Showing 78001 words to 81000 words out of 226732 words

Chapter 27 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12470

ya ja zanin rumfar ya rufemishi fuska.

Ya jima a tsaye yana tunanin t hanyar da zai sanarwa iyalin rasuwar Abban. A karshe dai ya daure ya fita ya fadamusu. Kowannensu ya saka salati.

Dif! Kukanta ya dauke sai kallo. Ta kalli wannan ta kalli wancan.

"Kuka ku ke yi? Abba ai bai mutu ba. Ku daina kuka."

Abinda ta fadi ne ya tabbatarwa Baba Dakta ba'a hayyacinta ta ke ba, ya karasa ya riko hannunta. Ta dubeshi tana murmushi har dimples dinta na lotsawa.

"Abbana bai mutu ba, bai mutu ba fa Baba Dakta. Muje na ganshi, zan fadamasa lafiyata kalau. Zan fadamasa bana dauke da ƙanjamau. Yanzu za ka ga ya tashi, baccin wasa yake."

Ta ja hannun Baba Dakta zuwa dakin Abban. Gaba daya suma suka shiga ciki banda Muniru da har lokacin bai dawo ba.

Mayafin ta yaye ta riko hannun Abba.

"Abba bacci ko? Ka tashi don Allah. Na warke, Baba Dakta ina result din?"

Ta juya a firgice ga Baba Dakta, sai kuma hankalinta ya kai saman tebur ta hango takardar maganin Abba wanda a zatonta shi ne na test din. Ta ɗago ta na nunawa Abban kamar mahaukaciya.

"Abb..Abba, ka ga, negative. Banda komai wallahi. Aliyu ma na fadamaka lafiyarsa kalau. Abba ka yi magana."

Hajiya ta ja hannunta suka fita bisa umarnin Baba Dakta, ya maida marufin ya rufewa Abban fuska.

***

Suna tafe zuwa mota tana sambatu, Hajiya na damƙe da hannunta.

"Hajiya bai mutu ba, wallahi Abbana bai mutu ba. Haba! Haka ake mutuwar?! Ai ba haka bane! Mutuwa ba haka take ba! Abba bai mana sallama ba! Um um Hajiya, Abba fa bai mutu ba. Wayyo Allahna!"

Hak rike kai da karfi kafin ta yi baya, Allah Ya taimaka Zulaihat na bayansu, ta riketa da karfi. Tuni ta suma. Ba shiri da taimakon wasu mata a wurin aka rirriƙeta zuwa ciki.

Dawowarsa kenan daga masallaci ya hango taron mata, har ya kauda idanunsa, hankalinsa ya kai ga Rafee'ah da ke kuka. Cikin sauri har yana tuntuɓe ya karasa.

"Ke lafiya?"

Ta dubi Muniru kafin ta faɗa jikinsa tana kuka. Ya ɗan tureta.

"Abba?" Abinda ya fadi kenan ya yi saurin nufar cikin asibitin. Hawaye kawai ya shiga fitarwa sadda ya ci karo da gawar Abban.

"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!" Ya fadi a fili.


***
Kafin ka ce me, mutuwar shahararren dan kasuwan Alhaji Khalid ya karade garin Kano. Mutum ne mai jama'a kuma mai girmama mutane. Yana da saukin kai da tausayi ga gaskiya da amana.

Mutum ne mai son zumunci kwarai. Shakka babu an ji mutuwarsa ba kadan ba.

Jama'a da dama sun halacci jana'izarsa, mutanen Daura an zo sosai.

Aliyu ya girgiza matuƙa da mutuwar surukinnasa. Abban da ya ke yiwa kallon maƙiyinsa a baya kafin ya fahimceshi da kuma irin kaunar da ya ke yiwa Ramlatu. Bai mance nasihar da ya sha yi mishi ba a duk sadda zasu hadu ko kuma ya je gida. Adalilin faɗa da Ramlatu. Shakka babu ya tausayawa iyalinsa musamman Ramlatu dake kwance gadon asibiti har aka yi jana'izarsa ba ta san ina kanta yake ba.

***
Hasken rana ne ya tasheta daga nannauyan suman da ta yi, ta yi cak tana nazarin dakin da take. Tabbas gadon asibiti ne, ta dubi hannunta, ruwa ne ake ƙaramata. A hankali ta motsa.

"Sannu kin tashi?" Ta tsinci muryar Indo a gefenta. A hankali kuma ta gyada kai. Indo ta fita da zummar kiran likita kamar yanda ya ba da umarni. Firgigit ta mike.

'Abba! Ina Abba?' Ta yi tambayar da babu mai amsamata, ta fisge ruwan da ake ƙaramata ba tare da jin nauyin cikinta ba ta nemi hanyar fita.

Karo suka ci da likita, duk yanda Dr Sunusi ya so ta tsaya hakan ya faskara, a dole ya kyaleta suka wuce gida da Indo. Kuka take yi sosai don tuni ta gano abinda ke faruwa, ta yarda kuma yanzun cewa Abban ba ya duniyar nan da take ciki.

"Ya bar min duniyar, ya tafi ya bar ni da abinda na zaɓa sama da su. Ya bar ni nayi yanda na so. Shikenan babu sauran mai sona..."

"Haba Ramlatu, ki yi hakuri, ki dauki dangana. Kar ki manta kina da Allah, don ya karɓi abinda ya ba ki aro sai ki ce don me?"

Ta girgiza kai kawai. Indo ta ci gaba da ba ta baki. A nan take fadamata anan Aliyu ya kwana, ya je don kawo abin kari ne daga gida. Ba ta ce komai ba har Indon ta kira lambar da Aliyu ya sanyamata ta fadamishi sun wuce gidan.

A falon ta iske mata maƙil, ta karasa ciki har wurin Hajiyarta ta zauna. Nan kuma aka shiga yi mata sannu da gaisuwa, kawai ta rungume Hajiyar ta shiga kuka mai tsuma zuciya. Wannan ya kara yiwa Hajiya fami, ta shiga sharar hawaye. Su Zulaihat kam ba'a magana dama, idanun sun yi ja.

"Ba'a bar ni na ga Abba ba."

Ta fadi cikin sheshsheka.

"Sai hakuri Ramlatu, haka Allah Ya tsara. Allah Ya ba ki lafiya."

Ta kasa amsawa Hajja, dakyar aka lallaba ta yi wanka ta sha ruwan shayi.

***
BAYAN KWANA ARBA'IN

Har sannan Ramlatu na gidansu, su Zulaihat ma dakyar suka koma nasu gidajen sai da Yayan Hajiya, Kawu Dauda ya yi musu fada ba shiri suka tattara a kwana ashirin suka tafi. Ita kuwa Ramlatu ta kasa lekawa ko waje ballantana ta fita.

Aliyu kusan kullum sai ya zo, har abin ya soma isar Hajiya. Ta kira Bana Dakta ta mishi maganar. Da kansa ya nemi Aliyu suka je yin gwaji bayan ya ba shi hakuri ya fadamasa dalili.

Koda sakamako ya fito ya yi mamaki ganin Aliyun shima lafiya kalau yake, ya kara jinjina lamarin Allah. Ya tabbatar ajali ne kawai ya riski Abban ta wannan hanyar.

Washegari Baba Dakta da kansa ya zo ya tisa Ramlatu a gaba suka wuce ya kai ta gidanta. Ranar ta yi kuka kamar ranta zai fita sakamakon famin da hakan ya yi mata game da mutuwar Abbanta. Murmushi da dariyar Abban sun kasa gushewa a zuciyarta. Kalamansa na nasiha gareta daki-daki su ke faɗomata a rai, wannan kadai ma yana kara sanyata zubda hawaye. Komai na duniyar ya fice a ranta.

***
Zamansu da Aliyu ya sauya, ta koma wata shiru-shiru. Aliyu na shaye-shaye ko ba ya yi, ya zama ba damuwarta ba. Ta daina shiga hayaniya, ta daina shiga lamarin kowa da komai. Ummi har sannan ba ta dawo ba, tana wurin Hajiya.

Tana lura da yanda Aliyun ya chanja, yakan wuni a gida idan ya so, wataran kuma ya fita kasuwa. Duk yanda ya so ta saki jiki ya kasa. Koyaushe cikin kuka.

"Dana sani ban aureka ba, da na sani na bi zaɓin Abbana."

Abinda takan yawaita fada kenan wanda take sosa zuciyar Aliyun da shi. Shi kansa yasan ya mata rashin kyautatawar da ya ci ace ta yi nadamar aurensa, sai dai ko mene ne ai shima ya zalunci wata a dalilinta.

***
BAYAN WATANNI BIYAR

Cikin Ramlatu ya cika watanni tara. Abin da ya bata mamaki tun a wata na takwas Aliyu ya haɗomata komai da ta bukata na haihuwa, abu ne da ba ta zata ba. Zuwa sannan ta ɗan saki zuciyarta, addu'a babu ranar da ba ta saka Abbanta ciki duk sallah. Kulawa sosai suke ba wa Hajiya daga ita har ƴan uwanta. Kowannensu gudun ɓacin ran Hajiyar yake yi. Ɓangaren Aliyu kuwa, ta ga sauyi sosai don ga dukkan alamu ya bar shaye-shaye. Koda ya na yi ba ta taɓa kamashi a gidanta ba. Ba ta dai gajiyawa da yi mishi nasiha da tsoratar da shi game da rayuwa da mutuwa. Tana dai godiya ga Allah yanda ya soma chanjamata shi, ya soma shiga cikin ƴan uwansa, har Alkur'ani yakan dauka ya yi tilawar inda ya iya. Har a sannan ba su koma makaranta ba.

Ranar wata juma'a da rana Allah Ya taimaka Aliyu na gida, naƙuda ya kama ta. Suna zuwa asibiti ba tare da daukar tsawon lokaci ba ta haifo ɗanta namiji.

Sai da aka gyarasu ita da jaririn sannan Aliyu ya sanarwa jama'a. Hatta su Zulaihat sai da suka zo ganin jariri banda Hajiya.

"Wannan dai kamanninki ya dauka Ramlat." Cewar Rafee'ah tana dan murmushi, dukkansu har sannan ba su gama maido kumarinsu ba. Abba ne ya faɗomata a rai sadda aka haifi Ummi. Wani irin kuka ya kwacemata, tun suna cewa mene hakan? Har su ɗin ma suka shiga sharar hawaye. Kowannensu ya fahimci tunanin dan uwansa. Ganin yan uwan Aliyu sun soma zuwa ya sanya suka danne abinda ke zuƙatansu cike da jimami. A ranar aka sallameta ta koma gidanta. Abulle ce ta turomata wata dattijuwa da za ta taimaka mata da wanka na sati biyu.

***
"Mu sanya masa sunan Abba?" Ya fadi yana dubanta, ta kurawa yaron idanu kafin ta girgiza kai.

"Meyasa?" Ya fadi cike da mamaki.

"Saboda abubuwa da dama, ka yi hakuri ka yi mishi huduba da duk sunan da ya dace. Amma banda sunan Abba."

Ya ƙuramata idanu kafin ya jinjina kai kawai. Bayan ya kammala ya dubeta.

"Sunansa Ansar. Allah Ya rayamana."

Murmushi ta yi ta dauke kwallar idanunta na tunawa da Abban.

Haka suka ci gaba da rainon Ansar, ba'a yi taron suna ba. Suna cika sati biyu, dattijuwa Yaha ta tattara da goma ta arziki da Ramlatu da Aliyu suka hadamata ta bar gidan tana ta godiya.

Sai da suka yi wata goma cif suna yajin aikin makaranta tukunna aka koma.

***
BAYAN SHEKARA DAYA..

*Allah Mai iko akan kowane bawa, Shi kadai buwayi gagari misali. Mai shiryawa kuma Mai Rahma.*

"Zan bi ka Abba."

Ummi ke fadi har da kukanta, Ramlat dake zaune tana shayar da Ansar ta dubeshi.

"Don Allah Baban Ummi ka taimaka ka tafi da ita. Ba sai ka sauketa wurin Hajiyar ba? Magiyar ta isa."

Aliyu na gyara zaman hular kansa ya harari Ramlat kadan.

"Kin ji? Yarinyarnan dai nema take ta koma gidan Hajiya din din din, wato shikenan mu sai dai ta kawo mana ziyara ko? To na ƙi wayon, nima ina sonta kusa da ni."

"Anya ba ka fi son Ansar ba?" Ta fadi tana mai kanne mishi idonta guda. Ya ɗan daure fuska.

"Na hanaki tada abinda ya wuce ba kya ji Baby."

Ta yi dariya.

"Afuwan." Abinda ta ce kenan sadda ta cire nonon a bakin Ansar da bacci ya yi awon gaba da shi. Kwantar da shi ta yi sannan ta mike ta karasa ga Aliyun ta taimaka mishi da sanya links na hannu. Kallon juna suke yi cike da so da kauna, abubuwa da dama suka shiga dawo musu a kai.

"Idan ban godewa Allah da Ya ban mace ta gari kamar ki ba Baby, me zan yi?"

Ta yi murmushi wanda ke karamata kyau.

"Allah Ya yi miki albarka. Wallahi idan har ni Aliyu, aljannarki a ƙarƙashina take, na ɗagamaki na ƙara ɗagawa ki shigeta."

Ta yi dariya.

"Dagaske nake."

"Toh na gode sosai."

Ya ja karan hancinta.

"Ni zan fadi haka Baby."
Murmushi ta yi shi kuma ya daga Ummi cak ya ba ta sumba a kumatu.

"Daukomata takalmi."

Jin haka Ummi ta kara wangale baki, Ramlat na dariya ta karasa ɗakin ta dauko. Yana rike da ita ta sanyamata, rakiya ta musu har bakin kofa sannan ta dawo.

Kwanciya ta yi tana tunanin abubuwa da dama. Sauyawar Aliyu ya fi komai yi mata dadi a zuciya.

Tun mutuwar Abba, sai kuma abin ya zama kamar yayewar matsalarta. Tun tana ganin Aliyu kamar karya yake bai bar shaye-shaye ba, tun tana ganin kamar komai yana yi ne don ganin idonta har ta zo ta fahimci dagasken ya bari. Maimakon shan sigari sai ya koma ma'abocin shan ruwan shayi mai citta da kanumfari wanda hakan ya kara taimakawa wurin danne mishi kwadayin sigari balle kwaya.

Duk abinda zai tunamishi da bariki ya yi watsi da shi, ya dinga cusa kansa wurin mutane nagari, y kasance maimakon idan ya dawo daga kasuwa ya je matattarar yan iska, sai ya sauya da zama a masallaci tsakanin Magriba da Isha'i yana jin tafsirin Malamai. Wasu lokutan Ramlat takan farka ta ganshi durkufe cikin Sujjada yana kuka da addu'a. Ita kanta takan ji hawayen ya cika idanunta ta kasa komawa ta mike ta yi alwala ta yi zaman tayashi.

Abu kamar wasa, lamarin ya ci gaba da tafiya a haka. Malam har hawaye ya yi don dadi ganin sauyawar dansa, ya kuma kara yarda cewa bawa bai isa ya shirya dan uwansa ba idan Allah bai shirya ba.
Anan ne Aliyu ya gane cewar ashe ba shi ne ba'a so ba, halinsa aka tsana. Abulle ma ta yi kuka don murna. Akwai da yawa da suka kasa gaskata Aliyun, har lokacin basu shiga harkarsa. Dama haka rayuwa take, ba lallai ne kowa ya so ka ba, hakanan ba ka isa ka ce ba ka da maƙiya ba.

A bangaren Aliyu da yan uwan Ramlat din ma sai godiyar Allah, ya zamana zai je har su ɗan yi hira da Baba Dakta. Hajiya ma sannan ta sakar mishi sai dai akwai ƴar kunya tsakaninsu. Tsakaninsa da Munir kuwa ko gaisuwa bai haɗasu. Koda ya gaidashi ba amsawa yake ba. Ƙarƙari idan ya yi sallama zai amsa yana cin magani. Wannan tasa shima ya watsar da lamarinsa.

Har Gombe ya kwashesu suka je ya sada zumunci da yan uwan Innarsa, sun yi mamaki sosai don ganin abin suka yi kamar mafarki. Kusan Aliyu tun Innarsa na raye rabonsa da su. Wannan ta sa sosai suka tarbesu suna tattalinsa da iyalinsa har suka dawo.

***
Ta shiga binsa daga daki zuwa falo, da ya gaji sai ya tsaya yana kallonta. Ta turo baki kadan.

"Baby, meye wai?"

Ramlat cike da shagwaɓa ta amsa.

"Muhibbat ce fa Baban Ummi. Ta tako gidannan ya fi a ƙirga. Har ta haihu a yi suna ban je ba? Gaskiya ban kyauta ba wallahi."

Ya taɓe baki, ta kuramishi idanu tana murmushi cike da so da kaunarsa da yanzun ta ke ji ba kaɗan ba. Ya ɗan murmure hakanan ya yi haske kadan ba kamar a baya ba. Kasuwa ta dan dawomishi daidai don yanzun yana maida hankali sosai.

"Nayi zaton ma asibiti za ki cemin za ki, ashe ba haka ba ke yawo kike son fita."

Ta daure fuska.

"Ni lafiyata kalau, na fadamaka ba ba ciki bane. Ko ka manta na yi planning?"

"Planning wane iri ne wannan da za ki dinga amai da kwadayi? Yaushe rabonki ma da al'ada?"

Ta numfasa ba don ta wani dauki abin da muhimmanci ba don dama idan ba ta mance ba Nos ta fadamata cikin side effect din maganin har alamomin masu ciki ko daukewar jini zai iya jazamata.

"Shikenan zan je, amma daga nan zan wuce gidan Muhibbat. Don Allah!"

Ta fadi da sauri ganin yana kokarin cewa a'a, ya yi dariya.

"Shikenan, a gaishesu. Ki dai tabbatar kin je asibitin."

Ta rungumeshi gami da yin godiya. Ya bata sumba a kunci gami da bata kudin mota da na ganin likita.

Yana fita itama ta shirya tsaf ta goya Ansar ta fice.

***
RUBUTACCEN AL'AMARI...I just published "BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/pcYjI4bZBab


🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

*_Rufaida Umar_*

Bismillahir Rahmaanir Raheem.


27)


  "Ke kam sai ayi magana ki yi shiru."

Maganar Muhibbat ya katsemata tunani a karo na barkatai, ta kakalo murmushi ta dubeta.

"Kai ban ji ba."

"Cewa nayi ina Ummina?"

Cike da kaunar yanda Muhibbat ke sonta da abinda ta haifa ta amsa.

"Tana can gidan Hajiya."

"Kai jamaa, da alama dai Hajiya ta kwacemana Ummi."

Dariya suka yi lokaci guda. Hira dai ta yi hira har hakan ya mantar da Ramlat damuwarta na cikin da ke jikinta. Duk da amsar da Likita ya ba ta sadda ta mishi tambaya hakan bai gamsar da ita ba sai da ta ƙara tambayar Muhibbat.

"Wai nikam Sis, dama ana iya samun ciki ko anyi family planning?"

Muhibbat ta dubeta, me za ta yi ba dariya ba. Yi ta ke ba kakkautawa har sai da Ramlat itama ta dara.

"Mene wai na dariya toh?"

"Ah ba komai fa. Sai dai na harbo jirginnaki. Ai idan Allah Ya so ikonSa, ba planning ba, ko mahaifar aka juya sai ki ga an samu ciki. Meyafaru?"

Jiki a sanyaye ta ce.

"Implant na saka, abin mamaki wai ana yimin test aka ga ina da ciki. Wai gocewa ya yi."

Jinjina kai Muhibbat ta yi.

"Ana haka, na sha ji ana fadin haka. Wata har allura ta yi amma bai karɓeta ba sai ga ciki. To ke me zai dameki? Ai ko ba komai Ansar ya shekara."

Ajiyar zuciya ta saki, kuma fa hakane. Idan a baya munanan ɗabi'un mijinta ne ta ke gudu, yanzun komai ya kau, ya zama labari da yardar Allah.
Muhibbat ta ci gaba da ba ta shawara akan kar ta damu ba komai. A karshe ta ji zuciyarta ta yi sanyi.

Sai wuraren yamma ta yi mata sallama ta bar gidan bayan ta diremata turmin atamfa cikin wadanda ta samu na barkar Ansar. Godiya sosai Muhibbat ta yi kuma ko kadan ba ta raina ba duk kuwa da cewar ta fi karfinsa. Har kofar falon ta yi mata rakiya suka yi sallama.

***
  Juyi ya shiga yi da ita yana karawa, ita kuwa banda dariya ba abinda ta ke, hakan da ya yi ya zo mata a hagunce don ta yi mamaki. Ba ta zaci ganin irin wannan farin cikin a fuskarsa ba. Farin ciki ne da ya taho tun daga ƙahon zuciyarsa. Ya shiga sumbatar duk inda bakinsa ya kai a fuskarsa.  Ta kauce gami da faɗawa kan kujera tana dariya lokaci guda tana mai watsa mishi harara.

"Kai don Allah Abban Ummi. Duk rawar ƙafar don cikin ne? Ciki na uku?"

Zama ya yi a gefenta gami da riko hannunta.

"Bar ni na yi murna kinji ko? Kyaleni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login