Showing 141001 words to 144000 words out of 226732 words

Chapter 48 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12461

yana shigar da wasu takardu don son kauda damuwar da ke sukarsa a ƙirji.

"London nake son mu je, ka ga daga nan sai a binciki lafiyata sosai akan matsalar haihuwa. Kana iya ɗaukar annual leave."

Ta fadi cikin dabara tana mai kissimawa a ranta shikenan Hussein ya yi bankwana da Nijeriya har abada.

Ba tare da ya kalleta ba ya amsa a gaggauce.

"Ki yi duk yanda ki ka so."

Yana kaiwa nan ya miƙe ya nufi sama. Ba ta dakatar da shi ba don ita fa ya gama biyanta. Da wani irin farin ciki ta kira Hajiya Batool ta fesamata. Dariya suka yi lokaci guda.

"Habawa! Wa ya faɗamasa Borno gabas ta ke? Ai wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa."

Cikin nishaɗi Hajiya Zeenatu ta gyara zama.

"Allah Ya barmin aminiyar kwarai. Yanzu ki yiwa ɗanmu magana ina so ya yimin duk wani shiri na tafiya."

Suka yi dariya sannan suka ci gaba da ƙulla-ƙullarsu.

***
Kasa zama ya yi sai kwanciya, kwanciyar ma bai fi minti uku ba ya miƙe zaune gami da dafe kai. A hayyacinsa ya amincewa Hajiya Zeenatu, gani yake nisan da zai yi daga gareta shi zai sa ya mance da dukkan lamuranta. Hisham ba zai yi ƙarya ba don ya baƙanta ransa hakanan kawai, a farko yana mata kallon wata halitta ɗaya tallin tal da ta dakatar da shi daga biyewa Hajiya Zeenatu tun farko akan su bar garin, yau kam har Ƙasar ya amince su bari idan hakan zai ba shi farin ciki. Zai nisantashi da ita kuma ya yaye damuwarsa. To wa ya ke da shi da zai damu? Ba shi da uwa bare uba, ba danginsa babu na Hajiya Zeenatu. Wannan abu sau da dama kan ɗauremasa kai matuƙa kuma ya jefashi cikin tafkin tunani iri-iri. Nan da nan farar fuskarsa ta yi ja kamar yanda idanun suka kaɗa. Ya riƙe kansa da ke sarawa da ƙarfi yana salati. Tun yana gani daidai har ya dawo gani dishi-dishi. Ya yi kokarin mikewa tsaye sai ji kake tim! Ya fadi.

Ta turo ƙofar ta shigo ranta fari sol bayan kammala wayarta da Hajiya Batool. Turus ta yi ganin Hussein a ƙasa. Wani ƙara ta saki kafin da sauri ta nufeshi.

"Hussein! Hussein?!"

Babu alamar zai motsa, don haka ta dauko ruwa ta yayyafa, nan ma shiru. Ganin haka ta yi wurgi da robar ruwan ya malale a kafet ta fita daga dakin.

"John! John! Ola!"

Kusan lokaci guda ma'aikatan dake kicin har wajen su uku suka fito.

"Yes Ma!"

Umarni ta ba su akan su hayo su taimakamata. Da gudu suka nufi saman, suka cicciɓi Hussein. Mayafi kawai ta dauka sai mukullin mota da ta damkawa John ta bi bayansu tana kuka. Kai tsaye suka wuce asibiti.

***
Sun sauka lafiya a Kano. Bayan kimtsawa suka hadu suka ci abincin rana. Fuskar Ramlat cike da fara'a don  tun safe bayan dawowarsu Muhibbat ta kawo su Ummi. Affan ya maƙale mata duk inda ta sa ƙafa yana biye. Labarin gidan su Aliyu da na Muhibbat kuwa ta sha har ta gode Allah. Ta lura dai ba su fuskanci kowace matsala daga dangin Aliyu ba don a yanda bakin Ummi ba ya shiru sai ta fesamata.

Da yammacin ranar gidan ya rage daga ita sai Hajiya da su Ansar don tuni masu auren duk sun tafi gidajensu. Ta shirya tsaf da niyyar zuwa ganin Kawu Modibbo kafin zuwan AlHassan wanda tun safe ya shaidamata cewar yana hanya. Ba ta ɓoyewa Hajiya komai ba na halin da ake ciki. Hajiya ta jinjina lamarin.

"Ramlatu Allah Yasa a dace. Allah Yasa karshen wahalar yaron nan ce ta zo."

Cike da tausayawa Ramlat ta amsa da amin. Suka yi sallama ta fita, ba ta ɗauki mota ba don haka kawai ta fice. Har za ta wuce ta ga kyautuwar leƙawa gidansu Amrah su gaisa da Baba Dakta. Wannan yasa ta karya kwana ta shiga gidan da sallama.

Umma ta amsa fuska a sake.

"Mutanen Daura, saukar yaushe?"

Dariya ta yi tana mai kama hannun Zaituna da ta maƙalƙaleta tana oyoyo.

"Tun safe muka iso, Hajiya ma ta kira ba kya kusa."

Umman Amrah ta bude baki.

"Af, an yi haka. Na ga kiranta toh da alama dai wannan ɗiyartaki ce garin son a kunna mata kallo ta kashemin ƙarar."

Murmushi sosai Ramlat ta yi gami da shafa kan Zaituna tana mitar yanda amosali ke cinyemata gashin.  Can kuma ta ɗago.

"Baba Dakta ya na nan kuwa?"

"Ba ki taki sa'a ba Ramlatu, yana asibiti."

Ta mike tsaye.

"Toh Umma zan dawo anjima in sha Allah. Zan ɗan fita ne."

Umma ta amsa da toh, suka yi sallama  ta fice.

***
  Gidan ta tsaya tana ƙarewa kallo. Gida ne da ta sha zuwa ta wuceshi, ba ta mancewa akwai sadda suka taɓa shiga tun suna yara ita da su Amrah tsinko mangwaro aka koro su. Murmushi ta ɗan yi tunawa da cewar gidan ƴan uwan mutum mafi soyuwa a zuciyarta ne ashe. Ta ƙarasa ta yi sallama ga mazauna ƙofar gidan sannan ta sa kai ciki. Ɓangare biyu ta gani sai kawai ta faɗa na biyun. Wata baiwar Allah dattijuwa ta soma cin karo da ita zaune a tsakar gida, a gefenta wata budurwa tana gyaran alayyahu, wanda nan take ta gane fuskarta dalilin hotunanta da ta ke gani a status din Hafsat, sunan ne dai ba ta jin za ta iya tunawa.
Suka amsa sallamarta suna dubanta, duba na rashin sani.

"Sannu da zuwa, bismillah. Rasheeda kai ta falo ina zuwa. " Faɗin Amarya fuska a ɗan sake, sosai Ramlat ta ji dadin tarbar da ta samu. Ta bi bayan budurwar da aka kira Rasheeda zuwa falo. Falo ne mai girma ya sha ado. Ta zauna a saman ɗaya daga cikin hadaddun kujerun da aka zuba. Rasheeda ta gaidata ta amsa fuska a sake sannan ta je ta kawomata ruwa da lemun zoɓo.

"Na gode." Cewar Ramlat sadda ta dauki ledar ruwan ta sha kaɗan ta ajiye ragowa. Amarya ta shigo ta zauna. A ladabce Ramlat ta gaidata ta amsa fuska a sake.

"Sai dai kamar ban shaida fuskar ba."

Murmushi Ramlat ta yi.

"Eh gaskiya ba ki san ni ba Anti. Sunana Ramlat Khalid Mu'azzam. Kusan sanadin AlHassan Aminu Mamman dake Adamawa na san gidannan. Kwanakin baya ma sun zo biki nan suka biya ta gidanmu."

Kawai sai ta ga Rasheeda ta sa dariya haka Amarya.

"Ke ce Mamin Fatima ko? Mai zaɓamata takalmi? Ya bamu labari."

Da wani irin salama na jin dadin kalaman Rasheeda itama ta yi dariyar kadan.

"Ni ce, ai kema ina ganinki na shaidaki don ina yawan ganin hotonki a status din Hafsat."

Jin haka Amarya sai ta samu nutsuwa sosai da Ramlat, dama tun farko ba ta yi mata kalar mace marar kamun kai ba. Nan aka kara gaisawa da tambayar su Hajiya wanda ba karamin mamaki ya ba Ramlat ba. A karshe Ramlat ta gangaro kan abinda ya kawo ta.

"Ina neman izni ne, ina son ganin Kawu Modibbo."

Jin haka Anti Amarya ta amsa cikin kwarin gwuiwa.

"Wannan ba matsala ba ce Ramlat. Bari na yi miki iso, ina zuwa."

Hakan ya faranta ran Ramlat, ta dauka ganinnasa zai mata wuya ko kuma wani ko wata zai nemi sanin dalilinta na son ganinsa, sai dai akasin hakan ce ta faru. Ko ba komai ta gaskata kirki na Amarya, wanda ya sha bamban da na Hajja Fatuma kamar yanda ta ɗan ji kaɗan cikin labarin matannasa a bakin Hafsat. Yarinyar akwai hira idan ta so.

Jim kaɗan sai ga Amarya ta dawo, yanayin sanyin jikinta sai ya sa Ramlat shan jinin jikinta itama. Amarya ta daure tana murmushi mai kama da yaƙe.

"Za ki iya jira har bayan Magriba kuwa? Ina gudun kar ki dare."

Nan ta gano matsalar, don haka ta saki fuska.

"Lah ba komai Anti, Allah Ya kaimu."

Amarya ta yi murna da hakan, ta kunnamata kallo ta ba ta remote koda za ta sauya tasha daga nan ita kuma ta koma bakin aiki kasancewar girkinta ne. Ba jimawa da kunna kallon aka dauke wuta, nan take jin Amarya na ba Rasheeda labarin wai Hajja Fatuma ce ta ce tunda ba lokacinta ba ne sai ta yi hakuri da duk wani baƙonta da ke son ganin Modibbo, idan na ta lokacin ya shigo ta yi duk irin damun da ta so yiwa furarta.

Murmushi Ramlat ta yi na yaƙe, ta dai lura akwai takun saƙa tsakanin matan gida. Waya ta fiddo ta kira Hajiya ta fadamata.

"Anya kya zaunar musu har Magriba? Ba kya dawo ba ki hakura zuwa gobe?"

Girgiza kai Ramlat ta yi.

"Hajiya lokaci zai ƙuremin idan ya kai gobe, mu dai yi hakuri tunda kinga biyar da rabi ma ta wuce, kamar yanzu ne za'a kira sallar in sha Allah."

"Ai shikenan, Allah Ya kaimu anjima. Sai kin dawo."

Ta amsa da amin suka yi sallama. Ba ta kai ga ajiye wayar ba, kiran AlHassan ya shigo. Suka gaisa.

"Dole ta tsayar da ni a Gombe sakamakon lalacewar abin hawa. Na so kwarai na shigo yau, amma gobe da sassafe in sha Allahu zan taso."

Hakan ya dan yiwa Ramlat dadi, ko ba komai lamuran zasu tafi yanda ta so.

"Ayya ba komai, Allah Yasa hakan ya zama alheri."

"Amin, sai dai kin ƙi sanar da ni komai game da abinda na nema."

Sauke ajiyar zuciya ta yi.

"Ka yi hakuri, idan ka shigo har wanda zai ba ka mamaki duk zan faɗamaka kuma zan kaika ka ganewa idonka in sha Allahu."

Ya dan yi shiru, shirun da yasa Hussein faɗomata a rai, shi ya saba yi mata hakan. Kewar Hussein sosai ta ke ji ta kuma kudurce ko bai mata magana ba ita kam yau za ta taɓoshi ta whatsapp.

"Shikenan. Allah Ya jisshemu alheri."

Ta amsa da amin cike da tausayinsa. Dan uwan da Allah kadai yasan tun sadda ya ke bulayin neman ɗan uwansa. Ta ji idanunta sun cika da kwalla daidai sadda suka yi sallama. Ta shiga whatsapp ta aikawa Hussein saƙo, ta jima tana kallon profile dinsa wanda bai dora komai ba a idanunta tana wassafo hotonsa, karshe ta sauka.
Ba jimawa aka shiga kiraye-kirayen sallah, Rasheedat ta jagorance ta zuwa ɗakinta. Alwala ta ɗaura ta tayar da sallah saman dardumar da ta iske an shimfidamata.

Ta jima tana addu'ar nasara akan lamarin Hussein, shi kansa ta yi mishi addu'a kwarai kafin ta shafa ta miƙe.
Abinci aka zubomata, dolenta ta ci tana kallon tsarin yaran Amarya gwanin sha'awa. An idar da sallah ana kuma neman haddar karatun da aka biya na Islamiyya. Can kuma sai ga Amaryar ta fito sharr kamar sabuwa, ta shirya cikin riga da siket na leshi ta cakare abinta tsaf. Da fara'arta ta dubi Ramlat.

"Yi hakuri fa Ramlatu, bari idan na shiga zan miki magana sai ki zo."

"Toh Anti. Kin yi kyau tubarakAllah."

Hakan da ta fada ya ba su dariya har yaran. Amarya ta yi godiya ta wuce ɓangaren Mijinta. Sosai abin ya ƙayatar da Ramlat.

***
  Taimakon gaggawa likitocin suka shiga ba Hussein har Allah Yasa ya dawo hayyacinsa. Hajiya Zeenatu ta rasa sukuni, banda safa da marwa babu abinda ta ke yi a harabar bakin kofar dakin da Hussein ke kwance. Can ɗaya daga cikin likitocin ya fito, da hanzari har mayafin na sulalewa ta ƙarasa.

"Dakta ya farfado?"

Daktan ya yi murmushi gami da gyara zaman gilashinsa.

"Alhamdulillah Hajiya, ɗanki ya farfaɗo, ki kwantar da hankalinki."

Ta tamke fuska.

"Mijina ne."

Mamaki karara a fuskar likitan kafin kuma ya haɗiye don ba abinda ya shafeshi ba ne.

"Ok, idan ba damuwa ki biyo ni zuwa ofis."

Daga haka ya yi gaba.

"Matsalar Hussein damuwa ce da ta haddasa masa ciwon kai mai tsanani. Sai jininsa da ya hau, sai kin kula sosai da cimarsa har ma da walwalarsa domin irin ciwonsa na bukatar kulawa kuma ba ya son yawan tunani."

Hajiya Zeenat ta yi shiru a ranta tana jin takaicin Hussein da zai  sa damuwar wani abu bayan ita ce duniyarsa.

"Kin ji abinda na ce?"

Tambayar ta katse tunaninta. Ajiyar zuciya ta saki.

"Naji kuma zan kiyaye. Yanzu ina iya ganinsa?"

Likita na ƙaremata kallo ya gyada kai.

"Eh Hajjaju."

Ta mike tana watsa masa kallo mai kama da harara, ba shiri ya janye idanunsa tunda ya san shi ya jaza wa kansa da ya bita da kallon kurilla. Ba kuma don sha'awa ba, sai don ya ga abinda ya kwaɗaitar da mara lafiyarsu da ta kira da Hussein har ya ji ita ya ke da muradin zama abokiyar rayuwarsa.

"Su ta shafa." Ya ƙarƙare tunanin ta hanyar furta hakan a fili.

Hajiya Zeenatu ta shiga ɗakin da Hussein yake, wannan karon babu kowa sai shi ɗaya. Idanunsa a lumshe, a farko ta yi zaton bacci ya ke, sai dai rufe ƙofar da ta yi yasa shi kallonta. Ta sakarmasa murmushi tana mai ƙarasowa ta zauna gefen gadon ta kama hannunsa.

"Sannu Hussein, ya jikin?"

Gyadamata kai kawai ya yi ya kara kauda kansa.

"Ba zan kwana a nan ba, su sallame mu."

Yanda ya yi zancen ka san iyakar gaskiyar kenan ba wasa. Cikin rarrashi ta shigo kokarin fahimtar da shi kuskuren hakan, sai dai yanda ta kafe haka ya kafe har abin ya tsorata ta. Aikuwa dai karshe sai sallamar aka ba su da lodin mgunguna bayan an ƙara jaddada masa akan ya kula sosai da jikinsa.

Su na komawa gida ma'aikatan suka tarbeshi tare da yi mishi sannu.

"Dalla Malamai ku matsa! Ba kwa ganin yanayin jikinsa ne?"

Hussein ya dubi Hajiya Zeenat, a fuskarsa ta gane bai ji dadin abinda ta yi ba. Ya tsaya ya amsa gaisuwarsu ita kuwa ta yi gaba tana tsaki. Godiya ya yi musu san nan ya shige ya bar su da gulmarta.

Sallar Magriba ya soma yi san nan ya shiga wanka. Yana fitowa ya kimtsa, Hajiya Zeenatu kuwa tana ƙasa ta na bada umarnin abinda za'a girkawa mijinnata.

Ya dauki wayarsa, ya ga missedcalls din Hisham sai kuma na wani abokin aikinsa. Data ya kunna ya leƙa whatsapp. Shiru ya yi ya ƙurawa sunanta idanu yana kallon saƙon da ta aiko ba tare da ya buɗe ba, ya hangi dai sallama da gaisuwa, sauran ne bai da masaniya. A hankali aka zare wayar daga hannunsa. Hajiya Zeenatu ce, gabansa ya faɗi.

"Haba Yallaɓai, yaushe ma ka farfaɗo da za ka ɗauki waya? Ba dai ka manta sharuɗɗan Dakta ba?"

Ta ƙarashe tana duban wayar, tuni ta shiga key, shima yanda ta ke kallo haka ya ke kalla, ganin ta rufe ya sanya shi sauke ajiyar zuciya. Gaba daya ta kashe wayar tana mai duban soyayy duk a kokarinta na gudun kar ya sauya shawarar da ta kawomasa a ɗazun.

"Wayar a hakura a bar ta zuwa gobe. Yanzu mu je ƙasa ka jira abinci sai ka sha magani."

Ta faɗi gami da riƙe hannunsa. Ya ciji leɓɓansa, haka nan ya ji bai kyauta ba bisa rashin ba da amsa ga Ramlat sai dai maganganun Hisham na faɗomasa a rai sai ya yi gaggawar fidda tunanin.

***
Mintuna kusan goma sha biyar sai ga kiran Amarya a wayar Rasheedat.

"Muje na yi miki rakiya."

Haka kawai Ramlat ta ji faɗuwar gaba, ta amsa da toh tana mai haɗiyar yawu mai ɗaci.

Da sallamarta ta sa ƙafa a falon. Dattijo cikin shigar kamala, kana ganinsa ka ga cikakken bafulatani. Tundata shigo yake yiwa fuskarta kallon tsanaki don son tantance ko akwai inda ya santa ko kuwa yau ne farkon ganinsa da ita. Ta karasa ta gaishe shi, Amarya tuni ta mike zuwa ɗaki. Hakan kan faru, idan har Modibbo nada baƙo, sukan ba shi wuri ya gana da ita.

"Baiwar Allah daga ina?"

Ya tambaya cikin hausarsa da har sannan ba ta ginu kamar ta Bahaushe ba.

Ta hadiyi miyau gami da ambaton Allah. Ta gabatar da kanta sannan ta ɗora bayan ya shaidamata eh ya san Malam Abdullahi kakanta kuma ɗan unguwar da yake, Yakasai.

"Kawu dama magana ce da ta danganci Hussein, dan uwan AlHassan da ake nema."

Shiru-shiru, ba ta ji ya ce uffan ba don haka ta ɗago kai. Yanayin dake shimfiɗe a fuskarsa ya tsorata ta, ya kuma kaɗa hanjin cikinta.

"Kina da labarinsa? Ke wace ce?"

Wannan ne tambayoyin da ta samu da suka ƙara cilla ta a kogin tunani da mamaki.[3/16, 1:55 PM] +234 703 629 0938: I just published "BABI NA ARBA'IN DA BIYAR" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/gqyFr6qwCcb




🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

45)

ALLURA TA TONO GARMA...



"Kurma ki ka koma?"

Ta  dawo hayyacinta ta kalle shi gami da girgiza kai. To me za ta ce bayan ta gabatarmasa da kanta?

"Ina gargaɗinki da ki cire kanki a abinda bai shafeki ba. Idan kina son tsira da lafiyar kwakwalwa da na gangar jikinki ki fita hanyar Hussein da Zeenatu."

Da wani irin razana ta dubeshi, wannan ƴar fara'ar dama tun soma labarin ya kauda ita a saman fuskarsa sai ya zama kamar wani Mugyambo a idanunta. Kwallar da ta cika kurmin idanun suka soma sharara.

"Ka...ka..san Hussein yana nan? Ban ambaci Zeenatu ba, ka san..."

"Ke Bingel! (Yarinya). Ke wacece da za ki tuhume ni? Ina gargadinki karo na biyu kuma na ƙarshe ki tashi ki binne maganarnan a nan wurin da kike zaune. Idan ba ki ƙi ji ba, ba kya ƙi gani ba. Duk abinda ya faru gareki sanadin fasa wannan zancen, ki yi kuka da kanki!"

Ramlat kirjinta na bugu, hawayenta na kwaranya, kwakwalwar ta tsaya cak ta bar aiki. Ta kasa haɗa kowane lissafi, jin ta take yi kamar ba'a duniyar mutane ba. Kamar wata duniyar ta daban ta ke ciki mai tsananin ruɗani da azaba. Kallonsa ta ƙara yi, girman tuni ya zube ƙasa warwas! Kallo ne kamar wacce ke zaune gaban sa'anta.

"Ka na da hannu a komai? Ka na a ɓatar da Hussein daga zuri'arku? Me ya yi maka haka da zafi?"

"Kina ƙara dulmiyar da kanki cikin tafkin nadama da da na sani, kalaman da kike yi za su rushe duk wani farin ciki na rayuwarki. Ki kama kanki! Ki tashi ki bar min gida tun kina da sauran lafiyar aikata hakan!"

Miƙewa ta yi a sanyaye, har za ta fice ta juyo ta dubeshi yana faman muzurai. Dattijon da bai kama daraja da girmansa ba, babu amfanin ganin ƙimarsa.

"Kawu ka sani, Allah na bayan masu gaskiya. Ƙarya fure ta ke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login