Showing 156001 words to 159000 words out of 226732 words

Chapter 53 - KARFEN KAFA complete hausa novel

Unknown   

11 Oct 2024

12466

da ma ƴan gidanku. Don haka zaɓi ya rage naki, na baki nan da awanni biyu, duk abinda kika yanke ki kira ki sanarmin. Kar ki manta rayuwarki a tafin hannuna yake."

'Ƙarya kike, Allah ne Mai iko da rayuwakanmu.' Nos Khadija ta fadi a fili don ba ta jin tana da kwarin gwuiwar faɗa a zahiri. Ta gyada kai kawai a fili, ta karɓi kudin ba don ta so ba ta zura a aljihun wandonta.

"Ina tsumayenki. Ga lambar wayata." Hajiya Zeenatu ta fadi karo na biyu tana miƙamata karamin complimentary card mai dauke da numbobin wayoyinta a jiki. Nan ma Khadija gyada kai ta yi.

"Je ki." Ta ba ta umarni, ta juya da sauri ta shige ciki har tana cin karo da wata mai tsohon ciki.

"Yi hakuri don Allah." Matar ta bita da kallo kawai gami da jan tsaki irin na masifaffun masu ciki. Haka ta wuce ta a mita.

Koda ta karasa dakin Nurses, ba ta tarar da kowa ba don haka da sauri ta ciro kudaden hannu na rawa ta cusa a jaka ta zuge zif. Bandaki ta shige ta soma watsawa fuskarta ruwa tana salati a ƙasan ranta. Yau da wane rashin sa'a ta fito daga gida? Kawai sai ta shiga hawaye, nutsastsiyar fuskar Ramlatu da kuma na Hajiya mai cike da dattako da kamala take tunawa. Ta ya ya? Ta wace hanyar za ta iya kashe wannan baiwar Allahn? Duk da dai idan ta so abu ne mafi sauki a aikinta, za ta iya kasheta irin kisar da zai yi wuya kafin a gane ita ce silarsa. Amma ina! Ba'a ba ta wannan tarbiyyar ba kuma ita ba haɗamammiya ba ce akan abin duniya. Kaɗan ma da ta ke samu ya wadatar da ita.

Sai da aka kwankwasa ƙofar sannan ta fito. Karo suka yi da Nos Jamila. Ta bita da kallo.

"Dije, lafiya?"

Murmushin yaƙe ta yi ta hau murza idanu.

"Ba komai, abu ne ya faɗa idanuna."

"Aa Dije, faɗamin gaskiya."

Girgiza kai ta yi, ba za ta iya ba, tana tsoron abinda zai sanadin rayuwarta.

"Ko haihuwar ki ka karɓa, don nasan halinki na tausayi."

Dariya ta ba ta.

"Oh na tuna, ashe fa ba duty naki bane yau." Cewar Nos Jamila karo na biyu.

Ita dai Khadija ta sulale ta fice daga ɗakin. Maganin ma kasa komawa ta ba Ramlat ta yi sai wata ta aika.

***
Hussein da AlHassan zaune a falon gidan Hisham suna cin lafiyayyen girkin Aisha. Gogan ci yake kamar an mishi dole.

"Wai Hussein lafiya? Ko kaima jinyar kake taya Ramlat?"

AlHassan ya fadi yana murmushi don tuni ya ɗago shi.

"Mene haɗina da ita? Kawai dai na damu da harbin ne, na kuma rasa waye zai yi ƙarya da ni ya harbe ta. Shiyasa na kasa fahimtar mai laifin, me ya sani tsakanina da ita da ya zaɓi hanyar kasheta ta amfani da ni."

"Da mamaki kam, amma ko ma mene in sha Allah nan ba da jimawa ba zai bayyana. Har wanda ake ɓoyemana."

Hisham ya furta yana kashe mishi io ɗaya, AlHassan ya yi kamar bai gansu ba ya ci gaba da kai loma yana murmushi. A yau jinsa yake kamar a duniyar gajimare tsabar murnar ganinsa zaune tare da ɗan uwansa.

Hussein din ma banda harara bai cewa Hisham uffan ba, saboda gudun zargin sai ya saki jiki ya ci abinci. Bayan sun kammala ya mike.

"Ina zuwa?"

Fadin AlHassan don ba ya son ya ji Hussein din ya matsa daga gareshi. Murmushi Hussein ya yi.

"Gidan Hajiya Zeenatu."

"Aa, bai kamata ka je kai kaɗai ba. Muje tare."

Jinjina kai Hussein ya yi cikin amincewa da zancen dan uwannasa. Suka ɗunguma suka fita, Hisham ya takamusu har ƙofa kafin ya dawo ciki. Kusan shima yau dai jinsa yake sak. Babu sauran damuwa.

***
RAMIN ƘARYA....
[3/16, 1:55 PM] +234 703 629 0938: I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/IRx4QB4kMcb


🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

48)


Kallonsa yake yi sosai kirjinsa na bugawa da sauri. Ramlat ta runtse idanu tana mai addu'ar komai ya tafi daidai.

Da wani irin sassarfa AlHassan ya tako ya rungume Hussein kawai sai ya soma kuka.

"Hussein." Ya ƙara kiran sunansa karo na biyu, Hussein ya yi ɗif sai hawaye da ke zuba saman fuskarsa. Ji ya yi kamar ana saramasa guduma a tsakiyar kansa, a hankali ya soma ganin dishi-dishi, lokaci guda idanunsa suka juye yayinda baƙin kwayar idanun ta ɓace ɓat. Hisham da ke tsaye a baya shi ya lura da sauri ya karasa ya rike Hussein. Jikinsa wani irin kakkarwa ya ke yi.

"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!"

Cewa Hisham yana rike hannun Hussein, jin haka AlHassan ya ɗago wanda saura kiris Hussein din ya zube don kuwa da jikinsa ya samu madafa.

"Riƙe shi sosai." Cewar Hisham, suka taimaka suka fitar da shi sai wurin likita. Ramlat tuni ta miƙe tsaye. Su kansu su Hajiya sun rude. Ganin tana kokarin ficewa yasa Rafee'ah riƙo ta.

"Ina za ki je? Ba ki ganin halin da ki ke ciki? Idan kin je lafiya za ki ba shi?"

Ta girgiza kai tana hawaye, ta bude baki sai dai ta rasa me za ta ce don haka ta koma ta zauna. Hajiya ce ya fidda waya don ta kira Malam ta sanarmasa halin da ake ciki. Nan take ya ce maza ta aiko a karɓi ruwan da ya haɗa da ganyen magarya ya yi addu'o'in karyewar sihiri. Ba shiri ta yiwa direbanta waya ta ce ya biya Yakasai ya karɓo mata saƙo.

***
  Duk iyakar awon da likitocin su ka yi ba su gano komai game da ciwon Hussein ba. Don haka koda suka samu ya bar jijjigar, idanun suka dawo daidai sai Likitan da ya karɓi Hussein ya fito wurin su AlHassan. Suka tarbe shi da gaggawa.

"Ku yi hakuri.."

"Mutuwa ya yi?" Faɗin AlHassan a gigice, girgiza kai Likitan ya yi yana mai riƙe hannunsa.

"Ko kusa ba haka ba ne, asalima yanzu mun samu komai ya daidaita. Sai dai hakikanin gaskiya ba za mu ce ga abinda ya jawomasa hakan ba, yanzu dai halin da ake ciki, dole zamu yi mishi tests don mu gano ainahin inda matsalar take."

Suka jinjina kai.

"Ba damuwa Dakta. Allah Ya ba shi lafiya." Cewar Hisham da hankalinsa ya ɗan kwanta.

Bayan wucewar Dakta ya dafa kafaɗar AlHassan wanda ya cire hular kansa tsabar gumin da fargaba ta haifarmasa.

"Kada ka damu ɗan uwa, na fadamaka dama duk sadda maganar dangi ko ƴan uwa ta haɗa mu da Hussein ya kan shiga wani irin hali, ina kuma ga yau ya yi ido huɗu da ɗan uwansa?"

"Hakane, sai nake ganin kamar ba na asibiti ba ne."

AlHassan ya faɗi bayan kai karshen nazarinsa.

"Hisham, ya jikinnasa?"

Suka juya, Rafee'ah ce. Ta karaso suka yi mata bayani.

"Allah Ya ba shi lafiya. Kada ku damu, Hajiya ta aika a karɓo ruwan ganyen magarya mai addu'o'in karya sihiri, da yardar Allah komai zai daidaita."

AlHassan ya sauke ajiyar zuciya yana ɗan murmushin jin dadi da wani irin kaunar zuri'ar da ke kara mamaye zuciyarsa.

"Na gode kwarai, Allah Ya sakamaku da alheri. Allah Ya bar zumunci."

Ta yi dariya kadan.

"Ameen. Ai yiwa kai ne. Bari na koma, dama Hajiya ce ta ce na sanarmaku sannan na gano halin da yake ciki don marar lafiyarmu ta tashi hankalinta sai kuka ta ke yi."

Murmushi AlHassan ya yi yana mai hasashen wani abu da tun a jiya ya yi zaman dirshan a kwakwalwarsa.

***
TA FARU TA ƘARE...

"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Halimar aka kama?!"

Hajiya Zeenatu ta faɗi tana tsaye a bakin ƙofar gidan Kakar Halima wacce ke rike da ita. Ƙanin Halima uwa daya uba ɗaya wanda daga ita sai  shi, su uku iyayensu suka haifa kafin rasuwarsu, dayayar Halima, Halima sai Yusufa. Kakarsu ta karɓi riƙo. Yusufan ya share hawaye yana duban Hajiya Zeenatu.

"Wallahi ranki ya daɗe, ɗazu aka yi mana waya, naje har ofishin ƴan sandan na sami Aunty Halima, wai dumu-dumu aka kama ta da bindiga za ta yi kisa. Wannan abu ne da ko a mafarki ba mu zaci faruwarsa ba. Su biyu aka kama, shi ɗayan ko Gwaska ko wa? Yana asibiti. Yanzu Kaka na kwance ba lafiya tun da ta ji halin da ake ciki."

Hajiya Zeenatu wacce ta yi mutuwar tsaye, ta yi sauri ta dawo hayyacinta. Baki na rawa ta ce.

"Ta..ta..faɗi wadanda suka sanya ta?"

Kallon da Yusufa ya yi mata na nazari sai da ya sa ta sakin ƙaramar tusa mai haɗe da fitsari ba shiri. Ya girgiza kai.

"Abin kunya ne ace saboda ɗa namiji za ta aikata hakan. Kishi ne kawai don uban gidansu na aiki zai auri abokiyar aikinta Ramlat. Haka ta sanarmin."

Ya karashe da wani irin jin kunya. Ajiyar zuciya Hajiya Zeenatu ta sauke ta juya za ta shige mota.

"Amm..Hajiya, na ce sai dai ban sanki ba. Kema wurin aikinta ki ke ne?"

Ta juyo.

"Eh, tare muke aiki." Tana kaiwa nan ta juya da sauri ta faɗa mota, ta ja. Kiyayewar Ubangiji ce kawai ta isar da ita gidan Hajiya Batool. Itama nan ta iske ta su na dambe da surukarta. Dakyar ta raba su. Ɗan Hajiya Batool ba ya nan ya yi tafiya Dubai, shi ne surikar ta zo gidan kwana.

"Haba Hajiya, me ya yi maki zafi za ki tsaya dambe da suruka? Ke kuma don ba ki da kunya wannan ba uwar mijinki ba ce?"

Fareeda wacce ke tsaye tana huci ta narkawa Hajiya Zeenatu uwar harara kafin ta saki dariya gami da tafa hannu.

"Ahayye! Ai fa da yake daga ke har ita jirgi ɗaya ya kwaso ku dole ne ki ga laifina! Tsoffin banza da ba su riƙe girmansu ba ai ba zan ji kunyar taka su son rai ba. Kin tauye hakkin yaro kin danne kina zaune da shi! Ko an fadamaki bani da labarin mijinki? Kina kai min uwar miji yawon bin bokaye don mijina ya ƙara aure ko? To wallahi karyar ku domin tun kan a haifi uwar mai sabulu balbela ke da farin kai. Don haka idan ku na son na lulluɓe dukkan sirrikanku to ku tabbatar an fasa batun auren Mijina da kowace shegiyar kucaka. Idan kunne ya ji..." Ta ƙarashe da rike kunne kafin ta wuce tana dariya ta bar su baki galala. Bayan shigewarta ɗaki Batool ta yi gaba ta haye sama, Hajiya Zeenatu ta bi ta a baya. Su na shiga ɗaki suka sa mukulli.

"Batool akwai matsala!"

Hajiya Batool da ta zauna rike da ƙugu tana ambaton wash sakamakon cizon da ta sha a wurin Fareeda. Ta amsa wa Hajiya Zeenatu kamar za ta yi kuka.

"Matsala nima cikinsa kika tarar da ni Zeenatu. Kamar Gora yaudararmu ya ke yi yana cin dukiya a ɓagas. Ni na rasa kan wadannan lamuran."

Hajiya Zeenatu ta yarfar da jaka da mayafi, da sauri ta faɗa banɗaki. Can kuma ta fito ta zauna tana sharce gumi. Ta kora dukkan bayani ga Hajiya Batool gaba dayanta a rude.

"Ya zan yi ne Batool? Ga Visa ta yi wuya an ce mu kara hakuri zuwa sati na sama, ga wannan lamari na neman kwaɓemin? Ba mu ga ta zama ba Batool, ta inda aka hau dai ta nan ake sauka idan ba haka ba mai afkuwa za ta afku. Ba ni da tabbacin Halima ba za ta tonamana asiri ba. Ban san iyakar lokacin da za ta riƙe sirrinmu matsayin sirri ba. Wannan fa barazana ce garemu. Tashi za ki yi mu kama ƙafa muje mu ga Gora tun kafin komai ya lalace."

Hajiya Batool ta share hawayen takaici, yau ita suruka ke dambe da ita,  ta rantse sai ta ga bayanta tunda dama ba ta haifarmata ko ƴartsana ba sai afkin ci da kasayarwa.

"Muje. Bari na lallaɓa."

Ta miƙe dakyar ta dauki gyalenta. Suka fice. Fareeda na leƙensu ta window ta yi dariya ta saki labule. A fili ta ce.

"Munafukan banza, da alama an tafi yawon abinda aka saba. Zama daram ni Fareeda!"

Ta furta tana mai zama kan gado tana dariya.

***
  Tunda Hajiya Zeenatu ta sanarmasa da batun kama Halima ya gaza samun nutsuwa. Don haka ya kira Dada a waya karon farko. Hakan ba karamin mamaki ya ba ta ba don har sai da ta ce.

"Yaya lafiya dai ko?"

"Ah lafiya kalau mana Amina, ba damar na kira ki kenan sai idan babu ita? Mtsw. Ina yaran nan kuwa? Husseini? Yana gari?"

Dada ta amsa a sanyaye.

"Aa, ya shigo nan Kano wani uzuri na ma'aikatarsu, bai ƙaraso nan ba?"

Wani zufa ya karyowa Kawu a goshi, ya samu wuri ya zauna ɗabas! Sai ya ɓige da faɗan borin kunya.

"Ina na isa dama ya zo wurina? Ai ban isa ba! Kin koyawa yara tsanata da tsanar iyalina. Sai ki yi idan hakan zai haifarmaki da ɗa mai ido! Mu din dai mu ne nasu."

Daga haka ya katse wayar bai saurari ban haƙurin Dada ba. Miƙewa tsaye ya yi yana sunturi, ba zai yiwu ba. Babu abinda zai ruguza dukkan sirrinsa. Idan ya tabbata lamarin Hussein ne ya kawo AlHassan garin Kano kamar yanda Bokansa ya buga ƙasa ya bincikamasa, toh shakka babu komai ya rushe. Tonuwar asirinsa kamar jin kunyarsa ne a cikin dangi, ya san duk tsanar da sauran yan uwansa suka yiwa jinin Aminu da Amina (Dada), bai kai tsanar da ya yiwa HUSSEIN ba.

Ya dau waya ya dannawa Hajiya Zeenatu kira, haka ya yi ta ringing ba'a ɗaga ba, wannan yasa shi kasa zama ya fice daga gidan don ƙara tuntuɓar Bokansa karo na ba adadi.

***
Ya mike zaune dakyar daga saman gadon da yake kwance. A hankali ya dafe kai yana salati.

"Sannu Hussein, ka tashi?" Ya dubi mai maganar da sauri, shi dai wanda ya gani a ɗazun ne mai kama da shi. Ɗan uwansa da ya daina sanyawa a idanu shekara da shekaru. Ƙuri ya yi mishi da idanu, daidai nan Hisham ya miƙamasa kofin ruwan tofi.

"Shanye duka please." Ba musu ya karɓa ya shanye tas. Kamar yanda jini ke zagaye a cikin jiki, haka ya dinga jin ruwan na zaga dukkan wata gaɓɓa ta jikinsa, a hankali hawayen da suka sauya kalar kwayoyin idanunsa suka samu damar kwaranyowa saman kuncinsa. AlHassan ya taso ya zauna a gefe gami da sanya hannu cikin nasa.

"Hussein, ka gane ni?"

Gyada kai kawai yake yi bakin na rawa amma kalmar A ta kasa fita daga bakinsa. Kawai sai ya ɗora hannunsa haɗe da na AlHassan saman goshi ya shiga kuka kamar ransa zai fita. Hisham a hankali ya juya ya fita daga ɗakin yana share kwallar dake kokarin zubowa a kokarinsa na katse ta yana mai hamdala ga Mahaliccin Sammai da kuma Ƙassai.

"Na gane ka. AlHassan Aminu Gidado."

Hussein ya furta da kakkarwar murya, jin haka AlHassan ya ƙara jan sa a jiki shima yana kukan. Zai so ace Dada na zaune a dakinnan, matar da idanunta ba su taɓa kafewa da zubar hawayen rashin Hussein ba. Kullum kiranta, amanar Allah ne su din a hannunta, koyaushe ɗorawa kanta laifin ɓatan Hussein ta ke yi.

"Ina Daa...da, Baba Naziru.?"

Hussein ya tambaya, AlHassan ya ɗago fuskarsa da wani irin murmushi mai haɗe da dariya-dariya.

"Dada tana nan, tana nan kullum cikin kuka da addu'ar Allah Ya nunamata kai. Babban burinta ta samu wani ko wata da zai kawomata kai koda labarin mutuwarka ne, ita dai ta san cewa ka mutu cikin musulunci kuma an maka kyakkyawan sutura. Da yawa ya faru bayan gushewarka Hussein, abubuda da dama sun faru garemu da baki bai isa ya buɗamaka su ba."

Hussein ya jinjina kai yana jan hanci.

"Eh, da yawa ya faru. Irin yawan da ban taɓa kawo wa kaina a rayuwa ba. Ban sani ba ko ni na jazawa kaina ko kuwa dai.."

Rufemasa baki AlHassan ya yi yana girgiza kai.

"Kar ka ce komai ɗan uwana, ka yi shiru mu ƙara godewa Allah da ganin wannan ranar da muka kwashe shekaru muna jira. Haɗuwa da Ramlatu alheri ne garemu baki ɗaya. Ina zan manta da ita da zuri'arta?"

Hussein ya ci gaba da dubansa da idanunsa da suka kaɗa. A idanun AlHassan ya gano karin bayani ɗan uwannasa ke nema. Murmushi ya yi.

"Mai hali ba ya fasa halinsa, ashe ba ka sauya ba?"

Suka yi dariya gami da ƙara rungume hannun juna gam! Kamar ance ga wani abu zai ƙara raba su. Tirya -tiryan ya ba shi labari tun daga haɗuwarsa da Ramlat har zuwa yanzu da aka harbe ta sanadinsa. Hussein ya yi shiru, ya rasa me zai ce. Ya kuma rasa wane yanayi ya ke ciki, tunani sosai ke neman shigarsa don haka ya gaggauta yanke tunanin.

"Mu je na ganta don Allah."

Ba musu suka mike, ya zura takalmansa, bini-bini za su kalli juna shi da ɗan uwansa su yi murmushi, haka suka jera idanun jama'a a kansu don ba karamin burge su suka yi ba musamman masu juna biyu, nan suka fara addu'ar su ma Allah Ya basu ƴan biyu masu bala'in kama irinsu, su gan su sun girma haka tare.

***
 
Gora ya duba, ya ƙara buga ƙasa ya duba, ya ɗago kai ya kalli Hajiya Zeenatu da Hajiya Batool da ke zaune gabansa cike da wani fargaba da tsoro.

"Lafiya dai?" Zeenatu ta nemi sani.

Ya girgiza kai ya ƙara maida hankali ya yi buge-buge da rubuce-rubucensa. Can ya ɗago ya dubesu yana sharce gumi.

"Bana jin akwai sauran duhu da yanzu haske bai mamayeshi ba a rayuwar mijinki. Yanzu haka maganar da nake maki yana tare da ɗan uwansa. Gaskiyar magana babu sauran asiri a jikin yaronnan. Da alama akwai wanda ya tsayamasa." (Allah Ya raba mu da aikin jahilci da jahilai. Ya kiyayemana imaninmu. Ameen).

"Na shiga uku na lalace ni Zeenatu!" Ta dora hannu a kai ta kurma ihu da kuka.

"Na fadamaki ai! Duk ranar da ya yi tozali da abokin haihuwarsa aikinki ya rushe. Ko kin manta wannan gargadin? Toh bari ki ji, akwai wani babban bala'i da ke tunkaroki daga ke har Batulu, ina mai gargaɗinku akan ku gaggauta barin garinnan kafin komai ya ida lalacewa. Wallahi kun ji na rantsemaku, taku ta kare domim ruwa ya ƙarewa ɗan kada!"

Gora ya na kaiwa nan ya mike ya gyara zaman malun-malun hadi da ɓantalar goro ya hau tauna. Da wani irin tsalle Hajiya Zeenatu ta miƙe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login