Showing 192001 words to 195000 words out of 226732 words

Chapter 65 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12476

kyakkyawar budurwar da suka gani da aka kirata da yar uwar mijin Ramlatun duk sai suka soma shan jinin jikinsu. A hankali Salma ta yi magana saitin kunnen Bilkisun.
  "Anya wadannan mutanen su na da labarin wace ce Ramlat a baya?"

Bilkisu ta ce "Oho musu, nikam daga suturar jikin yarinyar kamar dai ba karamin mutum shegiyar ta kwaso ba. Ai kuwa ƙafata ƙafarsu har Adamawan naje na ƙarewa danginnasu kallo sosai."

Salma da takaici da bakin ciki ya cika zuciyarta, ita kasa magana ma ta yi. Shekararta sama da ashirin da biyar yanzu amma ko auren fari ba ta yi ba, ga Ramlat har ta kara samun wani ɗanɗasheshan. Don jikinta ya fara ba ta hakan. Burinta yanzu a daura auren ya shigo ta karemasa kallo.

***
Yana kishingide saman kujera a gidan Hisham wanda ya shiga wanka, hotunan da Hafsat ta hankaɗomasa ta whatsapp ya ke aikin kallo, sosai ya yi zooming hoton Madam din tasa ya kasa kauda ido. Murmushi ya ke yana jin soyayya mai tsafta na kara mamaye ko'ina na zuciya da kwakwalwarsa.

Ba zato ya ji an fisge wayar, ya dan dago a ɗan razane don sam bai ji tahowar Hisham din ba. Hisham wanda ke daure da tawul ya ja tsaki.

"Aikin banza, sai afkin karewa mace kallo amma ba a iya tattali ba. To ka tashi, yanzu Yayanmu ya kira ya ce sun iso, ka tarbo su suna waje."

Hussein ya mike zaune gami da dan dafe kai kafin ya mike ya ja guntun tsaki yana gyara zaman rigarsa ta shadda fara ƙal sai dai babbar rigar na ajiye bai sanya ba.

"Ka ci gaba da shiga rayuwata. Kuma ma meyasa ya kiraka bai kira ni ba?"

"Ganin dama."

Daga haka Hisham ya yi ciki da wayar Hussein din a hannunsa don ya shirya, Hussein ya bishi da harara don sosai ya ragemasa nishadi, a bakin gate ya ci karo da su. Ganin wanda bai zata ba sai kawai ya tsaya kamar wani gunki baki a bude.

"RASHEED?!" Ya furta kai tsaye kafin da azama su yiwa juna wata wawuyar runguma da bubbuga gadon baya ana dariya. Can ya sakeshi suka kara cafkewa su na dariya. Nan da nan idanunsu suka kada kuma kamar wadanda ke shirin kuka. Tabbas sun yi masifar kewar juna. Bai ma ga sauran yan uwansa uku da ke tare da su ba sai da ya gama gaisuwar da Rasheed. Najib, Faruk da kuma Khalil duka Yola idan ka cire Faruk da ya zo daga Mubi.

"Allah Ya isa, ban yafewa  matarnan."

Rasheed ya fadi sadda suka nutsu suka zauna a falo. Murmushi Hussein ya yi.

"Ka bar damuwa da ita, ta kusa zama tarihi. Momi ta zo?"

Rasheed ya jinjina kai. Yana nufin mahaifiyarsa, Hajiya Binta.

"Yes tare muke, tana can Yola wurin Dada."

Haka suka yi ta hirarsu cike da nishadi, shi dai Hussein bini-bini zai duba agogo. Ganin lokacin sallah na ƙaratowa ya dubesu.

"Ya kamata mu hanzarta wuce masallaci ko?" Lokacin sallah ya gabato."

Me zasu yi ba dariya ba.

"Lokacin sallah ko lokacin daura aurenka? Kai Malam ba ka da kunya wallahi."

Faruk ya fadi yana dariya.

"Bar shi kawai, ai idan bai yi hakan ba bai cika sabon shiga ba."

Hussein dai har ga Allah sun soma ba shi haushi, dagaske so yakeya ga an hanzarta an tashi an tafi.

"Na rantse zan muku ƙofi yanzun nan ku ga maciji."

Ya fadi yana mai mikewa tsaye suka yi dariya sosai shi kuwa ya shiga zura babbar riga yana mai tafiya gaban madubin dake falon yana gyara zamanta. Karshe ma hular ya dauka ya shiga gyaramata zama yana ji AlHassan na cewa su tashi don da alama Angon  zai iya ficewa ya bar su.  Nan kuma wadanda ba su da alwala duk suka dora sannan aka kama hanya bayan Hussein ya feshe dukkan jiki da turaruka masu tsada da kamshi har kala uku. Bababn burinsa Ramlat ta zama mallakinsa kafin kowane irintsautsayi ya gifta da ba ma ya fatansa.

***

Misalin karfe biyu da mintuna, dubban jama'a suka shaida daurin auren HUSSEIN AMINU GIDADO da RAMLAT KHALID MU'AZZAM akan sadaki har dubu ɗari wanda nan take aka damƙawa Babanta Dakta matsayinsa na waliyyinta.

Bakin Hussein ya ƙi rufuwa, sosai daurin auren ya tara mutane. Hilal kansa sai da ya halarta, duk da Hussein ya san shi, haka suka gaisa faran-faran suka yi hotuna. A karshe aka dunguma gaida iyaye.


***
Babu damar sallah a wurinta sakamakon tana fashinsa, sai dai ta yi sujjadar godiya ga Allah kuma ta yi addu'a sosai.

Bayan ta mike ne Amrah ta ba ta tissue.

"Don Allah kar ki ɓata kwalliyar mana."

Ta karba tana goge hawayen.

"Kukan munafunci ne kawai, mace sai ka ce yau aka taɓa dauramata aure. Aure na uku?"

Bilkisu ta fadi da dariyar kissa, Hafsat jin ta ce aure na uku yasa ranta ya ɓaci, dadinta Hussein bai ɓoyemusu komai na labarin Ramlat ba. Dama tun zaman Bilkisun da irin kallon da suke jefamata ita da abokiyar rakiyarta ta ji sun ba ta haushi.

"Ko aure na nawa ne ai aure ne. Duk wacce ta san me ta ke yi dole zuciyarta ta karye a wannan rana, ko bakomai ta san nauyin da Allah Ya ɗoramata."

Maganar Hafsat ta zo wa su Bilkisu a bazata, wato dama sun san komai? Nan da nan ransu ya kara yin baƙiƙirin musamman Murja da Fareeda da basu jima da shigowa ba, suma dai ganin kwakwaf dinne.

"Muje falo ga Angon ya zo."

Fadin Muhibbat da ta shigo, ta ja hannun Ramlat suka fice, Aisha kam ji ta yi kamar ta goya Hafsat don dadi, balle kuma Rafee'ah da ke dariyar shaƙiyanci. Sosai Hafsat ta burgesu don kanta a waye yake ba karya. Ai su Bilkisu na jin haka suka bi bayansu rii duk domin su ganewa idonsu Angon Ramlatu. Ai kuwa sun yi kyakkyawan gani da ya birkita tunaninsu.

Yana durkushe gaban yan uwan Ramlatun ana kwasar gaisuwa, sai ga Amaryar. Nan da nan tsofaffi aka sjiga guɗa da kirari. Ya kasa kauda idanunsa a kanta, ita kuwa ganin irin kallon da yake mata babu kunyar ido yasa ta yi ƙasa da idanunta.

Tsakiya aka zaunar da ita shima ya zauna, yan uwa aka baibayesu mai hoto ya shiga aikin dauka. Kirjin Hussein banda bugu da sauri babu abinda ya ke yi, ji yake kamar ya ja ta ya sanya a babbar riga ya gudu da ita. Sai da aka kammala hotunan har da mutan Adamawa sannan Ango da tawagarsa suka fice.

Murja da Fareeda dai fasa yinin aka yi aka dunguma aka tafi yayinda Bilkisu ta daure suka zauna. Amma Salma rantsuwa take yi da ƙarawa cewa asiri ne kawai aka yiwa Hussein domin kuwa wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa, ko makaho ya shafa Hussein ya san ya wuce aurar Ramlat duk da dai itama ba baya ba.

***
Sai wuraren bakwai na dare sannan jama'a suka soma tafiya, wadanda suka rage da zasu je Adamawa ba su da yawa. Ramlat ta yi ɗai-ɗai saman gado tana hutawa duk ta gaji don yau ba karamin zirga-zirga ta sha ba a cikin gidan kawai. Kowa ya zo sai an kirata an ɗauki hoto, wannan zamani na hoto har haushi ya ke ba ta.

"Ke kinga mutuniyarki ko? Ta kasa ɓoye abinda ke cikinta? Kai Allah Ya rabamu da hassada mugun ciwo."

Amrah ke zancen ganin duka na dakin babu bare, daga su sai Nusaiba sai Aisha sai kuwa Hunainah dake sallah.
Murmushi Ramlat ta yi.

"Ni mamaki ma abin ya dinga ban, ta madubi fa ina kallon yanda suke hararata amma da mun hada ido sai su basar."

"Ke wa ya taɓa samun daukaka idan bai hadu da yan hassada ba? An fadamaki tsakani da Allah za ta je Adamawarnan? Ni wallahi ban san sadda Bilkisu za ta sauya ba. Gaba daya a farko kamar ba za ta yi ba." Fadin Rafee'ah wacce ke shan wani youghurt da ƴan Yola suka kawo.

"Dama DAN ADAM ance mai wuyar gane hali." Aisha ta furta.

Haka aka yi ta hira, har zuwa sadda Hafsat ta shigo da sauri ta hau kan gadon gami da sanyawa Ramlat waya a kunne. Ta kalleta kafin ta tambayi waye cikin rada-rada ta ce.

"Angonki."

"Assalamu alaikum."

Ta ji muryarsa sadda ta rike wayar sosai a kunnen, amsa sallamar ta yi.

"Shi ne kika kashe wayarki ko? Gaba daya kin sa na rasa nutsuwa."

Ta sauke ajiyar zuciya, ta tuna ashe fa tun a wurin kwalliya ta kashe wayar ba ta ƙara bi ta kai ba.

"Ina neman afuwa."

"Naji, amma yanzu ki fito ina mota. Gaisawa kawai zamu yi."

"Ka..."

Bai bari ta kai aya ba ya katse wayar, dole ta cire ta miƙawa Hafsat da hankalinsu gaba daya ba ya kanta. Ta matsa kusa da Amrah ta mata raɗa. Amrah ta murmusa.

"Kar ki manta dai, yanzu miji ne a wurinki ba manemin aure ba. Umarninsa za ki bi kawai. Ki je ba komai"

Ta mike ta gyara zaman dankwalinta ta yafa gyale sannan ta fice. Tana jin yanda matan dakin suka dauki sowa murmushi kawai ta yi ba ta ko juya ba.

A farfajiyar gidan ta ga mota sabuwa dal sai sheƙi ta ke, ba ta yi zaton shi ne a ciki ba sai da ta zo giftawa ta ji ya mata hon, hakan ya ba ta damar bude kofar don ba'a ganin na ciki. Shi din ne zaune kuwa, ta shiga ta rufe sakamakon AC da ke a kunne. Kamshin motar da kamshinsa sun hadu da sanyi sun saukarmata da ni'ima a zuciya. Ta dubeshi, ya cire babbar riga hakanan hular na ajiye saman gaban motar.

"Ina wuni."

"Lafiya."

Ya furta tamkar ba ya so. Can ya ce.

"Ya gajiyar biki? Anya kin ci abinci? Sai naga kamar kin faɗa."

Ita mamaki ma ya ba ta don haka ta kasa amsawa.

"Kin yi shiru."

"Uhm, na ci."

"Kin fa zama matata, amma na lura da ke tun dazu kamar murmushin dole ki ke yi."

Yanda ya yi maganar kamar zai yi kuka yasa ta dubansa, gaba daya ya juyo ya matsa dab da ita, ta ji nauyinsa, shi kuwa hakan yake so dama, tun shigowarta ya ke kokarin su hada ido amma hakan ya gagara. Za ta juya kai ya yi saurin riƙo haɓarta ya karkato da kan. Ta dora hannunta a saman nasa da zummar kautarwa. Sai dai ya rike hannun tamau.

"Please ka sakarmin hannu."

Ta ci gaba da kokarin kwacewa don ba ta shiryawa hakan ba. A hankali ya saki hannun.

"Na saki. Shikenan?"

Ba ta ce uffan ba.

"Ki je kawai, sai mun yi waya ko?"

Ta saci kallonsa, kamar dai fushi ya yi. To ita kuwa me za ta ce? Ina sabon da za ta sake don ya rikemata hannu?

"Kin tsareni da ido, ba na kyaleki ba?"

Yanda ya yi furucin sai ma ya ba ta dariya, ta kauda kai tana murmushi.

"Ni kike wa dariya?"

"Aa."

"Kin ma iya ki ci abinci, ni da ban ji ki ba kasa daurewa nayi da komai har sai yanzu da na zo na ganki. Idan na tsaya wassafa kalar farin cikin da nake ciki, zamu kwana mu wuni a nan."

A hankali ya jawo hannunta mafi kusa da shi ya damƙe cikinnasa. Wani yarr ta ji kamar yanda shi kansa sai da ya ji wani shock. Ya ƙurawa lallen idanu.

"Allah Ya bani ikon riƙe ki amana Ramlat. Ya ba ni ikon yi maki adalci a zamantakewarmu. Na san na ɓatamaki rai da yawa, amma ki yi hakuri. Haka nake, ban yarda da soyayya kafin aure ba, bayan aure ke kanki yanzu son zai fi maki armashi a kowace tafiya. Abubuwa da yawa ba ma sai na fada ba tunda ke ba yarinya ba ce ko?"

Ta saci kallonsa don gaba daya sautinsa ya sauya, gira ya ɗaga mata yana jifanta da tattausan murmushi. Ta kauda kai ta shiga kokarin zame hannunta.

"Na dauka zaman hakuri da biyayya kawai zamu yi ai tunda cikinmu ba wani mai kaunar ɗan uwansa."

Ba zato ya fisgota kafadarsu na gogar juna kamar yanda fuskokinsu tuni ya hadu wuri guda sai hucin numfashinsu da ke gaurayewa.

"Kina da tabbacin bana sonki? If yes, prove it."

Ta lumshe idanu tana shaƙar kamshin lemon mint da bakinsa ke yi. A hankali kuma ta yi nufin yin baya ya rike kanta kafin ba zato ta ji bakinsa a nata. Shirun kusan mintuna biyu kafin ta tureshi ya yi baya, babu kwari a jikinsa, don haka ya jinginar da kai yana kallonta da soyayyun idanunsa. Ita kuwa sai afkin goge baki da ta ke yi bayan ta zari tissue dake saman gaban motar. Ya kauda kai kadan yana dariyarnan irin na wanda aka rainawa wayau.

"Kai, ni kike gogewa baki don na taɓashi?"

Ta daure fuska ta harareshi.

"Saboda ban shiryawa hakan ba. Ai ba haka tsarin zamantakewar tamu ya ke ba."

Daga nan ta wurga tissue din a jikin motar duk dacewar hatta da kujerun baa ciremusu ledojinsu ba. Tana kokarin bude kofar ta fita ya kara yi mata wata wawuyar fisga, duk kokarinta ta kwace abin ya gagara. Haka ya taramata miyansa a baki kamar yanda bai kauda bakin ba sai da ya ji ƙarar tafiyarsa, loko da saƙo sai da ya tabbatar ya gauraye a bakin kafin ya saketa. Iyakar shaƙa ta shaƙa, ta bankamasa wata hararar. Ya ɗaga mata yatsu.

"Good night Love."

Ta bude kofar kawai ta fice, ya bita da kallo yana jin kamar kar ta tafi saboda wani tsananin kewa da ya kamashi nan take, har sai da ta shige gidan kafin ya lumshe ido da murmushi can kuma ya buga sitayari.

"Ya Rabb!" Ya fadi cike da nishadi, soyayyar Ramlat na kara ƙaimi a ransa. Dakyar ya samu kuzarin jan motarsa, kafin ya fice daga gidan ma sai da ya kira wayar Hafsat ya jaddada mata akan ta shaidawa Ramlat ta kunna wayarta.
[3/17, 9:18 AM] +234 703 629 0938: I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://www.wattpad.com/story/229538078?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_reading&wp_page=reading_part_end&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=3RG5g2a5w6izCuKU8HhNqobuQjDF3XsdSGdqdVtdShDrSoD84AKgTAv38ifr8A0P6JNqIoYXqVCm072j3Kj010bX%2FXCFmaovF0BtpPRfTxUwRF7KoTA35HGU0Qpfh9Zn







🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

59)


Kusan gaba daya mutan dakin bacci suke yi idan ka cire Amrah da ke zaune tare da amniyarta tana tayata wajen shirya kaya a ƙatuwar akwati. Wasu kayayyakin kuwa su na fitarwa domin bayarwa. Amrah na lura da yanda gaba daya ba ta da sukuni, jefi-jefi takan sa hannu ta share bakinta.

"Wai ke kam lafiyarki kuwa?"

Ta dawo hayyacinta.
"Me kika gani?"

Harara ta watsamata.

"Kamar ya me na gani? Alhalin ina lura da yanda tun dazu kike wani shagala da shafa baki, saurin me kike?"

Ranta ya kara baci ta ja tsaki.

"Me kike nufi? Idan ma wani abin kike nufi gwara ki watsar tun a nan don kinsan irin zaman da na shirya za yi da Hussein."

Amrah ta jinjina kai.

"Ko wane irin zama ne ba zan hanaki ba tunda ke ba yarinya karama ba ce da zan tsaya ɓata bakina, abu daya da zan tunasar da ke, yanzu Hussein ya tashi a kowane matsayi ya hau matsayin mijinki. Idan kin gyara kanki, idan kin ɓata ma ke za ta shafa."

Shiru kawai Ramlat ta yi ba ta kara tankawa ba. Can kuma aka kwankwasa kofar dakin da sallama aka shigo. Hafsat ce sanye da riga da wando na bacci kasancewar ita ta kafe ta ƙi bin yan uwansu Hotel, hakan yasa Hajiya ta mata wuri a makeken gadonta. Hamma ta ke zabgawa duk suka dubeta.

"Adda wannan Yayannamu ya hana ni bacci wallahi, don Allah ki tausayamin ki kunna wayarki ku yi magana. Ni ga wayata ma na bar maki a nan don wallahi da zarar na soma nisa a baccin yake tashi na."

Dariya ta ba su, aikuwa ba wanda ya kai ga cewa komai sai ga wani kiran. Da sauri Hafsat ta miƙamata.

"Yauwa gashinan. Sai da safe."

Ta fice Amrah na addu'ar Allah Ya tashemu lafiya. Ita kuwa Ramlat wayar ta ɗaga ta ɗora bisa kunne yayinda Amrah ta juyamata baya ta ci gaba da aikin da tuni ma sun ƙarƙare sai tattarawa. Sallama ta yi, jin muryarta sai ya sauke ajiyar zuciya. Shiru ya dan biyo baya kafin ya tanka.

"Kin hana ni bacci Heart."

Ta ɗan saci kallon Amrah wacce hankalinta na can wurin harhaɗe kaya ba ta ce masa komai ba.

"Meyasa ba ki kunna wayarki ba? Kinsan zan nemeki, zan so na ji muryarki. Bacci ya kauracemin, ba ni da burin da ya wuce na ganki a gidana. Heart, kin yi shiru."

Ta ɗan daure ta yi magana.

"Me zan ce?"

"Ko mene ne ki fada daidai ne. Amma kar ki kara kuskuren da ki ka yi dazu, idan kuwa hakan za ki ci gaba a zamantakewarmu, za ki sha wahala a wurina."

Murmushi ta yi mai sauti.

"Dariya ma na ba ki?"

"Ko kusa, bacci fa nake ji."

"Ni kuma ban shiryamasa ba, hira na ke son mu yi. Koda dai tambayar da nake son yi maki ba ta waya ba ce, sai mun haɗu ga ni ga ki."

Nan ma ba amsa sai shirun daga wajenta, har Amrah ta mike ta fada bandaki ta dauro alwala, yana ta magana Ramlat sai uhm ko uhm uhm. Tana kallo Amrah ta kashe fitilar dakin ta bi lafiyar gado kusa da Babynta ta kwanta. Cikin takaici Ramlat ta ce.

"Malam kowa fa ya kwanta, nima gyangyaɗi nake, ina son..."

"Be serious Heart, ko kadan ba ki tunanina?"

Ta lumshe ido ba tare da ta tanka ba.

"Talk."

Ya fadi a hankali. Ita har mamaki ma ya ke ba ta.

"Shiru ma fa magana ce ko? Inji Hausawa."

Ya kara fadi yana yar dariya, ta cije lebba don takaici, wato ma ya riga da ya fassarata.

"Kai ka san wannan, ni abinda ya tsayar da ni daban ne. Sai da safe bacci nake ji."

Ba ta jira komai ba ta kashe wayar gaba daya. Mikewa ta yi tana murmushi har ta na tuntube da ƙafar Dijen Daura da ke bacci a saman katifa. Hakuri ta ba ta sannan ta fada toilet. Alwalar itama ta yi ta nemi wurin kwanciya.

***
Tun da Asuba masu tafiya Adamawa suka tashi ba'a koma ba. Daga mai wanka sai mai sanya kaya, wasu kuwa da ba za su sami zuwan ba, sai suka fada kicin don yin abin kari. Ramlat dake bacci sakamkon tana fashin sallah, dolenta ta wartsake don ba karamin takuramata su Rafee'ah suka yi ba akan ta mike ta yi wanka. Bayan ta fito ta shirya cikin atamfar Holland kalar light

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login