jama'a, sai da duk suka fita, sannan ta bi bayansu. Aisha ko jiranta bata tsaya yi ba don ba ta son a huce a kanta. Ta na takunnan mai girgiza zuciyar masoyinta kuma mijinta, wanda ya zama normal tafiyarta. Haka ta ƙarasa har ta shiga ciki. Wuri fa ya cika, gaba ɗaya kowa na zaune ana kallon MC wanda ya fiddo Amare da Angwayensu tsakiya yana basu umarnin zama saman wasu kujeru a tsakiyar wurin, wannan yasa hankalin da dama suna kansu ana dariya a nishaɗance. Sun haɗa ido, sai ta dauke kai kamar ba ta ganshi ba, wani irin tururi kanta ke yi ganin wata kyakkyawar budurwa a gefensa zaune, shi kuwa AlHassan Madam dinsa ce a gefensa sun ba MC hankulansu. Takaici ya sanya kawai ta ja kujera ta zauna ba tare da ta ƙarasa wurin su Rafee'ah ba, sai ma bayan ta zauna ta ɗago kai ta ga ashe ƴanmatan gidan kakannin su Hussein ɗin ne.
"Kai Adda Amal you look beautiful wallahi."
Ta dubi mai maganar Teema ta yi murmushin da bai kai zuci ba.
"Thank you. Kuma kun yi kyau."
Daga haka ta maida hankali da fiddo wayarta dake faman vibrating, ganin lambar Hussein kawai sai ta maida wayar jaka. Tana ɗaga kai kuwa ta hango su Kausar na ɗaga mata hannu alamar