Showing 189001 words to 192000 words out of 226732 words
sauyawar muryarta ya sanya shi ɗan matso da kai kaɗan yana murmushi, cikin rada-rada ya ce.
"Mece ce damuwarki? Hajiya Zeenatu ko kuma maganar aiki?"
Ta juyo da zummar harararsa, sai dai ganin irin kusancin ya kai har fuskarsu na dab da haɗewa yasa ta saurin ja baya tana maida numfashi. Shi kansa sai da ya ji wani yarr tun daga yatsar ƙafafunsa zuwa kwakwalwa. Ya sauke ajiyar zuciya.
"Ina iya tafiya?" Ta nemi sani a gaggauce.
"Kin gaji da ganina? Sati nawa ba ki ganni ba?"
Baki sake ta dubeshi. To ma duka-duka yaushe suka hadu a titi ya cashe mata? Sai kuma ta juya kanta kawai tana duban yatsun kafafunta.
"Shikenan, zan kiraki a waya. Kina iya tafiya."
Ta amsa da toh sannan ta nufi ciki.
"Ba ki ji ba."
Ya katse ta, ta ciji lebban bakinta don ita kam ba ta son kallonnasa, ta daure ta juya. Murmushi kawai ya yi mata. Sai aikin kallo, ta gaji da rashin maganar ta juya abinta zuwa ciki.
Yau kam duk juyinta tunanin Mijinnata ne, ta yi mamakin sauyinsa amma ta fi kyautata zaton kawai kewarta da ya yi ne ya chanja shi. Koda ta kammala shirin kwanciya, ta ji bai kira ba sai ta yi zaton ya yi bacci. Da Asuba bayan ta idar da sallah, ta zare wayar a chaji. Ga mamakinta missedcalls har biyar duk na Hussein sai saƙon da ya turo. Ta bude.
_*Kin kyauta kenan?*_
Ta yi murmushi, Hussein rigima kenan. Ita shaf ba ta tsammaci zai kira ba tunda har goma ta wuce ga kuma bacci na cin idanunta don kwanakinnan ba ta fiye samun yi sakamakon sammakon zuwa wurin gyaran jiki da ta ke yi. Madadin ta ba shi amsa sai kawai ta share ta jefa wayar gefen gado sannan ta fita gaida Hajiya. Koda ta dawo, biyawa ta yi ta tashi Ummi da Ansar su yi sallah. Ba ta ci wuya ba suka tashi domin sun riga sun saba. Kamar yanda ta yiwa Hajiyar, hakanan su ma suka shiga suka gaisheta.
Ƙarfe takwas a gidan Hajiya Bingel Sudan ta yi mata, ta yarda sosai da gyaran matar don ta san ta kan gyara. Duka-duka ba a sani jima da farawa ba amma gaba daya ta sauya, sai dai ba laifi Yayyunnata mata sun kashe kudi.
Koda ta koma gida ta iske kaya jibgi a falo, ashe kasuwa su Maman twins suka je. Tarkacen kayan kicin ne kala-kala da Munir ya bada a siya. Babu laifi kullum kudinsa daɗa albarka ya ke yi. A bakin Rafee'ah ta ke jin zancen furnitures, wai Baba Dakta ya ce komai da ya danganci wannan a barshi a hannunsa. Ta kara jinjina riƙon zumunci da kuma abota na Baba Dakta wanda bai taɓa bari sun koka da rashin Abba ba.
"Kai wannan Jug din ya yi kyau. Ga azumi ya taho, har na hango bakin Hussein yana kwankwaɗar lemu."
Rafee'ah ke maganar tana dariya, gaba daya suka sa dariyar har Ramlatu.
"Ke dai Rafee'ah ban san sadda za ki girma ba. Yara uku amma har yanzu da sauranki."
Rafee'ah na dariyar furucin Hajiya, Maman Twins ta ce.
"Ai da alama sai Baban Abba ya rangaɗomata kishiya."
"Shi ya isa? Taɓdi! Ai shiyasa ko magana ya dauko nake katseshi da cewa ko gidanmu daya tal na tashi na gani. Soyayya tun na yarinta har girma don haka kada ma ya fara."
Daƙuwa Hajiya ta mata.
"Ungo nan! Kin isa ki ja da ikon Allah? Yau Isma'il ya so aure ai kuwa baki isa ki hana ba. Ba gwara kishiyar ciki ba da a yi maki ta waje ba?"
Nan fa aka shiga hirar kishiya, Maman Twins na fadin ita kam tana ma ji a jikinta Baban Twins aure yake son yi tunda ginin da ya fara na bangare biyu ne. Ita dai Ramlatu ta yi shiru kawai tana duba kaya, idan abin ya ba ta dariya ta dara. Can kuma maganar ta dawo kanta.
"Kedai me kishiya irin Zeenaru take ko wa? Wallahi sai kin tashi tsaye da addu'a. Azkar safe da yamma kar ki bari ya wuceki. Ni na ji dadi ma tunda ba wuri daya zai haɗaku ba."
Ta dubi Maman Twins.
"A ina kika ji?"
"Ni ya fadawa. Na fi zaton akwai dai abinda ya ke nufi a kan matar, amma bari mu zubawa sarautar Allah ido. Ke dai kamar yanda Uwanin ta fada, ki zage damtse da addu'a. Ya sanar da ni ma zuwan matar Hassan da wasu cikin yan uwansu, amma ba gidansa za su sauka, masauki zai kama musu. Ba yanda ban yi ba da shi akan ya bari su zo nan yace babu komai."
Hajiya ke zancen ita dai ba ta da labari ma sai lokacin. Sai kuma suka koma batun rakiyar Adamawa, su na tantance wadanda ya kamata su je.
"Bilkisu fa? Ke an fadamaki Bilkisu za ta shiga sabgar Ramlat?"
Rafee'ah ta tambaya da mamaki jin Maman twins na batun Bilkisu.
"Toh aikuwa za ki sha mamaki tunda Munirun da kansa ya sanarmin cewa za ta je. Kuma ita ta amsa da hakan."
Hajiya ta fadi. Nan dai Maman twins aka hau rantsuwar gulma ce kawai za ta kai ta. Haka suka yi ta tattaunawarsu abin gwanin sha'awa. Aisha ciki ya soma nauyi ba kasafai ta ke fitowa ba.
***
WASHEGARI...
"Ki soma shirya kayanki. Tafiya ta zo."
Hajiya Zeenatu ta dubi mijinnata gabanta ya fadi.
"London ko ina?"
Ba tare da ya dubeta ba ya ce.
"Adamawa kafin London. Ai na faɗamaki zamu je yan uwana su ganki ko?"
Ta dan yi shiru tana tuna wayar da suka yi jiya da daddare da Kawu Modibbo. Gargadi ya yi mata a kan zuwa Adamawa don a cewarsa ya zo garin, bai kuma ga wata alama da ke nuni da cewar ta samu karɓuwa ba, asalima labarin da ake shi ne, asiri ta yi ta rabashi da mahaifarsa.
"Kin yi shiru."
Hussein ya furta gami da ɗan riƙo yatsun hannunta yana murmushin yaudara. Ta bishi da na yaƙe.
"Hum, kana ganin ba ni da matsala da su? Za su karɓe ni da hannu bibbiyu?"
Hussein ya ci gaba da bin ta da kallo, abinda ya ke zargi ya kara tabbata. Jiya ya ji tana waya kuma tsaf ya ji me tace. Sai dai bai gama fahintar waye ke tare da ita a danginsa ba, ko ma waye dai ya lura sun jima su na tare. Zai bi ta sannu har wayarta ta fado hannunsa ya dauki lamba.
"Kamar kowane dangi, akwai masu murna da ci gaban mutum da ma wadanda ba su yin farin ciki. Ba zan rantse maki cewa duka dangina su na sonki ba Zeenat, musamman abinda ya faru tsakaninmu wasu su na daukar alhakin ki cewa ke ce silar komai. Amma bangaren yan uwana kuma shaƙiƙaina, ba ki da wata matsala. Don haka ki kwantar da hankalinki. Ban taɓa fadamaki ba saboda bana son sanyaki cikin wani hali. Amma yanzu ya zama dolena na faɗa don kar ki ga wani abu a wajen wasu ki ji ba dadi. Ba zaman kowa kike ba face ni."
Wani dadi ya lulluɓeta, ta ji a duniyar nan ta kara son Mijinnata. Ba ta sadda ta rungumeshi, ya runtse ido yana ji kamar wuta ta ɗosana a fatar jikinsa.
"I love you."
Ta furta a hankali. Ramlat ce ta fado a ransa kafin ya ce.
"I love you too."
Da wannan ya shawo kanta ta mike har da batun za ta shiga kasuwa ta soma siyan tsaraba. Ya fiddo kudi zai karamata ta girgiza kai da binsa da hararar wasa.
"Ah haba, yan uwanmu ne fa. Rike abinka, da kudina zan musu tsaraba."
Ya yi murmushi kawai. Yana binta da kallo, ya lura kwana biyunnan kurajen nata da sauki sun fara mutuwa, ta dai ce na gargajiya ta soma karɓa ta gaji da zirga-zirgar asibiti. Shi dai ba abinda ya shafeshi. Kusantarta ne tuni ya bari.
***
*RANA BA TA ƘARYA!*
[3/17, 9:18 AM] +234 703 629 0938: I just published "BABI NA HAMSIN DA TAKWAS" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1019046229?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=4ocpUEJVa%2B0bXSp4wxbK3lhNgthMCA7nB5QC2dclyyGJkYlECeIGKhiQUzgNGFlkVbskOsJU12vwNQbJIqJ2Pbn6%2F7TbXN1B%2BYmSMvxcC1P2DtDikL9OR4lEi83T5hqO
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
58)
Ana gobe ɗaurin aure tun da safe, suka bi jirgi zuwa Yola. Awa biyu da mintoci ta kaisu. Kamar yanda Hussein ya shirya, Kausar da AlHassan ne masu zuwa tarba. Kausar tun da ta ga Hajiya Zeenatu ranta ke zafi dakyar ta iya tankwara zuciyarta.
'Allah Ya isa.' Ta fadi a kasan ranta, Hajiya Zeenatu kuwa wani dadi ta ji ganin irin tarbar da ta samu a wurin Kausar duk da shekarun da ta ba ta. Suka dunguma a motar AlHassan zuwa gida. Bai yi gangancin sauketa a gidan Dada ba don ya tabbata Dada za ta iya kasa hakuri don ba ta iya ɓoye abinda ke ranta ba wasu lokutan sai dai ya san akwai ta da hakuri.
"Anan za ki zauna sai zuwa gobe idan an huta sai a leka dangi. Hakan ma ina ce ya yi miki?"
Hajiya Zeenatu dake karewa dakin da aka ba su kallo ta juyo tana dubansa fuskarta cike da damuwa.
"Yanzu dagasken a yau za ka juya? Gaskiya idan hakane zan jira a gidannan zuwa sadda za ka shigo garin sai mu leka dangin tare. Wallahi haka kawai na ke jin fargaba."
'Me akai da maza Zeenatu?' Ya furta a ƙasan zuciyarsa a fili kuwa murmushi ya yi kamar gaske ya shafi gefen fuskarta.
"Shikenan, yanda ki ka ce hakan za'a yi. Nima kin riga da kinsan dalilin komawar, ban larasa handling komai a wurin aikinmu ba ne, gobe juma'a in sha Allah da zarar na kammala, Asabar da safe zan taho."
Ta gyada kai.
"Babu wata damuwa. Allah Ya kaimu."
"Amin. Amma toh ko bikin ba za ki leƙa ba? Na fadamaki Cousin Sister ce a wurina."
Ta tuno da hakan don Kawu Modibbo ya fadamata zancen bikin don shi ne silar zuwansa garin shima. Sai dai ya gargadeta da shiga dangin gudun samun matsala don haka ta girgiza kai. Shima Hussein kawai fada ya yi don ya gwadata, amma tuni ya ji tana batun ba bikin da za ta leka da wanda suka yi waya kwanaki.
"Ka yi hakuri dai, ka ga ba'a san ni ba. Zan jira har ka dawo ka gabatar da ni a wurinsu."
Ya jinjina kai.
"Ba damuwa."
Daga haka ya rage kayan jikinsa ya shiga bandaki, can ya fito, wanka ya yi. Ya sauya kaya ya feshe jikinsa da turare. Hajiya Zeenatu ta ƙuramasa idanu, kananun kaya ya sanya. Rigar da ya sanya milk mai gajeran hannu sai blue jeans. Tsayawa suffanta kyawun da ya yi mata ta sani ɓata baki ne, mijinta kara kyau ya ke koyaushe da kuma ƙuruciya musamman gashinsa baƙi siɗik da ya kwanta a sumar kansa irin na Bafulatanin Yola wanda ke kara fiddo da zahirin waye Hussein. Ta shagala a kallonsa da jin wani irin tashin hankali da kishin zuwan da za su dinga yi Yolan yanzu, tana da tabbacin idan matan Kano ba su yi nasarar raba ta da shi ba, to wadannan kyawawan matan na fulanin Yola za su iya rinjayar zuciyarsa. Hakan tunaninta ke ba ta. Har ya kammala ya ɗaura agogo ta shagala a tunani.
"Muje mu ci abinci, su na jiranmu." Ya fadi ba tare da ya kalleta ba, jin shirun sai ya ɗaga kai yana dubanta. Ta shagala a tunani, sai da ya ɗan yi tafi kusa da ita sannan ta yi firgigit.
"Um, am..me ka ce?"
"Tunanin me kike? Nace mu je mu ci abinci daga can zan biya wurin Dada sai na wuce Airport."
Ta yamutse fuska.
"Sai zuwa anjima zan ci, yanzu bacci nake ji."
Ya ɗan ɗaga kafaɗa.
"Ok. Bari naje, idan kin yi nisa a baccin ba sai na tasheki ba. Zan wuce."
"Allah Ya kiyaye hanya."
Ya fice yana mai amsawa da wani irin nishadi a ƙasan ransa.
A falon ya yada zango, yana cin abinci su na hira da AlHassan da Kausar duk akan tsarin bikin.
"Yanzu kenan ita kadai za ta zauna a gidan? Yaushe Amaryar za ta zo nan? Don naji ana cewa tare duka za su shiga dakunansu."
Kausar ke neman sani.
"Asabar za su zo. Ke dama ai yanzu ba zancen zuwanki Kano saboda matarnan. Su Hafsat dai da saura sai su je."
AlHassan ke maganar. Kausar ta jinjina kai.
"Allah Ya kaimu."
Shi dai Hussein loma kawai ya ke, yana kammalawa ya mike ya gyara bakinsa. Koda ya shiga munshari Hajiya Zeenatu kawai ke yi. Ya ja mata kofar bayan ya dauki abinda zai dauka yana tsakin takaicin aurenta. Tare da AlHassan suka shiga gidan Dada. Kullum ta gansu sai ta ji kamar an yayyafawa zuciyarta ruwan sanyi. Tana tare da su Baba Yakura yan Maiduguri da ma sauran yan uwan mahaiyarsu. Aka gaggaisa kafin ya yi musu sallama da zummar wucewa Kano.
"Allah Ya kaika lafiya Ango. Mu dinma ai yanzu zamu wuce. Kai dai tunda a jirgi ne za ka riga mu sauka."
Ya yi murmushi jin abinda Gwaggo Lubabatu ƴar abokiyar zaman kakarsu ta bangaren Uba da ke Mubi ke fadi, ya yi addu'a akan Allah Ya kawo su lafiya sannan aka kara yin sallama ya tafi.
***
CIKAR BURI..
Gidan cike yake da yan uwa da aboka arziki, tun safe ake shige da fice na dora sanwa. Dangi an cika a madafi ana aiki ana kwasar hira. Fuskar kowa ka gani cike da farin ciki musamman Hajiya da har kwalla sai da ta yi don kuwa sun debemata kewar Abba. Cikar da suka yi ya motsa zuƙatan mutan gidan da tunanin Abba, bikin ganinsa suke yi tamkar na wata budurwa ba bazawara ba. Ƴan Daura da yawansu sun zo hakanan kafatanin mutan gidan Hajja su na nan. A bangaren Baba Dakta ma, hatta Kanwarsa Hajiya Nabila da yan uwan Umman Amrah duk sun hallara. Wannan shi ne kadai karar da zaa yiwa Hajiya mace mai son mutane da kuma zumunci. Don sun shaida, Hajiya ko ba ta je sabgarka ba, to hannunta zai je. Ba ta gajiya da kyautatawa hakanan marigayin Mijinnata. A ganinsu wannan ce karar da zaa yi.
Kowa ya bude baki ya ga cikar gidan cewa ake, har ma da auren Ramlatun, shima ya yi albarka kwarai. Duk wannan shagalin da ake, Ramlat na can tare da Amrah da kuma Rafeeah a gidan kwalliya. Dama tun ana gobe daurin aure suka je aka tsaramata lalle a ƙafa da hannu na gani na fada. Hakanan duk a ranar aka yi mata kitso sirara.
Maryam Cutie ce gwanar kwalliyar, tsayawa faɗin irin kyawun da ta yi ba'a cewa komai. Kasancewar Maryam kawar Rafee'ah kuma ba ta da matsala ne yasa ba su wani jima su na roƙo ba ta amince za ta bisu har Adamawa don yiwa Amarya kwalliya ta musamman. Ba ta samu matsalar hakan daga mijinta sosai ba don shi mutum ne mai fahimta hakanan sanin da ya yiwa Rafee'ah da mijinta ne yasa bai yi ja in ja ba.
"TubarakAllah Masha Allah."
Amrah ta fadi tana kallon Ramlat baki ya ƙi rufuwa tsabar kyawun da ta yi mata. Ko aurenta na farko ba ta tsaya ta nutsu an mata kwalliya kamar hakan ba. Murmushi Ramlat ta yi jin yanda su ke koɗa ta. Farin leshin wurin Muniru ta sanya an mata dinkin gown. Maryam Cutie ta yi mata dauri na gani na fada a karshe ta yafamata gyalen kamar yanda ya dace .
"Ke Ramlatu, kinga yanda kika sauya?"
Rafee'ah da ke tsaye gaban madubi tana dauri ke fadi, ita da Amrah suma duka Maryam ta fito da fuskokinsu ba laifi.
"Ya isa kar ku cinyeta."
Fadin Maryam tana dariya. Hotuna ta shiga yi mata tana mai yin alfahari da baiwar iya kwalliya da Allah Ya ba ta. Ta tabbata fuskar Ramlat ko kasar waje za ta a haka, to fa za ta ciri tuta.
Sai wuraren sha biyu suka kama hanya zuwa gidan, ita dai Ramlat jikinta duk ya yi sanyi, fatanta Allah Yasa wannan ya zama aure na karshe a gareta wanda mutuwa ce kawai za ta raba. Allah kuma Ya ba su zaman lafiya.
Koda suka shiga gidan nan ma haka yan uwa suka yi caa ana ta koɗa kyawun da Amarya ta yi, kunya ta kamata ganin Hafsat diyar Dada, sai a sannan ta kula da zuwan yan Adamawan. Hafsat ta ja hannunta zuwa can falon Abba na baya da aka kai su, suka karasa ta durkusa ta kwashi gaisuwa.
"TubarakAllah, Amaryar Hussein kyakkyawa da ita." Matar ta fadi da hausarta da ba ta fita sosai. Ita dai Ramlat kanta a kasa tana murmushin jin kunya. Sai da Hafsat ta sanya ta zauna ta dinga daukarsu hotuna kafin a karshe ta yi musu sallama ta fito tare da Hafsat. Nan fa Hafsat ta shiga cikinsu aka dinga raha kamar dama can an shaku sosai. Su Nusaiba duk sun zo, daga mai goyo sai mai ciki.
Suna zaune a daki sai ga Salma da Bilkisu, dama Hunainah ita kam tun safe tana gidan, ko sadda suka shigi tana kwance ta yi rashe-rashe a saman gadon suna kwasar hira da kanwar miji kuma aminiyarta A'isha.
"Amarya Ramlat. "
Bilkisu ta fadi tana yamutse fuska musamman jin bakin cikin ganin Hunainah ta riga ta zuwa. A ranta ta ce 'Cusa kai.'
Ramlat ta gaidata da murmushi saman fuskarta. Ta mance rabon da ta sanya Bilkisun a idanu, gaba daya ta kara wani fari fat sabida shafe-shafe ga wani uban ƙiba da ta ke narkawa, ita kuwa Salma har tambarin baƙi-baƙi ya yi mata a fuska. Ramlat ta ja hannun Yasmeen suna gaisawa, yarinyar yanzu ta bar sakewa sosai kamar a baya don dif haka uwar ta raba ta da gidan. Yanzun ma da biyu ne zuwannata, ba ta san mijin Ramlatun ba. Ko a hanya suna ta gulmar abin suna dariya don har Salma na fadin Allah Yasa wani Alhajin ne mai mata uku da katon tumbi. A jikinsu ba su taɓa kawo wai matashi mai jini a jika zai aureta ba musamman idan an san wacece ita.
"Murja da Fareeda ma suna tafe, Hilal ya fadamusu tunda ke ba ki iya gayyata ba."
Ramlat ta dubi Amrah, Amrah ta kanne mata ido don ta san gulma ce.
"Ayya, ban yi zaton za su zo bane. Allah Ya kawosu lafiya kuwa. Ina murna."
Bilkisu ta taɓe baki ita kuwa Salma murmushi ta yi ta dora kafa daya kan daya tana girgizawa. Sai dai