Showing 195001 words to 198000 words out of 226732 words
blue da fari, ta yafa farin mayafi sannan ta fita wurin yaranta. Ta dauka za ta gansu cikin damuwar tafiyarta sai dai da sauki musamman ga Ummi da Ansar wadanda suka shaku sosai da Hajiya. Affan ne ma ya dan yi wuri-wuri da idanu da ya tabbatar dagasken tafiyar Maminsa za ta yi. Itama dannewa kawai ta ke amma tsananin kewarsu ta ke ji tun kan a je ko'ina. Kiran da Hajiya ta mata ne yasa ta lallaɓa Affan da ya kanainaye a jikinta ta fita. Can ƙuryar daki ta isketa. Ba ita kadai ba ce har da Umman Amrah da ta shigo tun sassafe da kuma su Baba Hajara da sauransu. Nasiha sosai suka yi mata, Hajiya a karshe ta tofa da cewar sun gama magana. Ta yiwa Ramlat addu'a kawai. Ita kuwa banda afkin kuka ba abinda ta ke fitarwa. Iyayenta masu sonta da komai, a baya ta bijirewa saboda son zuciyarta. Nan ta bude baki ta na mai kara neman gafararsu akan abinda ta aikata a baya. Murmushi suka yi.
"Banda abin Ramlatu, ai kowa ya fahimci kaddara. Ba komai kedai komai ya wuce sai da kawai yanzu ki maida hankali wurin biyayya ga mijinki."
Wata Gwaggonta daga Daura ta fadi.
***
ADAMAWA...
Hajiya Zeenatu hakanan ta ji faduwar gaba, shigar da Hussein ya yi da irin fara'arsa sai ta soma wani tunani daban. Ganinsa ta ke yi kamar wani Ango. Ya kammala ɗora agogon hannunsa bayan ya idar da sallah, murmushi ya ke tun sadda suka yi magana da Hafsat ta tabbatarmasa da isowarsu garin su ma. Dama habyar da ya biyo daban da tasu.
"Hussein."
Jin ta kira sunansa kai tsaye yasa shi dubanta.
"Duk wannan fara'ar ta mecece? Wani kyau ka yi kamar wani Ango. Gabana faduwa ya ke yi. Yaushe za mu je ka kaini mu gaisa da danginka?"
Ya yi wani banzan murmushi ya rike kafadunta.
"Kar ki damu, kin ga yau daurin auren yar uwata ake yi, ke kuma na sanki ba kya son cunkuso da wani hayaniya, ki yi hakuri gobe zamu shiga ku gaisa da kowa. Kallon banza aka yi maki Hussein ba zai rabu da mai shi ba. Sannan kina batun wai Ango, na dauka kodayaushe ni Ango nake a wurinki? Toh ki kwantar da hankalinki, babu macen da ta ishe ni kallo har naji ina sonta. Ke kinsan yanda nake."
Yanayin da ya furta kalmar karshen kawai sai ta kara shan jinin jikinta, ga wayarta ta rasa ya aka yi ta fada ruwa balle ta tambayi Kawu Modibbo ko akwai wani labari, yanzun dai ta ƙi tashi Hussein kuma ya karɓe ya ce zai siyomata wata da kansa. Abinda ba ta sani ba, da gayya ya tankwaɓar da ƙaton jug na ruwan dake saman centre table, burinsa dama ta rasa hanyar jin kowane labari.
Bai bar gidan ba sai da ya tabbatar ya kwantar mata da hankali, har cewa ya yi ta dauko mayafi su fita tunda hankalinta bai kwanta ba, soyayyar Hussein da ganin tsantsar gaskiyarsa a yanzu ta rufemata ido ta yanda ba ta tuna komai da kowa, hakan yasa ta kasa hasaso wani abin musamman ma da ta ga ta fito falon Kausar na mishi batun bikin da ake yi. Hankalinta ya kara kwanciya bayan fitar Hussein din da Kausar ta shiga budomata hotunan auren da ake yi tana kallo tana ƙara jin sanyi a ranta. Ta na kuma kara tabbatarwa zuri'arsu Hussein kyawawa ne tsantsa.
***
Bangaren Marigayi Baba Naziru wanda ya sha gyara da fenti daga AlHassan, nan aka kai Ramlat kafin lokacin da Hussein zai yi gininsa. A sannan yan uwanta suka hau aikin jere da ma sauran abinda duk ya kamata. A ranar daga su sai su, an kawomusu abinci da abubuwan sha.
Da daddare suna zaune ana hira, wayarta ta yi kara, Mr.Wuff. Murmushi ta yi ta dan mike ta bar wurin zuwa can wani dakin da ta tabbatar babu kowa ciki.
"Assalamu alaikum." Ta furta a hankali.
"Waalaikumussalam. Fatan an iso lafiya?"
Ta dan lumshe ido kafin ta bude tana bin dakin da kallo, shima gado ne aka shimfida a dakin, don wannan karon gatan da ta samu har gado biyu aka yi mata.
"Alhamdulillah."
Shiru kamar ba wanda zai tanka can kuma ya ce.
"Kin shiryawa abinda zai biyo bayan aurenmu?"
Ta ji maganar banbarakwai.
"Kamar ya?"
Murmushi ya yi mai sauti.
"Za ki haɗu da Uwargidana mana."
Ranta ya sosu matuka, kishi mai zafi na Zeenatu ya mamaye koina na zuciyarta.
"Ina ruwana da ita? Zamana da nata ba iri guda ba ne. Ko ba komai ita ai auren soyayya aka yi kamar a cinye juna."
"Sai aka fadamaki kema ba zan iya cinyekin ba? Wai meyasa kike son koyaushe ki nunan babu soyayya tsakaninmu? Dama akwai soyayyar da ta girmi aure?"
Ta kasa ba shi amsa don har lokacin kiran Zeenatu da uwargidansa da ya yi yana mata zafi, ta rasa rashin zuciya irinta Hussein da ya iya rayuwa da matar da ta rushe dukkan wani tubalin ginin rayuwarsa saboda son zuciyarta.
"Shiru ki ka yi?" Ya tambaya.
Ta dan turo baki kamar yana ganinta.
"Bani da abin cewa."
"Saboda kin san ba ki da gaskiya ne kawai. Na dai fadamaki, ki shiryawa hakan. Tsoro ba naki ba ne, dama na riga da nasan ke jaruma ce. Amma ban sani ba ko har a fannin kishiya."
"Wanda aka damu da shi ne ake kishinsa, tunda ba na kishinka me zai dameni da matarka? Don haka kar ka samu damuwa, ita dai za ka yiwa wannan kashedin. Zan kwanta sai da safe."
Ta katse kiran ranta a tsananin ɓace. Me Hussein ya gani a tattare da Zeenatu har yake mata son da ba zai iya rabuwa da ita ba wai? Ita ta rasa dalilin da yasa duk laifin da ta yi masa ba ya ganin ko ɗaya. Wato har shaidamata yake ta shiryawa haɗuwarta da ita saboda ya san ba zai yi kyau ba.
Ramlat ta yi kwafa, ta mike da zummar barin dakin sai ga saƙonsa ya shigo.
"Kashe waya ba shi zai sauya zancena ba, ba kuma zai hana na faɗi ba. Ki shiryawa haɗuwarki da Uwargidana. Anan za ki gane so da kuma ƙiyayya."
Ta harari wayar tana jin kamar shi din ta harara, sai kuma takaici yasa idanunta cikowa da kwalla ta yi azamar daukesu ba ta bari sun zuba ba. Daga nan ta ja tsaki ta fice daga ɗakin.
***
Washegari da safe suka gudanar da shagali irin na al'adarsu da suke kira Fansa, inda dangin Ango ke kawo kayan abin ci da sha ga dangin Amarya ba tare da sun ga Amarya ba.
Da yammaci aka hau shirye-shiryen buɗar kai. Maryam Sambo (Cutie) ta fente fuskar Amarya da kwalliya wanda ya fi na ranar daurin aure. Maganar kyau ma na Ramlat ba sai an tsaya ana ɓata baki wurin faɗa ba. Ta yi kyau iyakar kyau, ga ta nan dai ba farar mace ba, amma Allah Ya mata baiwarSa a halittarta. Wannan karon ma Leshi ne golden cikin kayan da Hussein ya bata ta sanya an mata dinkin gown. Bilkisu dai gaba daya sai ta kara raina kanta, bakin ciki kuwa kamar ya kasheta. Ba ta taba zaton family din da Ramlat za ta shiga su na da wannan kuɗin ba. Hatta da muhallin Ramlatun, ya ci a kalla a ƙara kalla duk kuwa da cewar tsohon gini ne sai dai ya yi tsari sosai.
Gaba daya suka fita katon rumfar da aka tanada a babban filin tsakar gidan gadon na Marigayi Alhaji Gidado. An lulluɓe jikinta gaba daya da turmin zanin atamfa yanda ko fuskarta ba'a gani.
Nan kuma dangin su Hussein aka shiga fansar fuskar Amarya, Dada nan take da ba da Dubu ɗari na fansa, haka nan ma yan uwansu na Mubi da Maiduguri kowa ya shiga kawo nasa. Amrah ce gwanar faɗin nawa Amarya ta samu. Ita dai Ramlat na ƙunshe tana murmushi a ƙasan zanin don al'adar tasu ta burgeta matuka sai dai da zarar ta tuno batun haɗuwarta da Hajiya Zeenatu da Hussein ya yi sai jikinta ya yi sanyi sai dai kuma ta tabbatar addu'a ne maganin komai.
Hafsat a matsayinta na ƙanwar Ango ita ta mike don zaɓawa Amarya suna, a karshe ta radamata suna Amal. Sunan da kafatanin dangin za su dinga kiranta da shi kenan. Bayan an kammala aka kwashesu zuwa gida.
Da daddare ana zaune gaba daya ana hirar bankwana.
"Amal."
Suka yi dariya gaba daya jin sunan da Amrah ke kiran Ramlatun. Ita kam tasan kafin ta saba da sunan za'a jima.
Anan wata ma ke tambayar Kishiyar Ramlat.
"An cemin tana nan amma ban ganta ba."
"Anya ta zo Adamawa? Ina ji fa a Kano za ta zauna ita." Cewar Rafee'ah.
"Ta huta. Zama da dangin miji gari daya ai sai tsautsayi."
Babu wanda bai kalli Bilkisu ba, ita kuwa sai karkade kafa ta ke don dama da biyu ta yi maganar tana jira a tanka. Umman Amrah ce ta hana kowa magana karshe ma aka maida hankali ga hirar bikin yanda ya yi kyau.
Koda za ta kwanta tana ganin kiran Hussein ta ƙi ɗagawa don ba ƙaramin haushi ya ba ta ba. Karshe ma ta katse wayar.
***
A bangaren Hussein sam bai samu ya fita ko'ina da Hajiya Zeenatu ba sai a washegarin bikin bayan dangin Ramlatu sun kama hanyar Kano, ya zo tare da su AlHassan, Kausar da ɗiyarsa. Har yanzu akwai yan Maiduguri da Mubi wadanda ba su kai ga tafiya ba sakamakon dakatar da su daga yin hakan a Hussein ya yi, kowannensu na da labarin Hajiya Zeenatu, sai dai ba su ji cikakken ba sai yanzun da suke burin ji. Falon a cike yake, tun da ta ji suna juya harshe, wasu fulatanci wasu kuma yaren barbanci. Bayan an gaisa Hussein ya gabatar musu da ita sai kuma kai tsaye suka nufi ɗaya falon na Dada, babu cunkoson mutane kamar na farkon. Dada ta ƙuramata idanu, kusan koda ta girmemata ba da shekaru masu dumbin yawa ba. Suka gaisa da mutanen dakin, ita dai Hajiya Zeenatu an gaisa amma ba ta gamsu da kallon da kowanne ke bibiyarta da shi ba. Anti Amarya matar Kawu Modibbo itama gidan ta sauka, wannan karon dai Modibbo bai hanata ba, da biyu ya bar ta ta je don ya gama shan jinin jikinsa, yakan kirata akai-akai ya ji ko ana wani abin. Ita har mamakinsa ma ta dinga ji, ta kuma soma wani tunanin.
'Yanzu wannan ce azzalumar matar da ta raba ni da ɗana?'
Dada ta faɗi a ƙasan ranta, nan da nan tsanar Hajiya Zeenatu ya kara cika zuciyarta.
"Amm..Dada. Hafsat ba ta nan ne?"
Dada ta dubi Hussein, alama ya yi mata da ido akan kar ta nuna wani abu. Ta yi dan murmushin yaƙe.
"Ta shiga wurin Amarya saboda kowa ya watse, kar a bar ta ta yi zaman kaɗaici."
Hajiya Zeenatu dai ba ta ce uffan ba amma a ranta tana ta tunanin dama Dadar ba ita kadai ce wurin mijinta ba?
"Zeenatu."
Muryar wata mata ta ji, daidai sadda ta juya ta dubeta. Zumbur ta mike ido waje ta ke dubanta.
"Hajiya Binta?"
Hajiya Binta mahaifiya ga Rasheed ya karaso tana murmushi. Hajiya Zeenatu ta dan saki jiki ta karasa suka rungume juna amma gaba ɗaya jikinta ya yi wata irin mutuwa. Ta dago ta dubeta.
"Yaushe kika zo ƙasarnan? Me kike yi a nan?"
Yanda ta yi tambayar a mamakince yasa Hajiya Binta murmushi tana kara hadiye mamakinta, don koda ta ji labarin duk abinda ke faruwa har kuka ta yi don tausayawa Hussein. Ita ta ba Hussein dukkan shawara akan ya ɓoye dukkan batun aurensa da Ramlatu gareta don ta san komai na daga shaiɗancin Hajiya Zeenatu.
"Ina nan tun sadda Allah Ya bayyanamana Husseini. Ko kin manta amintarsu da Rasheed?"
Ta gyada kai tana yaƙe.
"Ban mance ba. Rasheed din yana nan shima?"
"Eh yana nan, ya dan fita ne ma, yanzu za ki gan shi ya dawo."
"Ok." Shi ne kawai abinda Hajiya Zeenatu ta iya faɗa kenan jikin a matuƙar sanyaye.
"Dama kun san juna?"
Dada ta jefo tambayar ga Hajiya Zeenatu.
"Eh, Ƙawata ce."
Ta amsa a dake, saura kaɗan dariya ta suɓucewa Kausar, AlHassan ya sa ƙafa ya ɗan taka ta don ta gimtse.
"Bayan an zauna sai Hussein ya fidda waya. Hafsat ya kira ya ce ta taho sashin Dada tare da Amal. Hakan da ya fadi yasa ta fahimtar komai, don haka da toh kawai ta amsa.
***
Ramlat da tun soma wayar Hafsat ta kafeta da ido.
"Hamma Hussein ya ce mu je."
Ta gyada kai, ta yi wankanta ta ci ado da wata shadda da aka yi mata dinkin doguwar riga ya sha aiki. Ta cakare ɗaurin ɗankwali don Ramlat ba baya ba. Ta ɗora mayafi a saman kayan ta zura takalmi suka fita tare. Hakanan ta ji gabanta na bugu da sauri-sauri, ta kara kallon Hafsat wacce ke wani zumudin suna tafiya sai janta da hira take amma ba ta fadi dalilin wannan rawar ƙafar ba.
A ƙofar falon farko suka yi sallama, kunya sosai ya kama Ramlat don ba ta zaci ganin sauran jama'a ba. Ta durkusa a kunyace ta gaishesu. Cike da fara'a aka amsa, nan kuma wata tsohuwa ta ɗauki guɗa da biyu. Jin haka daga cikin dakin, sai ga Kausar ta leƙo, Hafsat na ganinta ta tsallaka.
"Adda, dagaske ta zo?"
Hafsat ta tambaya da raɗa-raɗa, Kausar ta yi dariya ta nuna ƙofar falon.
"Tana ciki."
Hafsat ta harari ƙofar.
"Makira, yau ƙarshenta ai ya zo."
Suka yu dariya sabida duk da harshen fillanci suke maganar, Ramlat ta karaso.
"Muje ko?"
Sai kuma ganin Kausar suka shiga gaisawa, wasu mutan falon duk sun mike sun biyo baya don ba su kaunar abinda za'a yi ya kasance babu su.
Gaba ɗaya ana zazzaune har Hajiya Zeenatu da ta soma sakewa ganin Hajiya Binta har su na hira. Tana so ta tambayeta yanda su Dada suka ɗauketa amma babu dama tunda ba su keɓe ba. Ba su kadai ne a falon ba. Sallamar da aka yi duk ta dawo da hankulansu bakin ƙofar musamman ganin yanda wuri ya ɗauki guɗa.
Hafsat ce ta soma shigowa sai Kausar, bayansu kuwa Ramlatu.
Wani irin miƙewa tsaye Hajiya Zeenatu ta yi a matukar gigice. Babu chanjawar da za ta yi ta kasa ganeta tsabar tsantsar tsanar da ta yi mata. Ido waje ta ke duban Ramlatu, daga kan kafafunta har zuwa dukkan gaɓoɓinta babu inda ba ya rawa. Ba ta ƙara razana ba sai da ta ji muryar wata na fadin.
"Ƙaraso ciki ki zauna, Amaryar Husseini. Lale lale da kyakkyawar halittarnan."
Wani ihu Hajiya Zeenatu ta kurma kafin ta yi tsalle da nufin isa ga Ramlatu.[3/17, 9:18 AM] +234 703 629 0938: I just published "BABI NA SITTIN DA ƊAYA" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1023106863?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=bdvKCKOC3LLp5bowO1ooPkj4NyQWwtoNnAonSsHZp24WzPeGm2lKyYgVyvV%2Bh9gt6e1Oc%2BZqkJMVkFlQ2xAQQ3P60IL2qqoNgqvumrfhTuosHta7gVySLHczdgg1%2Fq97
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
61)
"A rayuwata, kar ki yi mamakin cewa ban taɓa soyayya ba. Ban yi ba tun ma kafin zuwan Zeenat, balle a bayanta."
Ta dubeshi, dama idanunsa na kanta, sai ya yi murmushi ya riƙo hannunta ya damƙe cikin nasa yana murzawa a hankali kafin ya ɗora.
"Sadda Allah Ya soma haɗa ni da ke, mun haɗu ne lokacin bana cikin nutsuwata sakamakon ɓacin ran wata hatsaniya da muka yi da Zeenat, ban ji komai a kanki ba sai sadda na ƙara cin karo da ke a ma'aikatar Revenue da muka je tax payment. A hankali a hankali haɗuwarmu kan zo akai - akai, tun bana daukarki da wani muhimmanci har ban san yanda aka yi na soma kula da lamuranki ba. Na soma jinki kamar wata ƴar uwata. Ba ki ƙara burgeni ba sai haɗuwarmu a A&Z da kika nunawa duniya da ma Zeenat, akwai soyayya tsakaninmu. Duk a matan da suke bibiyata da sunan so, babu wacce ta taɓa rainawa Zeenat hankali kamar ke."
Suka yi murmushin tuna ranar kafin ya ɗora.
"Tun daga wannan ranar na ji ina son kusancinnamu ya fi haka, na dinga hasashen da ace gaskiya ne muna soyayyar ya kenan? Wane yunƙuri Zeenat za ta yi? Duk fa da cewar a sannan ina ɗan shakkarta, hakan bai hana ni tunaninki ba. Dangantakarku da Hisham ya ƙara ƙarfin shaƙuwarmu. Da tafiya ta yi tafiya, na fahimci ba wai kawai burgeni kike ba, kaunarki nake dagaske. Akwai ranar da na ji Zeenat na waya da Chairman tana kyakyata dariyar mugunta. Maganarki suke yi akan ya ci gaba da yin duk yanda zai yi ya aureki, za ta ba shi kyauta ta musamman idan hakan ta kasance. A lokacin har jaddada masa ta dinga yi kan ya yi amfani da masu gidan rana, sai kuma ga Hisham ya zo min da batun aurenki da Chairman. Bayan tsananin kishin da naji yana neman zautar da ni, sai na dinga ayyanawa a zuciyata ashe dagaske ƙarfin dukiya na saurin rinjayar zuƙata. Ban yi zaton kina daga cikin kwaɗayayyun mata ba, sai gashinan lokaci guda kin ban mamaki. Daga lokacin kuma tunanina ya sauya a kanki."
Ramlat jin haka ta bude baki za ta yi magana ya yi saurin dakatar da ita ta hanyar ɗora yatsansa ba bakin. Murya a tausashe ya ce.
"Yi shiru please, labari ne fa nake ba ki, ki bari na kai ƙarshe."
Ta gyaɗa kai sai dai tuni idanunta sun cicciko, ta kasa kunne tana sauraronsa.
"Baki ba zai iya misalta maki ɗumbin damuwar da zancen aurenki da mutuminnan ya jefa ni ba. Na rasa walwalata, ke kaɗai nake ganin za ki mayemin gurbin ƴan uwana da ban san su ba, ina da su ko bani da su, ba zan tuna ba. Sai gashinan lokaci guda wani can zai rushemin hakan. A sannan har kwanciya nayi a asibiti, aka tabbatar da cewa damuwa ce. Na rage tunani. Bayan na farfaɗo na kasa samun sukuni da walwala, ban yi ƙasa a gwuiwa ba sai da na nemi gidan Baba Dakta, naje a matsayin manemin aurenki."
Da mamaki ta tsuramasa idanu baki a sake, hawayen da ta ke dannewa tun ɗazun suka zubo. Ya yi murmushi gami da sa yatsa ya sharemata.
"Kar ki yi mamakin ta yanda aka yi na san Baba Dakta. A hirarrakin da mukan yi da Hisham, yakan sanyamin shi a ciki don ya cemin ma a wurinsa ya soma neman auren Aisha kafin ya sada shi da Kawunnanku. Yanda na fahimta, banda ma