Showing 144001 words to 147000 words out of 226732 words

Chapter 49 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12485

ba ta ƴaƴa."

Daga nan ta bankaɗa labule ta fice, ba  ta jin za ta iya jiran yin sallama da Amarya. Babu inda ta ƙara shiga a gidan haka ta fice tana hawaye.

  Tafiya ta ke ƙafafun na harharɗewa, kalaman Kawu daki-daki ta ke tunawa tana ƙarin fahimtar dagaske dai akwai hannunsa a cikin ɓatan Hussein.

"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un!"

Ta ambata a fili, tausayi sosai da wata irin ƙauna ta Hussein ya ƙara mamaye zuciyarta. Ji ta ke komai za ta iya aikatawa muddin hakan zai dawo da Hussein cikin ƴan uwansa. Wayarta ta yi ƙara, Hajiya ce. Yanda ta ke kuka ba ta jin za ta iya amsawa, don haka ta mayar da wayar jaka. Kafin ta bar lungun sai da ta tsaya ta saita kanta ta share fuska. Abin hawa ta tsayar ta faɗa.
"Malama ba ki faɗi inda zan kai ki ba."

Ta haɗiyi miyau. Dakyar ta faɗi sunan unguwar ta yi shiru, kanta ke sarawa ga wani zazzaɓi-zazzaɓi.

***

Tsam! Modibbo ya miƙe ya shiga ɗaki, Amarya na zaune na kallon wani ƙaramin bidiyo na Ibro tana dariya, ganin mutum ya faɗo ba sallama ya sa ta ɗan razana kafin ta sauke ajiyar zuciya. Tun kafin ta nemi ba'asi ya katsemata hanzari. 

"Fita zan yi, ki je kawai idan na dawo zan kiraki. Akwai uzurin da zan gabatar."

Ya faɗi a kausashe, ta miƙe jikinta a sanyaye ta fita fuskar cike taf da tarin tambayoyin da babu mai amsa mata sai Ramlatu. Sai dai sama ko ƙasa babu ita, hatta su Rasheeda sun yi mamakin da ba ta biyo ta musu sallama ba.

Fitar Amarya ya ba Kawu Modibbo damar buɗe sif ɗinsa ta kaya, can ƙasan ya zura hannu ya ɗauko wani ɗan akwati mai girma da duk faɗin gidan babu wanda ya isa ya taɓa. Hankalin ma bai kai gareshi ba. Cikin rigarsa ya zaro mukullin da ba ya rabo da shi a jikinsa, ya buɗe, kwakwalwa ce! Kwakwalwa ta ƊAN ADAM! Ta yi baƙiƙirin a madadin jan da ta ke da shi har da jini-jini a shekaru masu yawa. Idanun Kawu Modibbo suka kaɗa.

"Ita ce! Ita ce yarinyar!"

Abinda ya faɗi kenan a fili kafin hannu na rawa ya maida ya rufe. Gumi ya shiga tsastsafowa daga fatar jikinsa. Ya sa hannu ya share. Tun komai bai ƙarasa lalacewa ba zai yiwa  abin tufka. Ya ayyana hakan a ransa yana jin tsanar Hussein tsagwaronsa a fili da ɓoye. Miƙewa ya yi ya dauki waya ya danna kira direbansa.

"Kana ina?"

Daga can aka ba shi amsa kafin ya dora.

"Ka fiddo mota, fita zamu yi."

Daga nan a gaggauce ya dauki hula ya rufe kansa ya fita yana zuba sauri.



***
  Ramlat bakinta ya yi mata nauyi, ta kasa ba Hajiya labarin abinda ya faru. Damuwar da ke kwance samam fuskarta yasa Hajiya ta fahimci ba lafiya. Ganin ta shige daki sai ta mara mata baya.

"Ke mene ne wai? Shi Kawun ne ba ki samu gani ba ko wani abin ne ya faru da Husseinin?"

Girgiza kai ta yi. Tunanin ta faɗa ɗin ya rinjayi komai, ko ba komai Hussein na bukatar addu'a, don haka ta karya bille ta labartamata duk yanda suka yi da Kawun. Hajiya ta saki salati.

"Ni Rabi wannan rayuwa da ban mamaki. Ban taɓa jin labari makamancin haka ba tunda uwata ta haifeni. Kai.."

Hajiya sai ta soma hawaye, ita kanta tausayin Hussein ke ɗawainiya da ita. Hatta da abokin haihuwartasa ma tausayinsa take ji. Miƙewa ta yi tana jan hanci.

"Addu'a zamu dage da yi, ke kanki yanzu ki dage da addu'a don mutum idan aka ce mugu ne komai ma zai aikata. Bari na kira Malam na faɗamasa, shima ya tayamu da addu'a."

Daga nan Hajiya ta fita ta bar Ramlat da tarin damuwa. Dakyar ta iya mikewa ta ɗauro alwala ta gabatar da sallar isha'i, zaman dirshan ta yi saman dardumar jefi-jefi tana sharar hawaye.

Addu'a sosai ta yi kafin ta miƙe ta nufi gefen gado ta zauna. Hayaniyar su Affan ta ishe ta don haka ta kora su waje. Waya ta ɗauka ta hau kan whatsapp, babu alamar Hussein ya hau. Yau ɗaya ta ɗaura ɗamarar kiransa. Don haka ta sauka ta danna masa kira. Wayar a kashe. Damuwarta madadin ta ragu sai ta ƙaru, ganin dukan na nema ya yi mata yawa, sai ta miƙe ta koma falo ta yi jugum. Ba jimawa Hisham ya kirata. Ta ɗaga.

"Antinmu shiru, ina jira na ji yanda ku ka yi."

Ta haɗiye hawayenta da ɓacin rai. Komai ba ta ɓoyewa Hisham ba, ya dinga salati da salallami karshe dai ya kwantar mata da hankali.

"Kar ki sanya damuwa a ranki Ramlat, in sha Allah kamar yanda kika ce toh hakan ne, Allah Ya fi su. Mu dage da addu'a."

Ta amsa da toh. Kamar ta tambayeshi ko sun yi waya da Hussein sai ta share.

***
Washegari haka ta shirya ta fita wurin aiki ranta a jagule. Ga wayar Hussein da ke a kashe. Ta gwada kira har cikin dare don tsautsayi amma ba ta shiga. Tuƙi ta ke kusan ba za ta ce a cikin hayyaci ba. Don haka ba ta kawo da cewar an basu hannu ba sai da ta ji wani ruɗaɗɗen Hon daga bayanta. Hakan ya fusata ta, ta madubi ta ke duban mai shi. Ido da ido suka kalli juna, yana cin magani. Wannan karon ba Tinted glass din  a motar da yake. Yanda ya ɗaure fuska ba alamun fara'a ya fi komai ruguza lissafinta. Asalima ba wani wawan overtaking da ya yi ya kaɗa hancin motarsa sai da ya daskarar da ita ya jazamata ɗaukewar numfashi na ƴan dakiku.

"Me nayi masa?" Ta ambata a fili, da rawar jiki ta ja motar bayan ta gaji da tsinuwa da zagin mutanen da hankalinta ba'a kansu yake ba. Koda ta gangara sai ta nemi wuri ta tsayar da motar. Hankalinta ya gushe na ɗan lokaci. Tunaninta abinda ta yiwa Hussein, shi dai ta gani kamar yanda ya gan ta amma ya kauda kai. Wannan abu ne da bai taɓa afkuwa ba tsakaninsu. Ta ɗauki wayarta da karar shigowar saƙo ya katsemata tunani, kuɗi ne har dubu ɗari aka aikomata. Ta kai duba ga lambar mai account din. Aliyu Dikkl. Hakan ta gani a rubuce. Ranta ya ƙara ɓaci, ga babu lambar acc balle ta mayarmasa. Ta ja tsaki. Kai tsaye ta ƙara kiran wayar Hussein, wannan karon ringing ta ke yi sai dai har ta katse bai ɗaga ba. Ta kuma kira nan ma shiru, a karo na uku ma babu alamar za'a ɗaga. A na huɗu sai ji ta yi an kashe wayar gaba ɗaya.

"Meke faruwa?" Ta ambata a fili. Kawai sai ta ji zuwa wurin aikin ma ya fita a ranta, don haka ta ba kanta mintuna kusan biyar a tsaye tana jin karatun Alkur'ani tana hawaye kafin daga bisani ta samu ƙwarin gwuiwar da za ta tashi motar. Gidan Amrah ta nufa, a hanya ta kira ɗaya cikin abokan aikinta, Hindu. Uzurin rashin lafiya ta bayar domin dagasken ba ta jin dadin zuciya da gangar jikin.

***
Amrah ta yi mata duban tsanaki bayan gama sauraron dukkan bayanin Ramlat. Ita kanta kwallar ce ta cicciko mata.

"Yanzu AlHassan ɗin bai shigo ba?"

Ramlat da kanta ke jikin kujera sakamakon zazzaɓi-zazzaɓin da ta ke ji. Ta girgiza kai murya a dusashe.

"Mun yi waya da shi yanzu da zan fito, abin hawa ne ba'a kammala gyara mishi ba, yana tunanin ma bar musu zai yi ya biyo motar kasuwa."
 
"Kai! Wannan lamari akwai wata sarƙaƙiya a cikinsa Ramlat. Sai dai kuma ki zauna don Allah ki yi tunani ko dai akwai abinda ki ka aikata ga Hussein har ya ɗauke maki wuta haka? Ni fa gani nake da walakin goro a miya."

Cike da damuwa ta ɗago ta zauna sosai tana duban Amrah da ciki ke ƙara girma.

"Da ace akwai abinda nake jin zan ba dukkam girma da kulawa bayan iyaye, ƴaƴa da ƴan uwa, wallahi ya biyo bayan Hussein. Kin san ni, kin kuma san halina Amrah. Ina son Hussein, son shi nake yi da ban san iyakarsa ba. Akan me zan ƙuntata masa? Ni duka-duka ma yaushe rabon da ko chatting nayi da shi balle haɗuwa face to face? Ban sani ba, ban san me na yi ba. Ni dai babban burina koda zai zama abu na ƙarshe da zan mishi, shi ne na sada shi da ƴan uwansa da taimakon Allah."

Amrah ta jinjina kai, shakka babu Ramlatu na son Hussein, so mai yawa. Tana tsoron tarihi ya maimaita kansa idan har dangin uwa da uba suka dage mata akan auren Chairman. Sauƙinta ma wannan karon su Hajiya na goyon bayanta.

"Ko Hisham zan tambaya?"

Maganar Ramlat din ta maido ta hayyacinta. Gyada kai ta yi.

"Ki tambayeshi tunda amininsa ne. Ba zai rasa abinda ya sani ba."

Da haka ta danna wa Hisham kira. Yana ɗagawa suka gaisa.

"AlHassan din ya iso kenan?"
Ya nemi sani.

"Aa, wannan tsakanina da Hussein ne."

"Ina jinki Ramlat."

Ta ba shi labarin irin sauyin da ya ke mata.

"Ko akwai wani abu da ya ce maka na yi mishi don Allah?"

Shiru ya biyo baya kafin Hisham ya ce.

"Ya Salam!"

Jin haka ta gyara zama tana kallon Amrah don dama a speaker ta sanya. Suka nutsu.

"Meyafaru?" Ta tambaya kirjinta na dukan uku-uku.

"Ki yi hakuri, ina ga wannan laifina ne, yanda na ɓata kuma ni zan gyara. Kar ki damu don Allah. Zan kira ki anjima ko kuma ince zai yi kiranki da kansa. In sha Allahu."

Daga haka ya katse kiran. Suka dinga mamaki. Tunanin Ramlat me Hisham ya faɗawa Hussein?

"Hisham ya san batun aurenki da Chairman?"

Amrah ta nemi sani. Maganar Ramlat ji ta yi kamar an sokamata mashi a ƙahon zuci don haka maimakon amsa sai ta harareta ta ja guntun tsakin da ya ba Amrah dariya.

"Allah Ya ba ki hakuri. Mancewa nayi fa."

Ta cije lebɓa gami da girgiza kai ba ta ce komai ba.

***
MISALIN ƘARFE SHA ƊAYA..

Rubutu yake kamar wani Mango Park ba ya ko kallonsa, Hisham ya ƙuramasa idanu da mamaki. Ya sauya kamar ba Hussein din da ya sani ba.

"Malam ya ina magana ka kyale ni? Ba ka ji me nace ba?"

Ya ɗago ya dubeshi, ya ji, dukkan wani labari da ya ba shi, ya ji ba wai bai ji ba. Sai dai duk da hakan shi bai ga ta inda zai fara rage KISHIN Ramlat da ya ke ji ba. Ya soma yarda da abinda ya ƙaryata da gangan, ba kuma ya son sanya ta a matsala. Wannan ne dalili sauyawar sai dai ya ji wani sanyi kaɗan a maimakon tsananin zafin da ya ɗauka a farko duk akan lamarin aurenta da Chairman.

"Kunne ke ji, kuma na saurareka. Ka yi kokari."

Harara Hisham ya watsamasa yana danne tausayinsa.

"Shi ne za ka share ni? Nima fa takanas na taso don wanke laifin Ramlat amma ina da abin yi ai. Aikina na baro na zo."

Wannan ne karon farko da ya yi murmushi daga jiya zuwa yanzun, Hisham yana da raha. Ko ya ya ka zauna da shi sai ya sanyaya ranka.

"I'm travelling to London."

"For what?!"

Yanda Hisham ya nemi sani a hargitse, hakan ya ba Hussein mamaki har ya kalleshi, ganin ya zaro ido sai ya buɗe tafukan hannu gami da ɗaga gira cikin dakiya.

"Me akai na razanar? Tafiya ce kawai ta 3months."

"Gwara da Allah Yasa na zo." Hisham ya faɗi a fili kuma a hankali. Da ace ba su haɗu ba ba zai sani ba kenan. Lallai dole su yi komai cikin gaggawa.

"Me ka ce?"

Hussein ya tambaya. Girgiza kai ya yi.

"Ba komai. Yaushe za ku wuce?"

Damuwa ƙarara a fuskar Hussein sai dai ba ƙaramin ƙoƙorin dannewa ya ke ba.

"Ba na jin za mu wuce satinnan. Ya dai danganta da samun Visa."

Ya faɗi a sanyaye.

'Innalillahi wa inna ilaihir raajiu'un!'

Hisham ya ambata a zuciya gami da mikewa.

"Ok ok, Allah Ya nunamana. Bari na wuce sai mun haɗu anjima."

Hussein ya bishi da kallo har ya fita. Abinda ya kawo a rai shi ne damuwa ce tsantsa na ganin za su yi nesa da juna. Ya dafe kai da hannu. Shi kansa damuwar ce ke cinsa, tunanin tafiya ya bar Ramlat da Chairman kan ci masa tuwo a kwarya. Sai dai ya tabbatar furta wata kalma a kanta zai zama kamar barazana ga rayuwarta. Hajiya Zeenat ta sha faɗamasa gami da cin alwashin kashe duk wata mace da za ta shiga rayuwarsa. Ba a bayan idanunsa ba, a gabansa ta ke faɗi ya na kuma ji a jikinsa fiye da hakan ma za ta aikata. A hankali ya ɗauki waya ya kunna Data wacce rabonsa da whatsapp tun ranar da Hajiya ta kwace wayar. Saƙonni suka shigo har da nata. Ya shiga ya karanta. Gaisuwar safe ce ta mishi gami da tambayar ko lafiya. Ya dinga binyana karanta hirarsu da bai fi a ƙirga ba. Murmushi sosai ya ke yi san nan ya bude hotonta yana kallo. Ya kai kusan minti biyar ba'a hayyaci ba, tashin hankalinsa ya ƙaru. A hankali ya rufe hoton ya aikamata saƙo.

-*"Ki sa ranki Hussein ɗan uwanki ne. Ya na buƙatar addu'arki a duk inda zai je. Akwai wani duhu da na kasa fita, ke na gani kin fitar da ni kin sadar da ni da haske. Ina fatan mafarkina wataran ya tabbata. Ban ce ina sonki ba, ban kuma ce ina tsananin kishinki ba, amma ina roƙonƙi akan kar ki yi garajen aure. Nemi zaɓin Allah. Ke ba yarinya ba ce. Ina miki fatan alheri koyaushe."*_

Ya aikamata ya kashe datar, dakyar ya ci gaba da abinda ya ke ransa a jagule.

***
Kawu Modibbo tsaye a tsakar falonsa. Safa da marwa ya ke yi yana ƙarawa. Babu wani cikin iyalinsa da ya yi ƙoƙarin dosar inda ya ke, Amarya kanta haƙura ta yi da kwanan ta koma sashinta ta kwana.

*_"Kamar wuta da ruwa, haka ta ke barazana ga ayyukanka. Na sha faɗanaka, ba kai ɗaya ke aikin ba, akwai masu yi. Naka kan rinjayesu ne wani lokacin, kamar yanda nasu kan rinjayi naka aikin. Ina tsoron shaida maka muddin ba'a kawar da yarinyarnnan ba, aikin shekara da shekaru zai lalace. Za'a rasa dukkan wata nasara a kansa. Abubuwan da ka ke gudun afkuwarsu a rayuwarka, za su afku!"_*

Waɗannan jawabi na Tsoho, shi ke yawo a kwanyar Kawu Modibbo suka kuma hanashi sukuni daidai da sakan. Daren jiya kasa runtsawa ya yi balle har ya samu damar baccin. Idan komai ya lalace, hakan na nufin bayyanuwar komai.

"Lokaci ya yi da za mu haɗa ƙarfi da ƙarfe da ke ZEENATU."

Ya furta a fili kafin ya samu wuri ya zauna kamar kayan wanki.

***

ƘARFE BIYU...
Ta karanta saƙon Hussein sau ba adadi, sai dai ba ta fahimci komai ba. Cewar ba ya sonta ba kuma ya kishinta wannan ya haifar mata da matsananciyar damuwa. Kukan da ta yi ya jazamata tsananin ciwon kai. Hajiya na ganin haka ta tsorata, abinda ya faɗo a ranta kada ace wani mummunan abin ya sami Ramlatu sanadin wannan yaro, bayan ta taimaka mata ta sha magani ta shiga tofe ta da addu'a. Ummi kam su na Islamiyya ba su da labarin wainar da ake toyawa.

Wuraren ƙarfe huɗu da mintuna ne. Wayarta ta yi ƙara, dakyar ta iya ɗagawa. AlHassan ne.

"Na shigo Kano, ina hanyar gidanku."

Ta amsa da toh, a daddafe ta miƙe, babu laifi kan ya daina sarawa. Ta shiga ta yi brush ta kama ruwa ta yi alwalar jiran la'asar. Fitowa falon ta yi bakinta duk jikinta ya yi mata nauyi. Hajiya na zaune tana amsa waya.

"Ita Ramlatun?!"

Hakan da Hajiyar ta faɗi ya ɗau hankalinta, ba ta katse ta ba har ta kammala wayar.

"Ke da kanki ki ka ba shi Dikko damar turo kuɗi? Yaya Bello ya shaidamin ai sun ma gama magana ya turomaki kudin aurenki ta akawun dinki da ki ka aikamasa."

Dafe kanta ta yi tana salati, kirjinta na bugu da sauri-sauri.

"Ni kuma Hajiya? Wallahi ban.."

Ɗif ta yi, sai lokacin ta tuno da kuɗin da ya turomata account. Ranta idan ya yi dubi ya ɓaci. Ta faɗawa Hajiya gami da nunamata sannan ta ƙara da faɗin.

"Amma wallahi ban san inda ya samu lambar account ɗina ba. Ban sani ba. Me ake nufi da ni wai?"

Ta karashe hawaye na son zubomata. A fusace Hajiya ta mike tana faɗa.

"Bari na je gidan! Ba su suka haifarmin ke ba don haka ba zan zauna rayuwarki ta ƙare haka ba Ramlatu! Idan shi Munirun ya kasa ni zan je na same su."

Daga haka Hajiya ta faɗa ɗaki ta bar Ramlatu da ruɗewa da kuma hawaye. Waya ta ɗauka ta kura Zulaihat ta sanarmata komai, itama hankali a tashe ta ce za ta je can gidan su Dada kar abin ya ɓaci. Hajiya ta fito ta kama hanya ta fita.

Mintuna talatin bayan fitar ta sai ga kiran AlHassan yana shaidamata zuwansa ƙofar gidan. Ta mike ta shiga ciki ta gyara fuskarta da ta kumbura. Dole haka ta haƙuranta fita hakan. Tuni an gyaramasa ɗakin Muniru na baya, ta yi mishi iso ya shiga yana bin ta da kallo.

"Lafiya dai ko?"

Ta yi murmushin yaƙe.

"Lafiya kalau. Sannu da zuwa."

Ya amsa karo na biyu, shi ba wannan ya ke da muradi ba. Labarin Hajiya Zeenatu da adireshinta ya ke da buƙata.

Abinci ta kawomishi ta kuma ce ya yi hakuri har su yi sallah tukunna. Daurewa ya yi ya amsa da toh sannan ta fice.

***
"Rai kan ga rai?" Hajiya Zeenatu ta faɗi tana murmushi da wani irin mamaki shimfiɗe a fuskarta tana duban Kawu Modibbo da ke zaune a ofishinta na A&Z. Ya share goshi.
[3/16, 1:55 PM] +234 703 629 0938: I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/rSOQW4y2Gcb




🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

46)


"Kin san dai ruwa ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login