Showing 90001 words to 93000 words out of 226732 words
salati na yi hakanan masu fadin kai! Kai! Suma suna nasu.
Luguden da zuciyarta ke yi ya ƙaru, ɓacin ranta ya ninka na farko. Ta kasa koda motsi, ta kasa fitowa balle ta je ta ba mai shi hakuri ta nemi gafararsa.
'Da ka san damuwar da ke cikin zuciyata, da ka yimin uzuri kamar irin wanda na taɓa samu a wajen wani...'
Ta kasa ƙarasa zancen zucinta ganin wacce ta fito daga mazaunin kusa da direba. Shakka babu fuskar ba ranar ne farkon ganinta da ita ba. Fuskar da ta zo har ofishinsu.
"Isa da taƙama za ki nunamana?! Kin yiwa motata illa kin zauna kin hakimce ko gezau? Ke ƴar gidan uba wace ce?!"
Sanin da ta yi ita din mai laifi ce yasa ta fitowa daga nata motar, har lokacin akwai hawaye a fuskarta. Wannan hargagin na Hajiya Zeenatu bai dameta ba kamar yanda sanyo ubanta ciki ya yi mata zafi, ko ba komai shirunta ya jazamata.
"Kiyi hakuri don Allah." Ta fadi tana haɗiyar yawu, damuwar da ke ranta ma ya isheta. Kowa ya yi mata caa akan ba ta kyauta ba yayinda Hajiya Zeenatu ta dage akan lallai sai ta raina kanta, sai ta biya ɓarnar da ta yi mata.
Ramlat kallonta kawai ta ke sakaka, ita ta ma rasa me za ta ce da ita. Hakuri kawai ta ke bata don ba ta jin yin faɗan musamman a yanzun da ta ke jin tsanar kanta har cikin ranta.
Basu yi aune ba sai jin ƙarar murfin mota suka yi, hankalinsu ya kai gun. Kowa kallonsa yake har ya ƙaraso yayinda Ramlat ta ji bugun zuciyarta ya ƙaru, ba ta taɓa zaton wani abu zai ƙara sa ta ganshi ba. Yanzun kan ta yi amannar ba zai kyaleta ba sai ta biya ɓarnar da ta yi musu, ko ba komai yanzun zai ce da gayya take mishi ta'adi.
Shi kuwa koda ya ƙaraso kallonta ya yi na ƴan sakanni, kallon sani ya yi mata, kallon na ganeki. Ta kauda kai shima ya kawar, kallon da ya kai Hajiya wuya, ta daga hannu da nufin marin Ramlat, caraf ya riƙe hannun. Jama'a aka saki baki don diramar ma tafiya yanda ya kamata, an baza baki da hanci, go slow kam sun haɗa, masu zagi na yi, masu tsayuwa kallo suna nasu aikin.
Hajiya ta dubeshi a fusace.
"Ita yar iskar ina ce za ta tsaya tana ƙaremaka kallo?! Dama nasan ai da biyu ta bugi motar! Na ganeta! Ba ita ce wannan marar kunyar ba ta Revenue? Za ki san ki taɓoni!"
Daga haka ta fisge hannunta ta yi gaba, Ramlat na hawaye ta ke kallonsa. Bakinta ya yi nauyi, dakyar ta motsa.
"Ka yi hakuri. Wallahi ba da gangan na aikata ba."
"Ba komai." Ya fadi ƙasa-ƙasa, daga nan bai ce uffan ba ya wuce ya shiga mota ya ja suka bar wurin. Itama motarta ta shiga tana ji wasu na fadin.
"Ke kam Allah Ya so ki da rahmarSa. Tab!"
Wasu kuwa cewa suke.
"Ina rahmar? Ba ku ji me Hajiyar ke fadi ba? Da alama ta san ma'aikatar yarinyar, za kuwa ta yi mata sanadin barin aiki."
Ita dai Ramlat wacce kanta ke bala'in sarawa, ta ja motarta dakyar ta bar wurin.
Koda ta isa gida, Hajiya ta tambayeta abinda ya faru ganin yanda ta yi kaca-kaca, idanunta jage-jage da hawaye. Ba ta ɓoyewa Hajiyar komai ba. Ranta ya ɓaci.
"Ai ga irinta nan! Ga irin ABINDA AKE GUDU nan Ramlat! Shekara nawa da wucewar abu, yanzu gashinan yana bibiyarki. Ita kuwa wannan Hajiyar a zatonki za ta kyaleki ki ƙara taka ma'aikatarku? Uhm, Allah Ya kyauta."
Daga nan Hajiya ta yi shiru tana huci, ta tausayawa Ramlat amma fa haushinta ba ta da matakin dauka, ba ta da abin yi don kuwa Ramlatun ce ta fara ɓatawa kanta suna. Har Ramlat ta yi ɗaki ba ta ce mata uffan ba.
Ta kudurce a ranta za ta bar aiki, sai dai kuma ta ya za ta dinga wasu cikin hidindimunta har ta taimakawa gida da yaranta?
Ta mirgina saman gadon gami da lumshe ido. Can kuma ta buɗe su cikin zurfin tunani. Ya yi daidai da dawowar yara daga islamiyya, gaba daya suka shigo ɗakinta suna mata sannu da zuwa. Tana murmushi ta mike zaune.
"Kun dawo?"
"Eh, yau Affan bacci ya yi ta yi a aji." Cewar Ansar, Affan kuwa ya yi lamo jikinta, ta shafi kan yaron tana murmushi.
"Wai haka?"
Ya gyada kai, bai iya ƙarya ba ko don tsoro. Suka cikata da surutu, dakyar ta korasu su wuce chanja kaya.
Aliyu ya faɗomata a rai, mutumin da ya bar duniya bayan ya yi kyakkyawar shahada, shi ne ake jefamata bakar magana ake yayata abinda ta aikata dominsa?
'Ko me ya faru, laifinki ne.' Ta shiga gyada kai tana gaskata sashi na zuciyarta dake tunasar da ita hakan. Shakka babu laifinta ne. Dakyar ta samu ta shafe babin a kwakwalwarta ta mike ta shiga wanka. Ta san ƙaryarta ta iya barin aiki saboda Hajiya Zeenatu. Addu'a ya fiyemata komai. Shi ne makamin kowane mumini.
***
"Aikin banza! Kaima ai kallonta ka tsaya yi! Akan wane dalili?"
Hajiya Zeenatu ke wannan kalamin, tun dawowarsu gida duk inda ya saka ƙafa sai ta bishi da zafafan kalamanta na zargi. Idanunsa suka kaɗa, zai shiga wanka ta nufi kofar banɗakin.
"Wankan me za ka yi? Wato ba ka ga girman laifin da ka aikata ba ko? Shi ne har za ka shiga wanka?! Wallahi ka jawowa yarinyarnan! Sai nayi mata sanadin aiki! Sai na wulakanta ta!"
"Daga ranar da kika sanya aka koreta aiki, ki kwana da sanin da kaina zan dauketa aiki a Office dina!"
Cak! Ta tsaya,ta kasa kwakkwaran motsi, dakyar ta iya haɗiye yawun da ya tararmata a baki. Cikin tsananin mamakin kalamansa ta ke dubansa. Wannan ba Hussein din da ta saba juyawa ba ne, bai yi mata kama da wanda zai ɗauki wargi ba. Kalamanta ba su ƙara kashemata jiki sun jefata ruɗu ba sai da ta ƙara tsintar muryarsa.
"Yes Zeenat! Ina miki rantsuwa da Allah daga ranar da kika yi kuskuren raba yarinyarnan da aikinta sai ta dawo aiki a ƙarƙashina! Idan kishi na kisa, ya kashe ki! Haba! Wannan wane irin masifa ne! Wane irin takunkumi ne? Kin hana mace ko ɗaya aiki a gidanki, kin hana na yi aiki da mace a ofis! Babu dama ki ga mace ta kirani ko ta yimin magana ta media sai ki ɗau zargin duniya ki aza a kaina! I'm fed up! Nifa ba yaro bane!"
Daga nan ya gifta ya shige banɗaki gami da banko ƙofar har sai da ta tsorata. Gumi ke tsiyaya daga saman fuskarta duk da Ac dake gudu a dakin. Safa da marwa ta shiga yi gami da kwance ɗankwalinta, akwai babbar matsala! Akwai abinda ke shirin faruwa.
'Ko ita ce yarinyar da Gora ya gargadeni a kai?'
Ta fadi a kasan ranta, shekarun baya da suka gabata, Gora ya gargaɗeta akan abinda zai iya afkuwa muddin ba ta kula da lamarinta da Hussein ba. Ya tabbatarmata ita ce za ta zamo silar rushewar kowane aiki. Wannan ne dalilin da har gobe ta ƙi jinin kowa ya raɓarmata Hussein. Namiji daya tamkar da dubu a rayuwarta. A kansa ta aikata abinda acewarta shaiɗan ba zai iya ba.
"Dole na dauki mataki!" Ta furta a fili kafin ta fice daga dakinsa zuwa nata a gigice.I just published "BABI NA TALATIN" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/5Py5Xl04Mab
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
*_Rufaida Umar_*
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
30)
Wannan abu da ya faru, sai ya ƙara ragewa Ramlat walwalarta a Ofis. Tambayar duniya ƴan ofis din sun yi amma ta nunamusu ba komai. Tsakaninta da Halima gaisuwa kawai, daga nan ba ta kara bari wani abin ya shiga tsakaninsu. Ga Halimar hakan ba karamin dadi ya yi mata ba, ko ba komai ta samu wani makami wanda yake ganin a koyaushe za ta iya rushe Ramlat din da shi. Wannan girma da ƙimarta da ake gani a daina.
***
Bayan sati daya da auren A'isha, ranar Lahadi misalin karfe uku na rana, Ramlat ta shirya cikin riga da skirt na leshinta ja, ya yi mata kyau sosai, fuskarnan banda hoda ba abinda ta shafamata, sai gidan A'isha. Nan ma sai da A'ishar ta yi ta roƙonta akan ta zo. Abin ita har mamaki ya ba ta, yarinyar da basu fiye ɗasawa ba, raini ya shiga tsakaninsu, yau ita ke nemanta? Murmushi ta yi, aure ba karamin gyarawa mutum zama yake ba. Kodayake me akai da maza ma?
Ɗan sahu ta hau zuwa gidan A'isha, su Ummi tun safe Muhibbat ta zo ta ɗaukesu don halartar taronsu na Zuri'a.
***
Kai tsaye ta shiga cikin falon da sallamarta, A'isha ta amsa tana mai fitowa daga kicin cike da zumuɗi da jin dadi.
"Kai Maman Affan, wai sai yanzu? Wallahi kamata ya yi ki zo tun safe ki wuni."
Harara ta ɗan watsamata tana murmushi.
"Ko? Ga babbar kobo, to ban iya wannan katoɓarar ba."
Dariya A'isha ta yi, ita kuwa Ramlat sai bibiyarta take da kallo yanda ta yi fresh ta yi ɓulɓul abinta tsaf.
"Toh don Allah ku din ne ba wanda na ƙara gani a gidannan, nasan shirye-shiryen auren Yaya ma zai iya ɓoyeku amma ai ba hujja ba ce."
Taɓe baki Ramlat ta yi tana mai ajiye jakarta.
"Ke ni rabani, ba wani shiri da nake yiwa bikinnan. Inace dai mijinki ba ya nan?"
Ta tambaya sadda ta dakata da yaye mayafinta da take shirin yi. Girgiza kai A'isha ta yi.
"Ya fita amma ba jimawa zai dawo, abokinsa ne zai zo shi ne ya fita yin cefane. Ni wallahi naji dadin zuwanki, ko ba komai za ki taimaka mu shirya daddaɗan abinci."
Ramlat ta ji inama ba ta zo ba. Ba taya girkin ne matsalarta ba, ba ta so Hisham din yana gida ba ne. Dakyar A'isha ta samu ta lallaɓata ta zauna. Ba jimawa kuwa sai ga Hisham. Shi kansa ya ji dadin ganin Ramlat, mutum ne mai barkwanci don ko kadan bai tsaya wani kunya ko ƙumbiya-ƙumbiya ba. Itama ganin haka ta ɗan saki jikinta, daki ya shige su kuwa suka nufi kicin suka shiga aiki, Ramlat na mitar inama ba ta zo ba. Ita dai A'isha ba ta iya magana ba don tasan yanzun sai ta fadi abinda zai sa ta bar gidan ba shiri. Sai da suka yi la'asar suka faɗa kicin.
Fried rice suka yi wanda ya sha hanta. Suka yi chicken pepper sai hadin salad da lemun Mango. Komai suka jera saman tebur, A'isha ta shige don yin wanka. Ita kuwa dakin da ke falon ta shige ta hau shirin tafiya gida.
"Gaskiya Antinmu ba inda za ki je, ki yi hakuri mu ci abincin gaba daya. Na rantse har gida zan kaiki." Hisham ke maganar cikin alamun roƙo. Duk yanda ta so ta ƙi hakan ya gagara, magiya irin na Hisham sai da ya ci galaba a kanta, ta kara duban su da zummar magana, wayar Hisham ta yi ƙara. Ya dubesu kafin ya ce
"Inaga ma ya ƙaraso. Bari na fita."
Daga nan ya fice, dole Ramlat ta koma ta zauna A'isha na mata dariya.
***
Hussein ke tuƙin, Hajiya Zeenatu tun washegarin rikicinsu ta yi tafiya zuwa Abuja wurin Aminiyarta a yanda ta sanarmishi sai dai a zahirin gaskiyar Nijar suka wuce. Wannan karon wajen wani buzu za ta je don samarwa kanta mafita. Dama an dade ana ba ta labarinsa.
Waya yake cikin nutsuwa, sai ka nutsu za ka san me yake fadi. Magana yake fitarwa kamar ba ya so, a zahiri haka muryarsa ta ke. Motsa bakin yake kamar ba ya motsawa.
Ya yi parking a wani madaidaicin gida, ya sa hannu ya bude murfi ya fito. Hisham dake tsaye ya ƙaraso suka cafke suna dariya. Ya haɗe cikin shaddarsa blue. Ya dora hula mai adon fari da ruwan blue. Sai yatsunsa biyu na dama da basu rabo da zoben azurfa guda biyu, sai agogo ruwan silver da ya ɗora.
A Gym suka soma haɗuwa da Hisham, har yawan haduwartasu ya sanya shakuwa mai ƙarfi ya shiga tsakaninsu. Hatta da Hussein ya yi mamaki don bai zaci zai sakarwa kowane mutum fuska ba har su zama abokan juna. To sai ya kasance Hisham mutum ne wanda nan da nan za'a iya sabo da shi, yana da barkwanci sosai. Duk da irin abotarsu, sai ya kasance a waje. Koda wasa bai taɓa gayyatarsa gidansa ba balle ya fadamishi wani abu da ya dangance shi. Shi ɗin dai ya gayyaceshi sun gaisa da iyayensa ba sau daya ba kuma ba biyu ba.
"Kamar ni a yi bikina a ƙare shi ne ko ƙeyarka ban gani ba ko? Daidai kenan?"
Taɓe baki Hussein ya yi.
"Kana da mita. Hakurin ne ba za ka iya ba? Ba abin tada jijiyar wuya a abinda ya wuce."
Hisham ya yi ƙwafa, shi kuwa murmushi kawai ya yi, har suka karasa ciki suna ɗan hirarsu.
***
A'isha ta mike ta fito daga ɗakin ta bar Ramlat kwance saman katifa. Sun gaisa da Hussein kafin Hisham ya dubeta.
"Ki cewa Yayarmu ta fito don Allah."
Ta amsa da toh tana murmushi sanin halin ƴar uwarta, ba lallai din ta yarda ta fito ba. Aikuwa kamar yanda ta zata hakan ne, cewa ta yi ba ta ga dalilin fitar ba tunda ba ita ce matar gidan ba.
Yanda ta faɗa haka A'isha ta kai saƙon ba surki, abin sai ya Hisham dariya shi kuwa gogan kamar bai san ana yi ba. Wayarsa yake amsawa da Hajiya Zeenatu wacce ta tafi kamar ba ta tafi ba, bini-bini za ta kira ta ji a inda ya ke. A karshe ma cewa ta yi za ta gaisa da Hisham din. Ya cire wayar a kunne ya miƙa wa Hisham.
"Madam."
Hakan da ya faɗa ya ankarar da Hisham ko wace, suka gaisa sai dai ya ɗan yi turus jin muryar kamar ta babbar mace amma bai nunamishi ba. A karshe ya mikawa A'isha wayar kamar yanda ta buƙata. Ita kanta ta yi mamakin jin muryar mace kamar Hajiyarta. Abinda ta kawo, matar ƙatuwar murya gareta ne kawai, banda wannan ba wani abu.
Sai da ta kawowa Hussein ruwa da lemu kafin ta koma wurin Ramlat.
***
"Kai kin ganshi? Wallahi kamar wani buzu."
"Astagfirullah, ke fa matar aure ce." Ramlat ta katseta da sauri. Anan itama ta ankara da katoɓarar da ta yi, ta ja istigfari kafin ta yi dariya.
"Allah kuwa ban faɗa don wani abu ba, kawai dai na ganshi ɗan gayu. Da ace ba ki taɓa aure ba kuma ke fara ce, ba karamin matching za ku yi ba."
Daure fuska ta yi, ta ɗan ji takaicin kalaman A'isha, sai ya ɗan yi mata fami da irin cin zarafin da Halima ta yi mata a ofis. Ganin yanda fuskarta ta sauya ne yasa A'isha gyara zancenta.
"Kiyi hakuri, wallahi ba wai ina nufin wani abu ba, kawai ganin irin yanda ya haɗu ne sai nake ga kamar bai dace ma ya auri wacce ta taɓa aure ba ball.."
"A'isha! Ya isa haka don Allah ki rabu da ni. Wai ni sa'arki ce?"
Ɗan taɓe baki A'isha ta yi tana murmushi.
"Allah Ya ba ki hakuri babbar Yaya, na yi shiru."
Ramlat ba ta ƙara magana ba don tasan ban hakurin ma irin na ƙannen zamani ne. Karshe ma miƙewa ta yi ta soma gyara mayafinta.
"Tafiya zan yi, tunda har na miki mai wuyar ai shikenan."
Anan ne kuma A'isha ta marairaice.
"Wallahi ba zan iya cin abinci da baƙon nan a wurin ba. Don girman Allah ki yi hakuri ki zauna. Ya ce fa har gida zai kaiki."
Gaba daya ta koma kalar tausayi tana roƙonta. Wayar Ramlat ta yi ringing, ganin Hajiya ce yasa ta nunawa A'isha
"Kin gani dai da idonki ko? Uwata nemana ta ke yi."
Daga haka ta ɗaga wayar, aikuwa tambayar da ta soma jefomata shi ne me ya tsayar da ita?
Da sauri A'isha ta karɓi wayar ta yiwa Hajiyar bayani gami da roƙon alfarmar Ramlat ta jira har baƙon ya tafi sannan Hisham ya maidota. Dakyar Hajiya ta amince don ta ce ba hannunta idan Munir ya tambaya.
Suka kammala wayar ta mikawa Ramlat, bayan gama jin bayanin Hajiya ta amsa da toh kawai kafin ta wurgamata harara. Dariya A'isha ta yi tana kara nema afuwa.
***
Sai da suka idar da Magriba sannan suka hau saman dining table. Sai a sannan ne da Hisham ya matsa, Ramlat ta fito.
Bayansa kawai take hangowa don ya ba ƙofar ɗakin baya, ko kadan ba ta gane ko waye ba har ta ƙaraso da sallama.
"Haba ko kefa Antinmu, amma ace tun ɗazu sai kiranki ake kina togewa."
Murmushi kawai ta yi jin kalaman Hisham, shi kuwa Hussein jin an ce Anti yasa ya tsammaci wata babba ce don haka ya ɗago ya dubeta da zummar gaisuwa. Yanda bakinta ya tsaya a bude haka na shi ya dakata, mamaki ne a saman fuskar kowannensu.
'Wannan matar ko dagasken dai mayya ce?' Fadin Hussein a zuciyarsa cikin son gasƙata abinda matarsa ta hasaso a kan Ramlat. Mamakin yawan haɗuwartasu yake. Ta kai har ya ganeta, kamanninta sun yi zaman dirshan a ƙwaƙwalwarsa.
Toh haka itama Ramlat, haduwarsu na ba ta mamaki. Da kuma ace ta san shi ne baƙon, da har ya fita ba za ta yarda ta fito ba.
"Kun sa juna ne?" Tambayar Hisham ya katse kallon ƙurillar da suka tafi yiwa juna, kusan a tare suka kauda kai, ta ƙaraso ta maze ta zauna kujerar dake kallonsa. A'isha da Hisham dai abin mamaki ya basu, yanayin sauyawar kowannensu.
"Ina wuni, an zo lafiya?"
Ta gaisheshi cikin dakiya da kuma son kauda zargi daga zuƙatan ma'auratan da suka zubamusu ido.
Shima ya amsa a tausashe.
"Lafiya."
"Wai ba za ku amsamin ba, kun san juna ne dama?"
Hisham mai naci, ya ƙara neman ba'asi. Hussein ya dubeshi da dara-daran idanunsa yana dan murmushi.
"No, yau ne ma farkon ganin da na yi mata."
Ta dubeshi da sauri, itama ita din ya kalla har lokacin murmushinsa bai gushe ba. Me yake nufi da yau ya